← Book details Siyasa Ko Kabilanci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 66

Sashe 9

Siyasa Ko Kabilanci Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read

Baban Ama... da Ammi duk suna a asibitin, Amatallah na kwance, idonta biyu, amma tarufesu, su Aminta ne kawai ked'an hira duk akan ciwonta.
Wayar baba tayi ringing, cikin fara'a ya d'auka yana fad'in "inaga brother ya iso kam".
" Assalamu alaika brother, halan harka shigo".
"Ai ganima a k'ofar asibitin".
Cikin zaro ido Baban Ama... Yace, " maimakon kaje gida kawai? dama isowarka nake jira natafi gidan, nazata can zaka wuce?".
"Ai bazan iyaba, sainaga jikin my best D.. first brother".
" humm, kai da d'iyar taka ba'asan gwaniba ai, bara nazo to nashigo dakai".
"Baban Ama... Ya iso kenan?". Cewar Ammi.
" eh wlhy, wai gashima a gate d'in asibitin".
"Ikon ALLAH, nazatama zai wuce gidane ai".
"kinsan halin brother, bara mushigo dai".
"To".
Duk abinda ake Amatallah na jinsu, amma batace komaiba, saima luf data sake yi a kwance, haka kawai taji gabanta ya tsananta fad'uwa, duk da dama yau Throughout haka ta wuni gabanta na fad'uwa, jitake kamar wani gagarumin abu zai faru da ita, shiyyasa dukta tsangwami kanta......
tun kafin su shigo k'amshin turarensa yayo gaba, Amatallah ta shak'a tareda kuma matse idanunta, still zuciyarta nacigaba da bugawa da sauri-sauri. Addu'a tafara karantowa, dan batasan dalilin wannan gudun da zuciyarta keyiba?, kuma tun ganinta Na farko da *_Uncle M.A_* a wancan zuwan hakance tafaru, harya tafi wancan time d'in idan suna waje d'aya koya shigo sai heartbeat d'inta taringayi kamar zata fito, kuma itakam a shekarun baya tana yarinya batajin hakan akansa, komiyasa yanzu kuma?...........
Sansanyar muryarsa ce ta katse tunaninta. bayan sun gama gaisawa da Ammi yamatso gaban gadon saitin face d'inta.
Yace, "My best daughter! barci kikeyine?".
Ya sallam!, tafad'a a zuciyarta. batasan ya zata musalta yanda cool voice d'in uncle M.A ke razana zuciyarta da dukkan magudanar jininta ba, jitake kaf duniya yafi kowa dad'in murya.
Babantane ya ta6a k'afarta tareda d'an bubbugawa.
Ta bud'e id
o ahankali tamkar mai barcin gaskiya, da uncle M.A tafara tozali, yana tsaye agaban gadon kusada fuskarta, sanye yeke cikin Cyan color d'in tattausan boyal, Wanda yasha d'inkin babbar riga, ya kafa hular zanna bukar black akansa da ratsin cyan kad'an, sai bak'in agogo da bak'in takalmi heir cover. Waro ido tayi cikin acting like tana mamaki ganinsa.
Tattausan murmushi ya sakar mata.
Ta yunk'ura a hankali tatashi zaune tana "lah Uncle yaushe kazo".
Still murmushin yakuma yi, kafin yace, " my best daughter yanzunnan nazo kina barci, ya jikin naki?".
"Da sauk'i uncle, ya hanya? Yasu Saifudden da jikin baba?".
"Everything Alhmdllh my best D..., amma gaskiyafa kin rame sosai, anya kinacin abinci my best?".
K'asa tayi da kanta tana murmushi, saikuma tad'an jinjina kai, tamkar wata k'adan garuwa. Tana fad'in ''inaci uncle, katanbayi baba da Ammi ma".
Murmushi yayi, sannan ya maida kansa ga babanta, " brother wai miya faru da my Daughter hakane?".
"Humm ai Brother inaga muje gida, sai muyi maganar a can, dan yinta anana zai iya zama danger gaskiya".
"okey, amma anbata sallamane?".
"No basu sallamemuba, inga dai k'ilan zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu, dan kaganta yanzudai normal, sai dare yayi jikin ya rikice, taita firgita, kullum akanta muke kwana babu barci wlhy".
" ya salam, abin yayi tsamari haka Dama?".
"Brother Amatallah dama haka take da rik'e Abu, shiyyasa kullum nake cikin fargabar irin mijin da ALLAH zai iya had'ata dashi, ba kowane zai iya d'aukar wannan rayuwan tataba gaskiya, so ina tausaya mata".
" karkace haka brother, muyi mata addu'a kawai, insha ALLAHU ALLAH zai bata miji nagari ma".
"To ALLAH yasa brother".
dahaka suka k'arasa motar sa.
Har sun shiga motar Baban Ama... Ya hango Ammi Na tahowa da sauri.
