Sashe 14
So Da Buri Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummi bata san lokacin da ta fashe da wani irin mahaukacin kuka ba!
Tsoronta d’aya a yanzu
kar Granpa yaji zancen nan.
“Innalillahi wa innailaihirraji un”
Ta shiga maimaitawa, sannan ta fara kallon d’akin tana neman hanyar guduwa, da sauri ta juya ta nufi k’ofar closet, da mugun gudu.
Daidai nan Abba ya shigo da y’an sanda mata guda biyu!
Mom ya nuna musu yace “suyi arresting d’inta”
A take kuwa suka yo kanta..
Babu abinda yafi d’agawa Mom hankali kamar ankwar da suka saka mata, bata san lokacin da idanunta suka kawo ruwa ba.
Waige waige Abba ya hau yi…Chan ya hango k’ofar closet a d’an bud’e kad’an hakan yasa ya isa wajen gadan gadan ya bud’e k’ofar ya shiga, ya fara dube dube!
Idanuwanshine suka sauk’a a
,wajen jallabiyoyin da aka rar rataye…gani yai wajen yana d’an motsi, hakan yasa ya k’urawa wajen ido, cikin sa’a kuwa ya hango k’afafun Ummi da suka sha jan lalle ta chan k’asa
Ai kuwa ya janyo gaba d’aya kayan wajen da sun kusan 30 ya zubar dasu a k’asa!
Tarr!! Ummi ta baiyyana a gabanshi sai uban gumi take yi, ga fuskar nan tayi jazir.
Dukkan k’arfin shi yasa ya fincikota ya fara janta, sai da ya kaita gaban y’an sandan tukunna ya dank’a musu ita, itama aka sa mata tata ankwar.
Bai bi takan magiya da ban hak’urin da take yi masa ba, haka nan ya basu umarnin tafiya da su.
Mom kwata kwata bata yi gardama ba, amman Ummi sai da aka nuna mata bindiga tukunna ta nutsu.
Suna fita shima ya mara musu baya.
A k’asa cikin motar suka samu Mammy itama da ankwar ta .
Gidan gaba d’aya ya cika da jiniyar y’an sanda, kowa ya rud’e, duk an firfito, Sudais da Shuraim in banda kuka ba abunda suke yi!
Dai dai y’an sandan suna shirin tada motar Granpa ya fito Gramma na biye da shi a baya.
Daddy shima wanda shigowar shi yanzun kenan
Yayi saurin k’arasowa wajen, yana hango su kuwa da sauri ya k’arasa inda suke yafara kokarin fito da Matarsa, yana yiwa y’an sanda masifa!
Granpa wanda yanzu ya k’araso wajen ne ya dakatar da shi sannan ya kira babban d’an sandan…
Ko gaisuwar shi bai bari ya k’arasa ba ya d’auke shi da Mari, kafin ya fara magana cikin b’acin rai
“Ka san a ina kake!?
Ka san ko su waye waennan d’in)
Laifin me sukayi?
Who the hell ask you to arrest them?”.
“I did”
Yaji muryan Abba a bayanshi.
Da mamaki Granpa ya d’an juyo yana kallonshi..
Ba tare da Abb yace komai ba ya k’arasa cikin motar ya fito da Ummi ya kawota gaban Granpa sannan yace “ta fad’i abunda suka yi”.
Rarraba ido ta fara yi.
Cikin b’acin rai Granpa yace “a cire musu ankwar a fito dasu gaba d’aya.”
Bayan anyi hakan ne ya kalle ta sannan yace
“Mai ya faru?”
Da kyar ta iya d’agowa ta d’an saci kallon Mom, a take kuwa daman Mom d’in jira take, ta hau girgiza mata kai alamun kar ta fad’a.
Nan kuwa ta samu kwarin guiwa, cikin sheshshek’ar kuka tace
“Nima ban san abunda ya faru ba Granpa, kawai d’azu yana dawowa yace wai sun had’u da Maryam, in fad’a mishi me nayi ko kuma ya d’au mataki ban san me tace mishi ba amman kawai da nace ban san me nayi ba ya rufeni da dukaa.”
