Sashe 41
So Da Buri Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
In dai zan fad’a miki ki ji, tou inaso dan Allah ki bar Yarinyar nan ta koma wajen Mahaifinta
kamar yadda ya buk’ata, ko munje kotu ya fimu gaskiya, kuma rashin hankalin da Usman ya sake yi yau d’innan ma wata shaida da point ne Abba ya sake samu.
Ki barta ta tafi, za ku dinga waya sannan yace anytime kike son ganinta kije ki ganta, idan ma bakya son zuwa gidan nasa to zai saka ko driver ne ya kaita ko wani park ko restaurant, ku had’u achan amman yace ba zai sake barinta tazo inda kike ba!
Har ga Allah Maryam, Abba is trying to be just here.”
Da sauri ta d’ago tana kallonshi da jajayen idanunta.
D’aga mata kai yayi alamar gasgata mganar shi,
kafin Baba Bashir ya d’aura da cewa
“Maryam har yanzu zuciyar ki a k’ulle take da zafin abunda Abbas ya aikata miki, shiyasa ba za kiga abinda mu muka ganiba, wanda muma a da bamu ganshiba sai bayan da muka yi k’ok’ari muka goge takaicin shi daga idanuwanmu.”
“Mune muka haifeki, baki da masu fad’a miki gaskiya sama da mu, ki tashi ku tafi suyi miki kwatance ki kaisu ki dawo, dama haka rayuwar take, ba komai kake kwallafawa rai kuma ka samu ba, ki bari ko nan da wata biyu ne haka, sai a san abun yi kinji? Yanzu kuje kawai.”
Hudan ke kuma idan kin koma, ki san yanda za kiyi mishi magana a samu ya saki Babanku Usman kinji?”
Cewar Shuwa.
A hankali Mama ta rintse idanuwanta wasu zafafan hawaye suna zubo mata!
Ta manta rabon da Shuwa tayi mata magana mai tsayi haka.
Bata dawo daga duniyar tunanin da ta tafi ba, taji Sakina ta furta wasu maganganu da suka girgizata matuk’a! Wai “An saka ranar Huda nan da wata biyu da Arshaad!!”
Ba Mama kad’ai ba, gaba d’aya parlourn shiru ya d’auka!
Chaaan! Shuwa tace
“Allah ya sanya albarka”
Da sauri Mama ta kalle ta da idanunta hawaye shab’e shab’e!
Kasa jurewa Shuwan tayi kawai ta mik’e ta kama hanya ta fice…
Baba Bashir ne yace “ku tashi kuje Maryam, za muyi wannan maganar wata rana!”
Cikin kuka Mama tace
“Kaka, Abba
Naji zan barta ta koma
amman dan Allah kar ku saka na maida ita, ba zan...”
Kukan da ya kufce mata ne yasa ta kasa ci gaba da magana ta mik’e ta fice tayi cikin gidan…
Baaba Talatu ce ta bita domin lallashin ta.
Wannan shi ake kira isa da mallaka!!! Tayaya zaka
sa ranar Yarinya ba tare da tuntub’ar Mahaifiyarta ba? Saboda Allah fa!.
Shiruuu, parlourn ya d’auka, chaan Kaka yace “su mik’e su kai su”
Ita Sakina tausayi ma y’an tsofaffin suke bata, sun tsufa amman har yau basu huta ba, bayan jigilar case d’in y’an unguwa ga na family…ta tabbatar yanzu suna maida su, police station zasu wuce, akan case d’in Baba………..
A k’ofar tafkeken mansion d’in da suka isa da taimakon kwatancen Sakina suka yi parking, daganan suka yi musu sallama, da d’an Guntun maganganu tukunna suka wuce, su kuma suka shige ciki.
A parlourn suka tarar da Abba, Daddy har Dad da Arshaad! Da alamun maganganu suke yi masu mahimmanci.
Yadda Hudan ta baro Mama tana kuka yasa ta d’an ji zafin Abba!