Kallon Uncle M.A yayi dake k'ok'arin jan motar yace, ''d'an dakata ga Ammin tanan, inaga munyi mantuwar keys d'in gid......
Bai k'arasaba Ammi tak'araso, keys d'in tamik'a masa kuwa tana fad'in "kun manta keys d'in ai. abinci nannan a seatroom Na shirya".
Murmushi Baban Ama... Yayi yana fad'in " jazakallahu khairan uwargidana".
Hararan wasa tamasa tace, "kuma amarya ba".
Duk su biyun dariya sukayi shida uncle M.A, Baban Ama... Yace, " ai nima aure zan k'ara, bakiga brother ma 2 Star ne ba? kilama yana shirin zama 3 ban saniba, gara nadage nayi nima Amatallah tasamu abokan shawara itama".
Juyawa Ammi tayi tana fad'in " wace zata auri tsoho?".
Dariya suka kumayi, sai da suka fita daga asibitin Uncle M.A yace, "brother mata basa girma akan kishi, wani lokacin har mamakinsu nake, komin k'ank'antar Abu sai yazama Na kishi a wajensu fa".
Baban Ama... Yace, ''ai kishi a jinin mata yake brother, babu mai iya rabasu dashi sai dai ALLAH kawai, kana daiji mi Saliha kefad'a yanzun, wai wazata auri tsoho? alhalin zan iyama d'aukar budurwa sa'ar Amatallah". Yak'are maganar da dariya.
Uncle M.A ma dariyar yakeyi, " kai brother, yanzu in ance ga budurwa sa'ar my daughter saika aura kuma?".
"Ah da guduma kuwa, kana ganin tamin kad'anne?".
" hhh kamata yawa dai brother, mumafa balaifi munja kwana a duniyarnan, kusan 47years fa".
"Ai brother rayuwa nabani tsoro wlhy, ALLAH dai ya gafarta mana, yau kake gobe sai labarinka, yanzu nan su kawu da mamana Khadija harsunyi 12years da rasuwafa kenan?".
" ajiyar zuciya uncle M.A ya sauke, yad'an shafa fuskarsa yayinda k'asan zuciyarsa yay rauni saboda Baban Ama... yata6o masa wani sashen rayuwarsa, cikin sanyin muryarsa yace, "hakane brother sunkai".
Yanda baba yaji muryar uncle M.A ta canja saiya canja hirar shima, ya d'akko hirar abinda yay sanadin kwanciyar Amatallah a asibiti.
Ahaka suka k'arasa gida, mamaki dukya cika Uncle M.A, cikin damuwa yace, " brother gaskiya ina wata shawara da zuciyata tun kusan 1year data wuce, akan wani rikici dayafaru, danake kallo a labarai sainaga duk matasane a wajen, sannan duksu akafi kashewa, hakan yatada hankalina wlhy, tun lokacin nake juya maganar araina, amma narasa dawa zan tattaunata, kasancewar nasan akwai fuskantar k'alubalen masu dafamin mu tallafi tafiyar.
Murmushi baban Ama... Yayi, kafin su zauna a kujerun seatroom d'in, uncle M.A yacire babbar rigarsa shima ya zauna, ruwanda Baban Ama...yazuba a cup yamik'o masa, kar6a yay yasha.
"Brother mikake rik'e a zuciya har kusan 1year? In dai ka yarda dani kafad'amin, insha ALLAH ina tare dakai 100%".
"Haba brother mikake tunani? ai duk duniya inka cire baba da innani babu Wanda yasanni sama dakai, kama fisu sanin wasu abubuwan akaina, dansu bakomai zan iya yi agabansuba kona fad'a musu, kaikam a sirrin rayuwata miye baka saniba brother?".
" tom naji, nayi kuskure, amin afuwa, yanzu fad'amin mike ranka to? Insha ALLAH ina tare dakai".
"Alhmdllh brother".......
Katseshi Baban Ama... yayi, bayan yagama zuba musu abincin, yace, "mufara cika tunbinmu, sai maganar tafi shiga to".
Dariya suka tuntsure dashi suduka, sannan Uncle M.A ya sakko.
______________________________
" Oga akwai fa matsala gaskiya".
Wani yaron zike ne ke magana cikin muryar maye.
Zike dake zaune kan dakalin sokawe Na toilet d'in primary school yana busa taba yad'ago jajayen idanunsa yana kallonsa, "matsalar mi manu!?".
" oga! Gagis fa bai wullaba wlhy, ance yana general hospital kwance, kaima kasan yana mik'ewa yak'ine kawai zai tashi, ALLAH wlhy".
Wata 'yar zabura zike yayi, yacire tabar dayake busawa daga bakinsa, kallon sauran yaransa yayi daduk suke a cake, wasuma kwance suke a k'asa, wasu kuma suna busa wiwi, wasu kuma rik'e suke da roban faro suna shan wani far in abu, ya maida kallonsa kan manu, ''kai waye yafad'a maka?".
