Sashe 57
Siyasa Ko Kabilanci Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
One Luv my sweet fans
*_ALLAH ka jik'an iyayenmu_*
[1/19, 10:28 PM] Aysha Galadima: *_Typing
*_HASKE WRITER'S ASSO..._*
_{home of expert and perfect writer's}_
*_SIYASA KO K'ABILANCI_*
_(Hattara matasa)_
*_Bilyn Abdull ce
____________________
*_Number 36_*
____________________
Da safe haka Ama... ta tashi jiki duk yana ciwo, ba k'aramar murza tashaba wajen Uncle a daren jiya, hakadai ta tak'ark'ara tayi break fast mai sauk'i, shikuma ta d'ind'uma masa tuwon, bayan ta kammala gyaran kitchen d'in da babban falo tayi wanka a gurguje tanufi samansa, tashinsa kenan a barcin daya d'an koma bayan sun dawo massalaci, toilet tawuce ta had'a masa ruwan wanka.
Ya langyare mata akan bazai iya yi da kansaba, shi jikinsa ciwo yake masa, "jiya duk kin bani wahala my best".
Idanu Amatallah tazaro waje, " Uncle wato nimace nabaka wahalar ko? nan k'asusuwana sai ciwo sukeyi tamkar naje noma, shine zaka dawo da abin kaina ma".
Dariya yamata, "oh babyna zo namiki tausa saiki warware gaba d'aya".
" wad'in? tabd'i, Uncle ni zakama wayo? ai idan ka ganni lahira kaini akayi, ni yauma nayafe kwannan wa Anty Fateema, ta had'a uku kawai".
"Lallai yarinya kinma Isa, yau ma muna tare yini guda, namaso ace girkin naki yakama asabar da lahadine, humyim dakin fad'ama jama'ar jos".
Cikin dariya tace, " Uncle!, koda yake ni kama tunaminfa, Anty Aneesa na wucewa nima zan had'a kayana sai jos, wata biyu zanyo".
Wani kallo yamata na idan na kamaki saikin fad'i dawa kike. yashige toilet yana murmushi da cije le6ensa na k'asa.
Itama dariyar tayi tahau gyaran gadon, kafin yafito tagama gyaran bedroom d'in tsaf takoma falo yafito, bai katse mata aikintaba yayi shirinsa da kansa, k'ananun kaya yasaka, Dan babu inda zaije, yana gida cikin iyalinsa yau.
Cikin nishad'i sukayi break fast atare yau ma, daganan suka fito harabar gidan shan iska, yara suna wasan 6uya tareda Amatallah, Uncle da su Aneesa suna musu dariya, abinne ya burge Uncle yashiga shima, ganin haka Fateema da Aneesa suma suka shigo, akabar Siddiqa tanama Mah-mah wasa.
Fateema ta d'aurama Uncle k'yallen a fuska aka rufe masa ido, daganan kowa yanemi wajen 6uya, Uncle kuma yafara lalubensu, daga bayansa Aneesa taja rigarsa, yajuyo da sauri yakai hannu zai kamata ta zille tana dariya, Amatallah ma ta ta6a hannunsa, itama ta zille masa, Sahib yazo gabansa yana fad'in "Abbu gani ka kamani". da sauri Uncle yajuyo inda yake shima, amma Sahib ya gudu, Dariya suketa masa suduka, shikuma yana bin sautin dariyar amma yakasa kama kowa, daga k'arshedai ya damk'i Saifudden, nanfa suka saka masa tafi da ambatar an kama Saifi! an kama saifi!!.