A hankali suka gaidasu, bayan sun amsa bata tsaya ba kawai ta haye sama! Har sai da Sakina ta d’an yi mata magana bayan sun hau, dan taga kamar basu ji dad’in yadda tayi musu d’in ba.
Ko lunch k’in sauk’a tayi, ba yanda Sakina batayi da ita ba amman tak’i sauk’a, gashi Abba sai kira yake a waya tana amsawa tana cewa “Huda sallah take”
Kamar minti ashirin haka, suka ji knocking. Sakina ce tace
“Come in”
A tunanin ta ko maid aka turo ta kawo musu abincin.
Turo k’ofar yayi ya shigo,
Sakina bata san lokacin da ta fara dariya ba ganin Abba ya shigo har da hular kuku a kanshi da basket d’in abinci a hannunshi.
Harararta yayi, ya d’aura yatsanshi akan lips d’inshi alamun tayi shiru!
D’aga hannuwanta sama tayi
tana gimtse dariyar tata, sannan ta mik’e ta fice da sauri.
Sai da ya ajjiye kular, sannan yace “princess”
Shiru tayi still tana kwance ta bawa k’ofar baya.
Chan taji yace
“Hudan”
A hankali ta mik’e ta zauna ta juyo tana goge
hawayenta, fuskarta tayi jaaa alamun taci kuka, over!!
Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin ya zauna a bakin gadon, yayi hugging d’inta ya fara lallashinta ai kuwa kamar jira take ta saki kukan babu control.
Bai hana ta ba, sai da ta gaji dan kanta tayi shiru tukunna
a hankali yace “sorry dota, i’m really sorry, ok?”
Cikin sheshshek’a tace
“Abba Mama na da bp, yanda na baro ta tana kuka, Allah zai iya tashi?”
Murmushi yayi yana sakinta kafin ya gyara zamanshi yana kallon k’ofar fita tukun yace
“Hudan, na fiki jin zafin kukan da Maman ki take, please don’t question my decision, it’s the right thing.”
Ahankali tace
“Amman Abba pls...”
“Shhhhhhh”
Yace ba tare daya kalleta ba, kafin ya juyo ya fara k’ok’arin zuba mata abinci.
Omelet d’in da ya soya mata ya saka a gefe, da pizza slice uku da ya d’auko.
Da farko k’in ci tayi sai da yayi dagaske, tukun ta d’an karb’a.
Bayan ta gama ta sha ruwa, ya d’an dunga janta da magana yana ta faman lallashinta.
Hudan bata iya dogon fushi da mutum ba, don haka ta d’an sauk’o, hakan kuwa yayi matuk’ar ragewa Abba kusan 20% na damuwar da yake ciki
shiyasa da ta rok’esa akan ya saki Baba ba don halinsa ba sai dam kakanninta da hankalin su yake a tashe!
Abban ya amince, a take ma a gabanta yayi waya yace a sake shi.
Ta ji dad’i sosai kuwa.
Daganan suka d’an ci gaba da maganarsu.
Hammar da yaga tanayi ne
ya sanya ya fahimci bacci take ji, dan haka yace mata “ta kwanta”
Bata yi 10 minutes da kwanciyar ba ta fara bacci….
Ahankali yake kallonta yana tunani kala kala…
Sai bayan kusan 1 hour tukun ya rage mata k’arfin ac ya lullub’eta da bargo, sannan ya fita da kayan abincin...............
A chan parlourn k’asa kuwa, sam Sakina bata lura da Auwal wanda ya daya dawo break ba, sai da ta kusan k’arasawa dining d’in!
Tun kusan sauk’owarta yaji a jikinshi!
Addua yake Allah yasa itance, don haka ya k’urawa stairs d’in ido…
Ba a hankali take tafiyarta ba ba kuma da sauri ba! Da d’an
murmushi a kan fuskarta.
Gaba d’aya ya shagala da kallonta, har wani lumshe ido yake yi yana bud’ewa.