"Oga ba d'azun ka aikeni gidan Oga Pam ba? natarar wannan shegen d'an koran nasa zasuje wai dubashi a asibiti, harda mai k'aton kannan da ido gulu-gulu kamar Na kasa jan goro a faranti".
Dariya duk suka bushe da ita, amma banda zike da hankalinsa ke a tashe, yasan wanene gagis sarai, tashinsa kuma bazai zama sauk'iba a garesu su dukansu, kallonsu yayi, duk suka tsaya da dariyar dasukeyi.
Yace, ''kai guys, dolenefa yau d'innan lahira tayi bak'on bawa, am telling you idan gagis yatashi sai kowa yabar jos, kuma kunsani".
Manu yamik'e yana tangad'i, " Oga shiyyasa nafad'a maka ai, yanzu hakafa yaransa nemanmu sukeyi, danma Oga Pam yayi gargad'in kar Wanda yayi wani abune, ammafa dayanzu anfara Caskale a garinnan, ALLAH wlhy". yay taga-taga zai fad'i, saikuma yarik'e bango.
"Yau Operation biyu garemu, dolane mu k'addamarma tsohon yarinyar can daya had'amu da kwalawa wlhy, sannan Na yayyaga uwarta a gabanta, itama haka, kafin Na wullasu gidan daba'a dawowa".
Dariya suka kuma bushewa da ita, yanzu kam harda zike.
Yacigaba da fad'in saikuma wancan sauran gawan gagis, har yaransa saina k'are musu tanadi,, yanzu kutashi muje lik'a posters d'in Oga, koba'aso dolene ayisa kokuma lahira tai bak'i wallayi".
(Duk cikin harshen turanci suke magana, Dan k'alilanne ma acikinsu kejin hausar, manu nema kad'ai bahaushe, saurankam kowanne dayarensa, kusandai yanda jos ta tara yarurruka iri-iri, wannan yasa aka cakud'e waje d'aya, baka isa cewa wannan yarene tsageraba a jihar, saboda matasansu a cakud'e suke, musamman ma irinsu zike marasa jin magana
Duk mik'ewa sukayi, kowannensu a buge yake, dan sunyi mank'as da kayan mayen da Oga Pam ya basu, wani buhu dake gefe suka d'auka, zike yabud'e yad'ebo posters yana raba musu, saida kowa yasamu sannan suka tafi, kowa yana rik'eda posters da gam na ruwa a hannu. Sai ihu suke suna kirari wa Oga Pam.
Jikin pols da bangon gidaje suke lik'a posters d'in, daduk inda yay musu, babu mai hanasu Dan ansan halin tsagerancinsu sarai. ihu suketa zabgawa.
"Wuyyyyyiiii huhuuuuuuuu!!!!!, sai Oga Pam ko jiki yay tsami, a za6esa dole ko wlhy uwar gayu tahaifi wani, wuuuuyii huhuuuuuu!!!!!!!.
Abinda suketa fad'a kenan, ba yaraba hatta manya gefe suka koma suna kallonsu. duk poster d'in da suka gani cireta sukeyi, inhar bata Mr Pam baceba.
Kad'an yarage fad'a ya kaure tsakaninsu da wasu matasan anguwar, wad'anda suka lik'a wasu posters da suke cirewa. amma wani dattijo yamusu magana. ALLAH yasa wad'ancan masu fahimtane, akwai sauran hankali a jikin, saisuka k'yalesu akan zasu had'une koba yauba.
Su zike kam filin nasune, haka sukaita bin anguwanni suna lik'e-lik'en fostar Mr Pam.
Wata anguwar a tanka musu, wani wajen kuma ayi kamarma ba'a gansuba. Saida suka gama tas sannan suka koma bayan Government primary school inda suka maida dan-dalin shaye-shayensu suka zauna maida numfashi, da hirar tsiyatakun dasukayi a yau d'in, wani suyi dariya. Wani suyi surutu da zage-zage.
_____________________________
Tunda suka fita Amattalah ta sauke ajiyar zuciya, gyara kwanciyarta tayi tana tunanin rashin zuwan Sadeeq saurayinta dubata.
Kobaiji batada lfy bane? Kokuma yazo tana barci halan?.
Gashin wayartama tana gida balle ta kirashi, kuma tanajin kunyar tambayar Ammi koyazo...........
*yawan comments, yawan kwazona fa
One luv my fans
*_ALLAH ka gafartama mahaifanmu._*
[1/16, 1:05 PM] Aysha Galadima: *_Typing
*_HASKE WRITER'S ASSO..._*
_{home of expert and perfect writer's}_
*_SIYASA KO K'ABILANCI_*
_(Hattara matasa)_
*_Bilyn Abdull ce
____________________
*_Number 7_*
____________________
*_WASHE GARI_*
Chapter 9 · 0% Book details