Handkerchief d'in Uncle yacire yana dariya shima, Saifudden aka d'aurama sa, kowa ya matsa, shima ta6asa sukaitayi suna guduwa da dariyar yanda yake laluben san kama wani, Abulkhairi yazo ta6ashi ta baya ALLAH yabama saifudden ikon damk'oshi, shima aka d'aura masa, Abulkhairi baisha wahalar damk'e Aneesa ba shima, yahau dariyar yakama momy Yakama momy, su Uncle na tayashi da tafi, itama Aneesa aka d'aura mata, aiko da k'yar takama Ummita itakuma, Ummuta koda aka d'aura mata dawayo tad'an d'aga kad'an tana gani da ido d'aya, tashin farko ta damk'o Amatallah, itama aka d'aura mata, itama tafi shan wahalar kafin ta damk'o Fateema da Sahib lokaci d'aya, akadai d'aurama Fateema, sunta zagaya gida ana dariya Sam ta kasa kamo kowa, sai can tarutsa Uncle dayaja mata d'an kwali tayi azamar kama damtsen hannunsa...
Haka suka yini cikin nishad'i, daga wannan wasa su koma wancan har lokaci yaja, kowa yagaji suka shige ciki aka zube a falo ana maida numfashin gajiya. Amatallah tashiga kitchen ta had'a abincin rana, daganan kowa yad'an watsa ruwa saboda zufar dasukayi wajen wasa, sai bayan sallar la'asar Uncle yad'an fita zuwa gidansu.
Yau ma haka suka kashe juna da soyayya shida Amarsa.
Washe gari suka yini gidansu Innani suduka har yaran, koda suka dawo da daddare miji yakoma hannun Fateema, itama haka taita shagalin damk'e kayanta, Yakuma kar6eta tamkar ba ranar yarabu dawata macenba, ya nunu mata soyya mai tsayawa arai da tattalinta tamkar itakad'aice gareshi.
Washe gari Monday, yara da Ama..... Duk suka tafi makaranta, shima Uncle yafice harkokin gabansa, kasuwa yafara zuwa ya gaggaisa da jama'a da duba yanda komai ke tafiya, sannan yad'an Shiga B.U.K, bai dad'eba yafito danufi tafiya, Amatallah ma batasan yazoba, tanacan sunata hirarsu dasu Rita bayan sunfito lecture a gajiye sunad'an hutawa kafin ashiga wata.
Harya bud'e mota yaji ana masa sallama a bayansa, juyowa yayi batareda ya rufe k'ofarba.
Yad'an had'e fuska Dan ganin yarinyar datake Neman takura rayuwarsa a kwanakinnan (zee), inhar zaishigo b.u.k saitazo wajensa, dukda bata fito fili tace tana sonsaba take-takenta sun nuna masa hakan.
Canjin fuskarsa baisa tadamuba, ta gaisheshi cikeda ladabi.
Amsawa yayi yana tambayarta ya karatu.
Tace, "Alhmdllh ya iyali?".
Bai amsaba yace, " yau ma tambayarce?".
Murmushi tamasa tana gyaran tsayuwa, "eh to kusan haka, amma tayau tasha banban data ranar sir".
" lallaikam, gashi kuma ni INA saurine" yay maganar yana kallon agogon hannunsa da gyaran babbar rigarsa ta farar shadda.
"Babu damuwa sir, in ban takurakaba kawai kabani number d'inka, koda ta test message ne saina turo tambayar".
Yad'an kalleta kad'an, sanye take cikin gown ta material bak'i da d'igon Fari, sai siririn gyalenta Fari data yafa akanta, doguwace babu laifi, sannan tanada haske sosai, kuma yakula 'Yar gayu ce, ko magana a yangance take yinta, zata iya Girman Amatallah koda da shekara uku ne ko biyu, kauda idonsa yayi batareda ya tankaba, ya d'akko card d'insa d'aya yabata sannan yashige motar.
Cikin salonta tace, " INA godiya da wannan karamci, daka mini".
Wani murmushi kin gundireni yamata yatada motar yatafi.
Ta sumbaci card d'in tana wani lumshe idanu da shak'ar k'amshinsa daya mannewa card d'in sannan tabar wajen tana mai addu'ar ALLAH ya mallaka mata bawan ALLAHn nan.
Nace hummm.