Jikinta ne ya bata kamar ana kallonta, sai kuma mayen k’amshin turarenshi da ta fara ji a jikin shi tun ranar farko ya daki hancinta!
Dan haka da sauri ta d’ago ta kalli dining d’in..
Suna had’a ido yayi saurin rintse idanuwanshi kafin a hankali ya bud’e su a kanta!
Doguwar riga ce a jikinta Ashape y’ar kanti bak’a mai ratsi ratsin sky blue sai d’ankwalinta wanda tayi simple d’auri da shi..
Rigar bata wani kamata ba,
amman kasancewarta mai garin jiki yasa ta d’an fiddo mata surar jikinta kad’an!.
Ranta ne ya b’aci ganin yanda yake wani rufe ido yana sake bud’ewa yana k’are mata kallo! Da sauri ta sa hannu ta warware d’ankwalinta ta yafa a jikinta sannan ta doka wani uban tsaki, wanda yayi sanadiyyar dawo dashi cikin parlourn.
Har ga Allah abinda take tunani ma shi Allah bai bashi ikon lura da nan d’in ba, kawai shi dai yasan ya tsinci kanshi cikin tsananin farin ciki da shauk’i na daban, sannan yanda ta yi d’aurin ya sake fito da ainahin kyauwun fuskarta
dan yawanci cikin hijabi yake ganinta, ga wani lallausan saje dake shirin had’ewa da gashin girarta, na gefen kunnenta ma ya sauk’a sosai kamar zai had’e da gashin k’eyarta, sannan tunda yake bai tab’a ganinta tana murmushi irin yau ba!
Bai ida dawowa dede ba yaga ta juya da sauri zata bar wajen.
Da sauri ya mik’e ya k’arasa ya sha gabanta kafin yace
“Sakina, please, listen to me dan Allah.”
Wani kallon tsana tayi masa kafin tace
“mallan dalla matsa In wuce”
Tayi maganar babu alamun wasa a tare da ita….
Zagayeshi take k’ok’arin yi amman yak’i ya bata damar yin hakan, da alamun ma in ta biyeshi to a yadda yakesa hannayenshi wajen k’ok’arin kareta daga wucewa tsaf zai tab’ata!
Don haka ta tsaya ta fara aika mishi da harara kafin tace
“Malan ni ba Jalila bace ba!
Ka bar ganin wai a gidanku nake wallahi
Idan baka bani hanya na wuce ba, zan zabga maka mari!”
Ga mamakinta sai taga yana dariya, sai da yayi mai isarshi sannan yace
“Na yarda!
But duk mari d’aya zaki bani 10 minutes d’inki, kawai ko d’an hira ne muyi…..tbh i can do anything to get your attention”
Ya k’are maganan yana kallonta da murmushi akan fuskanshi sannan ya d’anyi k’asa da kanshi…..
Yanayin zanen flower d’in da aka yi na sky blue akan kayan jikinta yayi mishi kyau sosai!
Zanen ya bi da kallo, har ya sauk’e idanunsa akan yatsun k’afarta! ,
Gaba d’aya ya shagala da kallo yaga ta janye da sauri cikin b’acin rai tace
“D’an iska kawai!!” k’asa k’asa, ita kanta bata yi tunanin zai ji ba, sannan tayi sauri ta nufi d’akin da ke kusa kusa, tana shiga ta datse k’ofar ganin yana shirin biyo ta.
Tunda Auwal yake a rayuwar shi, har snake friends d’insa wani lokacin suke kiranshi da shi, ko master, ko danger sunaye dai na rashin d’a’a kala kala but bai tab’a jin ba dad’i ba!
Amman yau da Sakina tayi mishi wannan kallon har ta furta, gaba d’aya duk sai yaji babu dad’i! He hates it.
Kasa ci gaba da lunch d’inma yayi don haka ya mi’ke ya fita ya koma office da tunani barkatai a ranshi!
He just wants to talk to her, yana so ya sake ganin smile d’in nan nata!