Tana kaiwa nan ta fashe da kuka sannan ta durk’usa a gaban Granpa.
Da k’arfi Abba ya runtse idanuwanshi…
Sai da yad’an seseta zuciyarshi da take ingiza shi a kan yaje ya rufe Ummu da duka, tukunna ya bud’e idanunshi ya sauk’e su akan Granpa…
Shima kuwa shi d’in ya zubawa ido.
Ganin kallon da Granpa yake yi mishi ne yasa kawai ya juya ya nufi side d’insu Aslam.
Ko minti uku ba a yi ba ya fito rik’e da hannun Huda.
Tunda suka tunkarosu Granpa ya kafe Yarinyar da ido!
Sai da yazo gabanshi sannan ya tsayar da Huda, da gaba d’aya kallo ya koma kanta.
Ummi ya kalla wadda ta rikice da ganin Yarinyar had’i da sake rud’ewa, sannan yace
“Baki santa ba ko?” Yayi maganar yana nuna Huda, kafin cikin d’acin zuciya yace
“Zaki fad’i gaskiya ko sai na yanke hukuncin da nayi miki alk’awarin d’auka???”
Gaba d’aya ilahirin jikinta karkarwa yake yi, tun ba ma da taga Gramma ta jawo Hudan kusa da ita tana d’an shafa fuskarta sannan ta k’ura mata ido ba!
Tabbas wannan itace y’ar Maryam da Abba, dan ga tsananin kamanni nan suna yi da Mijinta(Abba) ba kad’an ba, yanzu ya za tai mai zata ce??
Karaf!! suka kuma had’a ido da Mom, a take ta sake girgiza mata kai, wanda hakan ya sake rud’a ta dan bata san kuma abun yi ko cewa ba, ba daman tayi k’arya dan ga evidence, kuma ba daman fad’an gaskiya tunda bata san dalilin Mom na hanata fad’a ba.
Yanke shawarar sumewa tayi, dan haka ta fara k’ok’arin lumllumshe ido amma sai maganar da Abba ya fara tayi saurin watstsakar da ita daga suman k’aryar da tayi shirin yi jin yana cewa
“Granpa wannan y’a ta ce!”
Yai maganar yana nuna Huda
Sannan ya k’ara da cewa
“Those 3” ya nunata da Mom da Mammy, kafin ya cigaba
“Knew about everything all this while!!…
Ranar da Maryam zata haihu ta turo sister d’inta ta fad’a min, bayan sistern nata ta bawa Daniel sak’on, shi kuma munafuki sai ya fara zuwa wajen su da takardar saboda bakinsu d’aya tuntuni!
Bayan sun karance sak’on nata shine suka yi mata wannan reply d’in.”
Ya k’arashe maganar tare da zaro takardar gaban rigarshi ya mik’awa Granpa.
Hannu Granpa ya saka ya karb’a, sannan ya fara karantawa…..
Baya Daniel ya fara ja
dan daman, tun lokacin da aka fara zancen ya sha jikin jikinshi…
Karaf! idon Granpa ya sauk’a a kanshi, dan haka yace mishi “idan ya isa gate d’in daga nan yayi gaba kar ya sake ganinshi near his estate!!”
Ummi dajin haka ta san kashin ta ya gama bushewa don daga gani Granpa ya gama gasgata maganar Abba!
Don haka ta fara jiran jin sauk’ar mari ko duka, amman sai taji kawai ya dafa ta.
Tana d’agowa gabanta ya fad’i don gani tayi ya mugun had’e rai babu alamun wasa ko sassauchi akan fuskar shi.
Suna had’a ido ba tare da b’ata lokaci ba yace
“1 word from you!
Akwai gyara a cikin maganarshi?
Yes or no?”
Gabanta yana fad’uwa tana kuka tace
“No”
Da sauri Mom ta runtse idanuwanta gam!!!.
A hankali Granpa ya sauk’e ajiyar zuciya sannan ya zare hannunshi daga kanta, kafin ya kira d’an sandan daya mara d’azu!