Alhaji Sabi'u dake zaune gefensa Wanda soyayya tarufe idon zee ko ganinsama ita batayiba ya kalli Uncle d'in yana 'Yar dariya.
"Mutumina kodai ta hud'uce?".
Uncle yakuma dafe sitiyarin da k'yau yana murmushi, ''haba Alhajina ai ka tausayamin kaima, inani ina mata hud'u? Uku nan sun isheni, ni banima da kud'in aure a yanzu balle inda zan ajiye matar, kawai dai yarinyarce nima naga take-taken nata auren suka dosa".
" a kawai kashiga kaima, indai kud'in aurene matsalarka ALLAH zai kawo".
"Hhh lallaikam Alhaji Sabi'u, to aini yanzuma babu wani gurbi da wata mace zata samu a zuciyata, matana sun mamaye ko ina da ina, harma bana kallon matan dawani fasali, kainema yakamata kashiga ta uku kawai wlhy".
" a to tunda abin kaina zai dawo abar maganar kawai".
Dariya sukayi gaba d'aya suna cigaba da tsokanar juna har suka kai inda zasuyi meeting d'in nasu.
Kusan kowama ya hallara su ake jira. babu 6ata lokaci suka fara abinda ya tarasu.
Sun tattauna akan abubuwa masu yawa dasuke damun k'ungiyar sannan suka koma kan neman hanyar samun kud'in shiga, kowa yana kawo shawararsa.
Alhaji Murtala yace, "toko zamuci bashin bankine mu kafa wasu sana'oi kafin muga abinda ALLAH zaiyi".
"Amma Alhaji murtala bama tsoron gudun Matsala nan gaba? Idanfa adadin maida kud'in yayi bamu sami yanda muke soba akwai matsala kenan".
" ito dakuma wannan, to'ai munada sauran kud'i mizai hana muduba wani kasuwanci mai saurin kawo kud'i".
"Wannan shawarar tayi kam, toga wata hanya danake d'an shakkar fad'arta da".
" wace hanyace? Kafad'a kawai kanka tsaye Alhaji Isa".
Nisawa yayi kafin yace, "kwangilace dama ta gwamnati, tun kwanaki governor yamin maganar amma nad'ank'i bashi had'inkai saboda wani dalilina, to yanzu mizai hana mu kar6a amatsayin k'ungiya, ni dama banason amsane alokacin gudun gutsiri tsomar 'yan siyasar k'asarnan".
Uncle ya jinjina kai yace, " yayi sosai, yanzu saikamasa maganar kenan?".
"Shikenan, saimuje a k'ungiyane to, zan sama mana damar ganinsa kenan".
" okey shikenan to".
(Alhaji Isa sirikine ga governor, shiyyasa yakeda lasisin ganinsa cikin kwanciyar hankali akuma duk sanda yaso, yak'i kar6ar kwangilar ne abaya saboda gudun surutai na jama'a, shima kuma ALLAH yaymasa rufin asiri dai-dai gwargwado, kuma yana bada muhimmiyar gudunmawa akan k'ungiyar, da kud'insa dakuma aikin kai da kai dasuka saka Kansu).
Sun dad'e suna kuma tattauna wasu hanyoyin kafin su tashi kowa yakoma kan harkokinsa.
Uncle dai kasuwa ma yakoma.
***********
*Bayan sati d'aya*.
Wannan karon kam a d'akin Fateema yagama kwanakinsa saikuma Aneesa ta kar6esa, randa zaibar wajenta ne kuma ranar tafiyarta Ghana, dayake anma yara hutun school, shiyyasa tatafi harda Sahib da saifudden da Uncle dazai mata rakkiya ya kwana biyu ya dawo.
Suntafi sunbar Fateema da Amatallah da kewa, duk saida suka had'a tsaraba suka bata ta kaima danginta. ta nunamusu jin dad'inta da godiya agaresu, shima Uncle yaji dad'i sosai, da kumajin k'aunar matan nasa sosai a ransa.
Sunsha hira harda Nazeefa data zo Dan tayasu zaman kwana biyu kafin Uncle ya dawo.