D’an 5 minutes d’in da suka yi shi da ita d’azu tare zai iya cewa
‘it one of the best moment of his life.......’
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
46
kamar yadda ya buk’ata, ko munje kotu ya fimu gaskiya, kuma rashin hankalin da Usman ya sake yi yau d’innan ma wata shaida da point ne Abba ya sake samu.
Ki barta ta tafi, za ku dinga waya sannan yace anytime kike son ganinta kije ki ganta, idan ma bakya son zuwa gidan nasa to zai saka ko driver ne ya kaita ko wani park ko restaurant, ku had’u achan amman yace ba zai sake barinta tazo inda kike ba!
Har ga Allah Maryam, Abba is trying to be just here.”
Da sauri ta d’ago tana kallonshi da jajayen idanunta.
D’aga mata kai yayi alamar gasgata mganar shi,
kafin Baba Bashir ya d’aura da cewa
“Maryam har yanzu zuciyar ki a k’ulle take da zafin abunda Abbas ya aikata miki, shiyasa ba za kiga abinda mu muka ganiba, wanda muma a da bamu ganshiba sai bayan da muka yi k’ok’ari muka goge takaicin shi daga idanuwanmu.”
“Mune muka haifeki, baki da masu fad’a miki gaskiya sama da mu, ki tashi ku tafi suyi miki kwatance ki kaisu ki dawo, dama haka rayuwar take, ba komai kake kwallafawa rai kuma ka samu ba, ki bari ko nan da wata biyu ne haka, sai a san abun yi kinji? Yanzu kuje kawai.”
Hudan ke kuma idan kin koma, ki san yanda za kiyi mishi magana a samu ya saki Babanku Usman kinji?”
Cewar Shuwa.
A hankali Mama ta rintse idanuwanta wasu zafafan hawaye suna zubo mata!
Ta manta rabon da Shuwa tayi mata magana mai tsayi haka.
Bata dawo daga duniyar tunanin da ta tafi ba, taji Sakina ta furta wasu maganganu da suka girgizata matuk’a! Wai “An saka ranar Huda nan da wata biyu da Arshaad!!”
Ba Mama kad’ai ba, gaba d’aya parlourn shiru ya d’auka!
Chaaan! Shuwa tace
“Allah ya sanya albarka”
Da sauri Mama ta kalle ta da idanunta hawaye shab’e shab’e!
Kasa jurewa Shuwan tayi kawai ta mik’e ta kama hanya ta fice…
Baba Bashir ne yace “ku tashi kuje Maryam, za muyi wannan maganar wata rana!”
Cikin kuka Mama tace
“Kaka, Abba
Naji zan barta ta koma
amman dan Allah kar ku saka na maida ita, ba zan...”
Kukan da ya kufce mata ne yasa ta kasa ci gaba da magana ta mik’e ta fice tayi cikin gidan…
Baaba Talatu ce ta bita domin lallashin ta.
Wannan shi ake kira isa da mallaka!!! Tayaya zaka
sa ranar Yarinya ba tare da tuntub’ar Mahaifiyarta ba? Saboda Allah fa!.
Shiruuu, parlourn ya d’auka, chaan Kaka yace “su mik’e su kai su”
Ita Sakina tausayi ma y’an tsofaffin suke bata, sun tsufa amman har yau basu huta ba, bayan jigilar case d’in y’an unguwa ga na family…ta tabbatar yanzu suna maida su, police station zasu wuce, akan case d’in Baba………..
A k’ofar tafkeken mansion d’in da suka isa da taimakon kwatancen Sakina suka yi parking, daganan suka yi musu sallama, da d’an Guntun maganganu tukunna suka wuce, su kuma suka shige ciki.
A parlourn suka tarar da Abba, Daddy har Dad da Arshaad! Da alamun maganganu suke yi masu mahimmanci.
Yadda Hudan ta baro Mama tana kuka yasa ta d’an ji zafin Abba!