Yana karasowa gareshi yace
“Arrest them!”
Da sauri Mom ta bud’e idanunta a firgice tana kallonshi, Daddy ma k’arasowa yayi wajen ya hau rok’on shi yana cewa
“Wannan family matter ne, a bari kawai za suyi settling a tsakaninsu dan Allah yayi hak’uri”.
Hatta Gramma sai da ta sa baki amman fur!!! Granpa yayi kunnen uwar shegu…
Banda kuka ba abunda Mammy da Ummi suke yi….
Sassauchi d’aya Granpa yayi musu shine
Bai bari an tafi dasu a motar y’an sanda ba kuma ba a saka musu handcuff ba.
Ya bada motar gida yasa drivernshi ya kaisu har cell, bayan ya tabbatar wa da y’an sandan “kar a bawa kowa bellin su sai nan da 2 months............”
Duk wannan bidirin da ake yi Aslam yana sama bolcony d’in parlourn Mammy yana kallon komai!
Motocin suna ficewa Gramma ta sake ruk’o Hudan da kyau sannan ta rungume ta, kafin tace
“Welcome to MT my granddaughter” har da d’an hawayenta. Sannan tace mata
“Zo muje ki huta ko?”
Ita dai Huda kawai binta take yi a haka ta jata tayi side d’insu da ita.
Har bedroom d’inta ta kaita, har ga Allah lokaci d’aya taji Hudan ta shiga ranta matuk’a!
Sai nan nan take yi da ita, cikin mintuna k’alilan aka cike gabanta da abinci kala kala.
Sai janta take yi da hira…
Da kyar Hudan ta samu ta d’an sake da ita, ganin da tayi matar tanada sauk’in kai ya sanya ta cewa “dan Allah tana so taje taga Mamanta!
Sun barta a asibiti tanata kuka, kuma bata da lafiya, gashi tanata kiranta amman bata d’auka.”
Gramma ta bud’e baki zata yi magana kenan Granpa ya shigo, kallonsu yayi kafin yace “ku biyo ni” sannan ya juya ya fita.
A zaune suka sameshi a parlourn da wani da suke da tabbacin Likita ne saboda ga lap coat a jikinshi.
A k’asa Hudan ta nemi waje ta zauna kan kafet, gramma kuma ta zauna a kan d’aya daga cikin kujerun parlourn.
Nuna mishi ita kawai taga Granpa yayi, daganan taga mutumin ya nufuto…..setin ta ya zauna sannan ya bud’e d’an k’aramin akwatin da ya shigo da shi.
Sirinji ya d’auko da wani abu kamar cutting bud sai reza guda d’aya!
Sai da aka sha fama sannan aka d’auki jikin, daganan ya bata rezar yace “ta yanko farcenta” cuttonbud d’in kuma a bakinta kawai ta saka ta cire ta bashi, daganan ya d’an sa hannu ya ciri gashinta dake kwance akan goshinta wanda har sai da tasa k’ara dan ba kad’an ba taji zafi!
Daga nan ya mik’e ya cewa Granpa “nanda 24 hours in shaa Allah zai dawo”
Sannan yasa kai ya fice.
Gramma taso tayi mishi magana amman ganin yadda ya had’e rai ne yasa kawai ta kyaleshi suka koma d’aki ita da Hudan bayan ya sallamesu.
Iya gata Huda taga gata a wajen Gramma, amman dukda hakka Hudan zancenta d’aya ne “zata je wajen Mama”
Da kyar ta samu ta lallab’ata akan zuwa gobe za suje su duba Maman nata, sannan ta yarda tayi bacci mai cike da mafarkin Mama kala kala.....
Sai bayan isha tukunna Auwal ya dawo, daman saboda aikin da ya d’orawa kanshi kwana biyun nan sometimes har kusan kwana yake yi a office.
Aikin da ba nashi ba da wanda yake nashi duk yi yake…ya kuwa ci sa’a dan Granpa har ya d’an fara sauk’owa da kuma tunanin maidashi kujerarshi.