*_ALLAH ka jik'an iyayenmu_*
[1/19, 10:28 PM] Aysha Galadima: *_Typing
*_HASKE WRITER'S ASSO..._*
_{home of expert and perfect writer's}_
*_SIYASA KO K'ABILANCI_*
_(Hattara matasa)_
*_Bilyn Abdull ce
____________________
*_Number 36_*
____________________
Da safe haka Ama... ta tashi jiki duk yana ciwo, ba k'aramar murza tashaba wajen Uncle a daren jiya, hakadai ta tak'ark'ara tayi break fast mai sauk'i, shikuma ta d'ind'uma masa tuwon, bayan ta kammala gyaran kitchen d'in da babban falo tayi wanka a gurguje tanufi samansa, tashinsa kenan a barcin daya d'an koma bayan sun dawo massalaci, toilet tawuce ta had'a masa ruwan wanka.
Ya langyare mata akan bazai iya yi da kansaba, shi jikinsa ciwo yake masa, "jiya duk kin bani wahala my best".
Idanu Amatallah tazaro waje, " Uncle wato nimace nabaka wahalar ko? nan k'asusuwana sai ciwo sukeyi tamkar naje noma, shine zaka dawo da abin kaina ma".
Dariya yamata, "oh babyna zo namiki tausa saiki warware gaba d'aya".
" wad'in? tabd'i, Uncle ni zakama wayo? ai idan ka ganni lahira kaini akayi, ni yauma nayafe kwannan wa Anty Fateema, ta had'a uku kawai".
"Lallai yarinya kinma Isa, yau ma muna tare yini guda, namaso ace girkin naki yakama asabar da lahadine, humyim dakin fad'ama jama'ar jos".
Cikin dariya tace, " Uncle!, koda yake ni kama tunaminfa, Anty Aneesa na wucewa nima zan had'a kayana sai jos, wata biyu zanyo".
Wani kallo yamata na idan na kamaki saikin fad'i dawa kike. yashige toilet yana murmushi da cije le6ensa na k'asa.
Itama dariyar tayi tahau gyaran gadon, kafin yafito tagama gyaran bedroom d'in tsaf takoma falo yafito, bai katse mata aikintaba yayi shirinsa da kansa, k'ananun kaya yasaka, Dan babu inda zaije, yana gida cikin iyalinsa yau.
Cikin nishad'i sukayi break fast atare yau ma, daganan suka fito harabar gidan shan iska, yara suna wasan 6uya tareda Amatallah, Uncle da su Aneesa suna musu dariya, abinne ya burge Uncle yashiga shima, ganin haka Fateema da Aneesa suma suka shigo, akabar Siddiqa tanama Mah-mah wasa.
Fateema ta d'aurama Uncle k'yallen a fuska aka rufe masa ido, daganan kowa yanemi wajen 6uya, Uncle kuma yafara lalubensu, daga bayansa Aneesa taja rigarsa, yajuyo da sauri yakai hannu zai kamata ta zille tana dariya, Amatallah ma ta ta6a hannunsa, itama ta zille masa, Sahib yazo gabansa yana fad'in "Abbu gani ka kamani". da sauri Uncle yajuyo inda yake shima, amma Sahib ya gudu, Dariya suketa masa suduka, shikuma yana bin sautin dariyar amma yakasa kama kowa, daga k'arshedai ya damk'i Saifudden, nanfa suka saka masa tafi da ambatar an kama Saifi! an kama saifi!!.