A hankali suka gaidasu, bayan sun amsa bata tsaya ba kawai ta haye sama! Har sai da Sakina ta d’an yi mata magana bayan sun hau, dan taga kamar basu ji dad’in yadda tayi musu d’in ba.
Ko lunch k’in sauk’a tayi, ba yanda Sakina batayi da ita ba amman tak’i sauk’a, gashi Abba sai kira yake a waya tana amsawa tana cewa “Huda sallah take”
Kamar minti ashirin haka, suka ji knocking. Sakina ce tace
“Come in”
A tunanin ta ko maid aka turo ta kawo musu abincin.
Turo k’ofar yayi ya shigo,
Sakina bata san lokacin da ta fara dariya ba ganin Abba ya shigo har da hular kuku a kanshi da basket d’in abinci a hannunshi.
Harararta yayi, ya d’aura yatsanshi akan lips d’inshi alamun tayi shiru!
D’aga hannuwanta sama tayi
tana gimtse dariyar tata, sannan ta mik’e ta fice da sauri.
Sai da ya ajjiye kular, sannan yace “princess”
Shiru tayi still tana kwance ta bawa k’ofar baya.
Chan taji yace
“Hudan”
A hankali ta mik’e ta zauna ta juyo tana goge
hawayenta, fuskarta tayi jaaa alamun taci kuka, over!!
Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin ya zauna a bakin gadon, yayi hugging d’inta ya fara lallashinta ai kuwa kamar jira take ta saki kukan babu control.
Bai hana ta ba, sai da ta gaji dan kanta tayi shiru tukunna
a hankali yace “sorry dota, i’m really sorry, ok?”
Cikin sheshshek’a tace
“Abba Mama na da bp, yanda na baro ta tana kuka, Allah zai iya tashi?”
Murmushi yayi yana sakinta kafin ya gyara zamanshi yana kallon k’ofar fita tukun yace
“Hudan, na fiki jin zafin kukan da Maman ki take, please don’t question my decision, it’s the right thing.”
Ahankali tace
“Amman Abba pls...”
“Shhhhhhh”
Yace ba tare daya kalleta ba, kafin ya juyo ya fara k’ok’arin zuba mata abinci.
Omelet d’in da ya soya mata ya saka a gefe, da pizza slice uku da ya d’auko.
Da farko k’in ci tayi sai da yayi dagaske, tukun ta d’an karb’a.
Bayan ta gama ta sha ruwa, ya d’an dunga janta da magana yana ta faman lallashinta.
Hudan bata iya dogon fushi da mutum ba, don haka ta d’an sauk’o, hakan kuwa yayi matuk’ar ragewa Abba kusan 20% na damuwar da yake ciki
shiyasa da ta rok’esa akan ya saki Baba ba don halinsa ba sai dam kakanninta da hankalin su yake a tashe!
Abban ya amince, a take ma a gabanta yayi waya yace a sake shi.
Ta ji dad’i sosai kuwa.
Daganan suka d’an ci gaba da maganarsu.
Hammar da yaga tanayi ne
ya sanya ya fahimci bacci take ji, dan haka yace mata “ta kwanta”
Bata yi 10 minutes da kwanciyar ba ta fara bacci….
Ahankali yake kallonta yana tunani kala kala…
Sai bayan kusan 1 hour tukun ya rage mata k’arfin ac ya lullub’eta da bargo, sannan ya fita da kayan abincin...............
A chan parlourn k’asa kuwa, sam Sakina bata lura da Auwal wanda ya daya dawo break ba, sai da ta kusan k’arasawa dining d’in!
Tun kusan sauk’owarta yaji a jikinshi!
Addua yake Allah yasa itance, don haka ya k’urawa stairs d’in ido…
Ba a hankali take tafiyarta ba ba kuma da sauri ba! Da d’an
murmushi a kan fuskarta.
Gaba d’aya ya shagala da kallonta, har wani lumshe ido yake yi yana bud’ewa.
Jikinta ne ya bata kamar ana kallonta, sai kuma mayen k’amshin turarenshi da ta fara ji a jikin shi tun ranar farko ya daki hancinta!