Tsoronta d’aya a yanzu
kar Granpa yaji zancen nan.
“Innalillahi wa innailaihirraji un”
Ta shiga maimaitawa, sannan ta fara kallon d’akin tana neman hanyar guduwa, da sauri ta juya ta nufi k’ofar closet, da mugun gudu.
Daidai nan Abba ya shigo da y’an sanda mata guda biyu!
Mom ya nuna musu yace “suyi arresting d’inta”
A take kuwa suka yo kanta..
Babu abinda yafi d’agawa Mom hankali kamar ankwar da suka saka mata, bata san lokacin da idanunta suka kawo ruwa ba.
Waige waige Abba ya hau yi…Chan ya hango k’ofar closet a d’an bud’e kad’an hakan yasa ya isa wajen gadan gadan ya bud’e k’ofar ya shiga, ya fara dube dube!
Idanuwanshine suka sauk’a a
,wajen jallabiyoyin da aka rar rataye…gani yai wajen yana d’an motsi, hakan yasa ya k’urawa wajen ido, cikin sa’a kuwa ya hango k’afafun Ummi da suka sha jan lalle ta chan k’asa
Ai kuwa ya janyo gaba d’aya kayan wajen da sun kusan 30 ya zubar dasu a k’asa!
Tarr!! Ummi ta baiyyana a gabanshi sai uban gumi take yi, ga fuskar nan tayi jazir.
Dukkan k’arfin shi yasa ya fincikota ya fara janta, sai da ya kaita gaban y’an sandan tukunna ya dank’a musu ita, itama aka sa mata tata ankwar.
Bai bi takan magiya da ban hak’urin da take yi masa ba, haka nan ya basu umarnin tafiya da su.
Mom kwata kwata bata yi gardama ba, amman Ummi sai da aka nuna mata bindiga tukunna ta nutsu.
Suna fita shima ya mara musu baya.
A k’asa cikin motar suka samu Mammy itama da ankwar ta .
Gidan gaba d’aya ya cika da jiniyar y’an sanda, kowa ya rud’e, duk an firfito, Sudais da Shuraim in banda kuka ba abunda suke yi!
Dai dai y’an sandan suna shirin tada motar Granpa ya fito Gramma na biye da shi a baya.
Daddy shima wanda shigowar shi yanzun kenan
Yayi saurin k’arasowa wajen, yana hango su kuwa da sauri ya k’arasa inda suke yafara kokarin fito da Matarsa, yana yiwa y’an sanda masifa!
Granpa wanda yanzu ya k’araso wajen ne ya dakatar da shi sannan ya kira babban d’an sandan…
Ko gaisuwar shi bai bari ya k’arasa ba ya d’auke shi da Mari, kafin ya fara magana cikin b’acin rai
“Ka san a ina kake!?
Ka san ko su waye waennan d’in)
Laifin me sukayi?
Who the hell ask you to arrest them?”.
“I did”
Yaji muryan Abba a bayanshi.
Da mamaki Granpa ya d’an juyo yana kallonshi..
Ba tare da Abb yace komai ba ya k’arasa cikin motar ya fito da Ummi ya kawota gaban Granpa sannan yace “ta fad’i abunda suka yi”.
Rarraba ido ta fara yi.
Cikin b’acin rai Granpa yace “a cire musu ankwar a fito dasu gaba d’aya.”
Bayan anyi hakan ne ya kalle ta sannan yace
“Mai ya faru?”
Da kyar ta iya d’agowa ta d’an saci kallon Mom, a take kuwa daman Mom d’in jira take, ta hau girgiza mata kai alamun kar ta fad’a.
Nan kuwa ta samu kwarin guiwa, cikin sheshshek’ar kuka tace
“Nima ban san abunda ya faru ba Granpa, kawai d’azu yana dawowa yace wai sun had’u da Maryam, in fad’a mishi me nayi ko kuma ya d’au mataki ban san me tace mishi ba amman kawai da nace ban san me nayi ba ya rufeni da dukaa.”