Handkerchief d'in Uncle yacire yana dariya shima, Saifudden aka d'aurama sa, kowa ya matsa, shima ta6asa sukaitayi suna guduwa da dariyar yanda yake laluben san kama wani, Abulkhairi yazo ta6ashi ta baya ALLAH yabama saifudden ikon damk'oshi, shima aka d'aura masa, Abulkhairi baisha wahalar damk'e Aneesa ba shima, yahau dariyar yakama momy Yakama momy, su Uncle na tayashi da tafi, itama Aneesa aka d'aura mata, aiko da k'yar takama Ummita itakuma, Ummuta koda aka d'aura mata dawayo tad'an d'aga kad'an tana gani da ido d'aya, tashin farko ta damk'o Amatallah, itama aka d'aura mata, itama tafi shan wahalar kafin ta damk'o Fateema da Sahib lokaci d'aya, akadai d'aurama Fateema, sunta zagaya gida ana dariya Sam ta kasa kamo kowa, sai can tarutsa Uncle dayaja mata d'an kwali tayi azamar kama damtsen hannunsa...
Haka suka yini cikin nishad'i, daga wannan wasa su koma wancan har lokaci yaja, kowa yagaji suka shige ciki aka zube a falo ana maida numfashin gajiya. Amatallah tashiga kitchen ta had'a abincin rana, daganan kowa yad'an watsa ruwa saboda zufar dasukayi wajen wasa, sai bayan sallar la'asar Uncle yad'an fita zuwa gidansu.
Yau ma haka suka kashe juna da soyayya shida Amarsa.
Washe gari suka yini gidansu Innani suduka har yaran, koda suka dawo da daddare miji yakoma hannun Fateema, itama haka taita shagalin damk'e kayanta, Yakuma kar6eta tamkar ba ranar yarabu dawata macenba, ya nunu mata soyya mai tsayawa arai da tattalinta tamkar itakad'aice gareshi.
Washe gari Monday, yara da Ama..... Duk suka tafi makaranta, shima Uncle yafice harkokin gabansa, kasuwa yafara zuwa ya gaggaisa da jama'a da duba yanda komai ke tafiya, sannan yad'an Shiga B.U.K, bai dad'eba yafito danufi tafiya, Amatallah ma batasan yazoba, tanacan sunata hirarsu dasu Rita bayan sunfito lecture a gajiye sunad'an hutawa kafin ashiga wata.
Harya bud'e mota yaji ana masa sallama a bayansa, juyowa yayi batareda ya rufe k'ofarba.
Yad'an had'e fuska Dan ganin yarinyar datake Neman takura rayuwarsa a kwanakinnan (zee), inhar zaishigo b.u.k saitazo wajensa, dukda bata fito fili tace tana sonsaba take-takenta sun nuna masa hakan.
Canjin fuskarsa baisa tadamuba, ta gaisheshi cikeda ladabi.
Amsawa yayi yana tambayarta ya karatu.
Tace, "Alhmdllh ya iyali?".
Bai amsaba yace, " yau ma tambayarce?".
Murmushi tamasa tana gyaran tsayuwa, "eh to kusan haka, amma tayau tasha banban data ranar sir".
" lallaikam, gashi kuma ni INA saurine" yay maganar yana kallon agogon hannunsa da gyaran babbar rigarsa ta farar shadda.
"Babu damuwa sir, in ban takurakaba kawai kabani number d'inka, koda ta test message ne saina turo tambayar".
Yad'an kalleta kad'an, sanye take cikin gown ta material bak'i da d'igon Fari, sai siririn gyalenta Fari data yafa akanta, doguwace babu laifi, sannan tanada haske sosai, kuma yakula 'Yar gayu ce, ko magana a yangance take yinta, zata iya Girman Amatallah koda da shekara uku ne ko biyu, kauda idonsa yayi batareda ya tankaba, ya d'akko card d'insa d'aya yabata sannan yashige motar.
Cikin salonta tace, " INA godiya da wannan karamci, daka mini".
Wani murmushi kin gundireni yamata yatada motar yatafi.
Ta sumbaci card d'in tana wani lumshe idanu da shak'ar k'amshinsa daya mannewa card d'in sannan tabar wajen tana mai addu'ar ALLAH ya mallaka mata bawan ALLAHn nan.
Nace hummm.
Alhaji Sabi'u dake zaune gefensa Wanda soyayya tarufe idon zee ko ganinsama ita batayiba ya kalli Uncle d'in yana 'Yar dariya.