Dan haka da sauri ta d’ago ta kalli dining d’in..
Suna had’a ido yayi saurin rintse idanuwanshi kafin a hankali ya bud’e su a kanta!
Doguwar riga ce a jikinta Ashape y’ar kanti bak’a mai ratsi ratsin sky blue sai d’ankwalinta wanda tayi simple d’auri da shi..
Rigar bata wani kamata ba,
amman kasancewarta mai garin jiki yasa ta d’an fiddo mata surar jikinta kad’an!.
Ranta ne ya b’aci ganin yanda yake wani rufe ido yana sake bud’ewa yana k’are mata kallo! Da sauri ta sa hannu ta warware d’ankwalinta ta yafa a jikinta sannan ta doka wani uban tsaki, wanda yayi sanadiyyar dawo dashi cikin parlourn.
Har ga Allah abinda take tunani ma shi Allah bai bashi ikon lura da nan d’in ba, kawai shi dai yasan ya tsinci kanshi cikin tsananin farin ciki da shauk’i na daban, sannan yanda ta yi d’aurin ya sake fito da ainahin kyauwun fuskarta
dan yawanci cikin hijabi yake ganinta, ga wani lallausan saje dake shirin had’ewa da gashin girarta, na gefen kunnenta ma ya sauk’a sosai kamar zai had’e da gashin k’eyarta, sannan tunda yake bai tab’a ganinta tana murmushi irin yau ba!
Bai ida dawowa dede ba yaga ta juya da sauri zata bar wajen.
Da sauri ya mik’e ya k’arasa ya sha gabanta kafin yace
“Sakina, please, listen to me dan Allah.”
Wani kallon tsana tayi masa kafin tace
“mallan dalla matsa In wuce”
Tayi maganar babu alamun wasa a tare da ita….
Zagayeshi take k’ok’arin yi amman yak’i ya bata damar yin hakan, da alamun ma in ta biyeshi to a yadda yakesa hannayenshi wajen k’ok’arin kareta daga wucewa tsaf zai tab’ata!
Don haka ta tsaya ta fara aika mishi da harara kafin tace
“Malan ni ba Jalila bace ba!
Ka bar ganin wai a gidanku nake wallahi
Idan baka bani hanya na wuce ba, zan zabga maka mari!”
Ga mamakinta sai taga yana dariya, sai da yayi mai isarshi sannan yace
“Na yarda!
But duk mari d’aya zaki bani 10 minutes d’inki, kawai ko d’an hira ne muyi…..tbh i can do anything to get your attention”
Ya k’are maganan yana kallonta da murmushi akan fuskanshi sannan ya d’anyi k’asa da kanshi…..
Yanayin zanen flower d’in da aka yi na sky blue akan kayan jikinta yayi mishi kyau sosai!
Zanen ya bi da kallo, har ya sauk’e idanunsa akan yatsun k’afarta! ,
Gaba d’aya ya shagala da kallo yaga ta janye da sauri cikin b’acin rai tace
“D’an iska kawai!!” k’asa k’asa, ita kanta bata yi tunanin zai ji ba, sannan tayi sauri ta nufi d’akin da ke kusa kusa, tana shiga ta datse k’ofar ganin yana shirin biyo ta.
Tunda Auwal yake a rayuwar shi, har snake friends d’insa wani lokacin suke kiranshi da shi, ko master, ko danger sunaye dai na rashin d’a’a kala kala but bai tab’a jin ba dad’i ba!
Amman yau da Sakina tayi mishi wannan kallon har ta furta, gaba d’aya duk sai yaji babu dad’i! He hates it.
Kasa ci gaba da lunch d’inma yayi don haka ya mi’ke ya fita ya koma office da tunani barkatai a ranshi!
He just wants to talk to her, yana so ya sake ganin smile d’in nan nata!
D’an 5 minutes d’in da suka yi shi da ita d’azu tare zai iya cewa
‘it one of the best moment of his life.......’
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
46