Tana kaiwa nan ta fashe da kuka sannan ta durk’usa a gaban Granpa.
Da k’arfi Abba ya runtse idanuwanshi…
Sai da yad’an seseta zuciyarshi da take ingiza shi a kan yaje ya rufe Ummu da duka, tukunna ya bud’e idanunshi ya sauk’e su akan Granpa…
Shima kuwa shi d’in ya zubawa ido.
Ganin kallon da Granpa yake yi mishi ne yasa kawai ya juya ya nufi side d’insu Aslam.
Ko minti uku ba a yi ba ya fito rik’e da hannun Huda.
Tunda suka tunkarosu Granpa ya kafe Yarinyar da ido!
Sai da yazo gabanshi sannan ya tsayar da Huda, da gaba d’aya kallo ya koma kanta.
Ummi ya kalla wadda ta rikice da ganin Yarinyar had’i da sake rud’ewa, sannan yace
“Baki santa ba ko?” Yayi maganar yana nuna Huda, kafin cikin d’acin zuciya yace
“Zaki fad’i gaskiya ko sai na yanke hukuncin da nayi miki alk’awarin d’auka???”
Gaba d’aya ilahirin jikinta karkarwa yake yi, tun ba ma da taga Gramma ta jawo Hudan kusa da ita tana d’an shafa fuskarta sannan ta k’ura mata ido ba!
Tabbas wannan itace y’ar Maryam da Abba, dan ga tsananin kamanni nan suna yi da Mijinta(Abba) ba kad’an ba, yanzu ya za tai mai zata ce??
Karaf!! suka kuma had’a ido da Mom, a take ta sake girgiza mata kai, wanda hakan ya sake rud’a ta dan bata san kuma abun yi ko cewa ba, ba daman tayi k’arya dan ga evidence, kuma ba daman fad’an gaskiya tunda bata san dalilin Mom na hanata fad’a ba.
Yanke shawarar sumewa tayi, dan haka ta fara k’ok’arin lumllumshe ido amma sai maganar da Abba ya fara tayi saurin watstsakar da ita daga suman k’aryar da tayi shirin yi jin yana cewa
“Granpa wannan y’a ta ce!”
Yai maganar yana nuna Huda
Sannan ya k’ara da cewa
“Those 3” ya nunata da Mom da Mammy, kafin ya cigaba
“Knew about everything all this while!!…
Ranar da Maryam zata haihu ta turo sister d’inta ta fad’a min, bayan sistern nata ta bawa Daniel sak’on, shi kuma munafuki sai ya fara zuwa wajen su da takardar saboda bakinsu d’aya tuntuni!
Bayan sun karance sak’on nata shine suka yi mata wannan reply d’in.”
Ya k’arashe maganar tare da zaro takardar gaban rigarshi ya mik’awa Granpa.
Hannu Granpa ya saka ya karb’a, sannan ya fara karantawa…..
Baya Daniel ya fara ja
dan daman, tun lokacin da aka fara zancen ya sha jikin jikinshi…
Karaf! idon Granpa ya sauk’a a kanshi, dan haka yace mishi “idan ya isa gate d’in daga nan yayi gaba kar ya sake ganinshi near his estate!!”
Ummi dajin haka ta san kashin ta ya gama bushewa don daga gani Granpa ya gama gasgata maganar Abba!
Don haka ta fara jiran jin sauk’ar mari ko duka, amman sai taji kawai ya dafa ta.
Tana d’agowa gabanta ya fad’i don gani tayi ya mugun had’e rai babu alamun wasa ko sassauchi akan fuskar shi.
Suna had’a ido ba tare da b’ata lokaci ba yace
“1 word from you!
Akwai gyara a cikin maganarshi?
Yes or no?”
Gabanta yana fad’uwa tana kuka tace
“No”
Da sauri Mom ta runtse idanuwanta gam!!!.
A hankali Granpa ya sauk’e ajiyar zuciya sannan ya zare hannunshi daga kanta, kafin ya kira d’an sandan daya mara d’azu!