"Mutumina kodai ta hud'uce?".
Uncle yakuma dafe sitiyarin da k'yau yana murmushi, ''haba Alhajina ai ka tausayamin kaima, inani ina mata hud'u? Uku nan sun isheni, ni banima da kud'in aure a yanzu balle inda zan ajiye matar, kawai dai yarinyarce nima naga take-taken nata auren suka dosa".
" a kawai kashiga kaima, indai kud'in aurene matsalarka ALLAH zai kawo".
"Hhh lallaikam Alhaji Sabi'u, to aini yanzuma babu wani gurbi da wata mace zata samu a zuciyata, matana sun mamaye ko ina da ina, harma bana kallon matan dawani fasali, kainema yakamata kashiga ta uku kawai wlhy".
" a to tunda abin kaina zai dawo abar maganar kawai".
Dariya sukayi gaba d'aya suna cigaba da tsokanar juna har suka kai inda zasuyi meeting d'in nasu.
Kusan kowama ya hallara su ake jira. babu 6ata lokaci suka fara abinda ya tarasu.
Sun tattauna akan abubuwa masu yawa dasuke damun k'ungiyar sannan suka koma kan neman hanyar samun kud'in shiga, kowa yana kawo shawararsa.
Alhaji Murtala yace, "toko zamuci bashin bankine mu kafa wasu sana'oi kafin muga abinda ALLAH zaiyi".
"Amma Alhaji murtala bama tsoron gudun Matsala nan gaba? Idanfa adadin maida kud'in yayi bamu sami yanda muke soba akwai matsala kenan".
" ito dakuma wannan, to'ai munada sauran kud'i mizai hana muduba wani kasuwanci mai saurin kawo kud'i".
"Wannan shawarar tayi kam, toga wata hanya danake d'an shakkar fad'arta da".
" wace hanyace? Kafad'a kawai kanka tsaye Alhaji Isa".
Nisawa yayi kafin yace, "kwangilace dama ta gwamnati, tun kwanaki governor yamin maganar amma nad'ank'i bashi had'inkai saboda wani dalilina, to yanzu mizai hana mu kar6a amatsayin k'ungiya, ni dama banason amsane alokacin gudun gutsiri tsomar 'yan siyasar k'asarnan".
Uncle ya jinjina kai yace, " yayi sosai, yanzu saikamasa maganar kenan?".
"Shikenan, saimuje a k'ungiyane to, zan sama mana damar ganinsa kenan".
" okey shikenan to".
(Alhaji Isa sirikine ga governor, shiyyasa yakeda lasisin ganinsa cikin kwanciyar hankali akuma duk sanda yaso, yak'i kar6ar kwangilar ne abaya saboda gudun surutai na jama'a, shima kuma ALLAH yaymasa rufin asiri dai-dai gwargwado, kuma yana bada muhimmiyar gudunmawa akan k'ungiyar, da kud'insa dakuma aikin kai da kai dasuka saka Kansu).
Sun dad'e suna kuma tattauna wasu hanyoyin kafin su tashi kowa yakoma kan harkokinsa.
Uncle dai kasuwa ma yakoma.
***********
*Bayan sati d'aya*.
Wannan karon kam a d'akin Fateema yagama kwanakinsa saikuma Aneesa ta kar6esa, randa zaibar wajenta ne kuma ranar tafiyarta Ghana, dayake anma yara hutun school, shiyyasa tatafi harda Sahib da saifudden da Uncle dazai mata rakkiya ya kwana biyu ya dawo.
Suntafi sunbar Fateema da Amatallah da kewa, duk saida suka had'a tsaraba suka bata ta kaima danginta. ta nunamusu jin dad'inta da godiya agaresu, shima Uncle yaji dad'i sosai, da kumajin k'aunar matan nasa sosai a ransa.
Sunsha hira harda Nazeefa data zo Dan tayasu zaman kwana biyu kafin Uncle ya dawo.