Yana karasowa gareshi yace
“Arrest them!”
Da sauri Mom ta bud’e idanunta a firgice tana kallonshi, Daddy ma k’arasowa yayi wajen ya hau rok’on shi yana cewa
“Wannan family matter ne, a bari kawai za suyi settling a tsakaninsu dan Allah yayi hak’uri”.
Hatta Gramma sai da ta sa baki amman fur!!! Granpa yayi kunnen uwar shegu…
Banda kuka ba abunda Mammy da Ummi suke yi….
Sassauchi d’aya Granpa yayi musu shine
Bai bari an tafi dasu a motar y’an sanda ba kuma ba a saka musu handcuff ba.
Ya bada motar gida yasa drivernshi ya kaisu har cell, bayan ya tabbatar wa da y’an sandan “kar a bawa kowa bellin su sai nan da 2 months............”
Duk wannan bidirin da ake yi Aslam yana sama bolcony d’in parlourn Mammy yana kallon komai!
Motocin suna ficewa Gramma ta sake ruk’o Hudan da kyau sannan ta rungume ta, kafin tace
“Welcome to MT my granddaughter” har da d’an hawayenta. Sannan tace mata
“Zo muje ki huta ko?”
Ita dai Huda kawai binta take yi a haka ta jata tayi side d’insu da ita.
Har bedroom d’inta ta kaita, har ga Allah lokaci d’aya taji Hudan ta shiga ranta matuk’a!
Sai nan nan take yi da ita, cikin mintuna k’alilan aka cike gabanta da abinci kala kala.
Sai janta take yi da hira…
Da kyar Hudan ta samu ta d’an sake da ita, ganin da tayi matar tanada sauk’in kai ya sanya ta cewa “dan Allah tana so taje taga Mamanta!
Sun barta a asibiti tanata kuka, kuma bata da lafiya, gashi tanata kiranta amman bata d’auka.”
Gramma ta bud’e baki zata yi magana kenan Granpa ya shigo, kallonsu yayi kafin yace “ku biyo ni” sannan ya juya ya fita.
A zaune suka sameshi a parlourn da wani da suke da tabbacin Likita ne saboda ga lap coat a jikinshi.
A k’asa Hudan ta nemi waje ta zauna kan kafet, gramma kuma ta zauna a kan d’aya daga cikin kujerun parlourn.
Nuna mishi ita kawai taga Granpa yayi, daganan taga mutumin ya nufuto…..setin ta ya zauna sannan ya bud’e d’an k’aramin akwatin da ya shigo da shi.
Sirinji ya d’auko da wani abu kamar cutting bud sai reza guda d’aya!
Sai da aka sha fama sannan aka d’auki jikin, daganan ya bata rezar yace “ta yanko farcenta” cuttonbud d’in kuma a bakinta kawai ta saka ta cire ta bashi, daganan ya d’an sa hannu ya ciri gashinta dake kwance akan goshinta wanda har sai da tasa k’ara dan ba kad’an ba taji zafi!
Daga nan ya mik’e ya cewa Granpa “nanda 24 hours in shaa Allah zai dawo”
Sannan yasa kai ya fice.
Gramma taso tayi mishi magana amman ganin yadda ya had’e rai ne yasa kawai ta kyaleshi suka koma d’aki ita da Hudan bayan ya sallamesu.
Iya gata Huda taga gata a wajen Gramma, amman dukda hakka Hudan zancenta d’aya ne “zata je wajen Mama”
Da kyar ta samu ta lallab’ata akan zuwa gobe za suje su duba Maman nata, sannan ta yarda tayi bacci mai cike da mafarkin Mama kala kala.....
Sai bayan isha tukunna Auwal ya dawo, daman saboda aikin da ya d’orawa kanshi kwana biyun nan sometimes har kusan kwana yake yi a office.
Aikin da ba nashi ba da wanda yake nashi duk yi yake…ya kuwa ci sa’a dan Granpa har ya d’an fara sauk’owa da kuma tunanin maidashi kujerarshi.