← Book details Siyasa Ko Kabilanci Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 66

Sashe 46

Siyasa Ko Kabilanci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

____________________ *_Number 30_* ____________________ Tashiga bedroom d'insa da sallam, harya fara k'ok'arin cire babbar rigarsa, saida yagama cirewa ya ajiye sannan tace, "sannu da zuwa Uncle". Ya amsa yana k'ok'arin fara cire mafallan rigarsa ta ciki, juyawa tayi tana fad'in " Uncle bara inje, idan ka gama saina daw........" Da sauri yarik'o hannunta tadawo baya, yad'an had'e fuska kad'an idonsa akanta. Maida nata k'asa tayi tana kallon k'afafunsu, duk kuma saitaji babu dad'i, ta marairaice murya kamar zatayi kuka dan ganin ya rik'eta kuma yayi shiru. "Uncle please miya faru?". Ta d'anso bashi dariya amma saiya kanne, yasa yatsu biyu ya d'ago ha6arta. idonsa taga ya k'ank'ance yana mata wani kallon da yasha banban dana kowacce rana, da sauri ta janye daga kallonsa. Yad'anyi gyaran murya. Hakanne yasata dole takuma kallonsa. Girarsa d'aya a d'age yace, " Khadeeja kinason kishiyoyinki su rainaki ko?". Cikeda mamaki tace, "Uncle kamar ya?". " kamar yanda kike nuna halin ko inkula akan mijinki. Haka kikaga su Aneesa namin? Sai dafa akace ki biyoni kika taso, Daba ace ki bizoba ma baki zuwa kenan ko?". Kanta ta girgiza masa alamar a'a. "To miyasa ke bakya koyi dasu? Ina kallonki kamar mai wayo amma ba haka bane ashe". A shagwa6e kamar zatayi kuka tace, " ALLAH uncle inajin kunyane, amma kayi hak'uri bazan sakeba zan canja insha ALLAH". Sai yanzu taga yasaki wani lallausan murmushi yana shafa gemunsa, murya k'asa-k'asa tamkar mai gudun ajisu yace, "Kunyace kawai matsalarki my babie? Karki damu zan canjaki da kaina ma kafin ki canja kanki". A kasalance ta d'aga masa kanta, saboda dukkan illahirin jikinta yamutu murus da salon Na Uncle. Ya d'an murmusa tare da bata sumbata a goshi, ya saki hannunta yacigaba da cire ma6allan rigarsa, itadai Amatallah kanta a k'asa takasa kallinsa. Tsaf ya cire komai, dagashi sai vest da boxer, yatako a hankali zuwa gabanta, duk'owa yayi saitin kunnenta, har tanajin saukar numfashinsa a dokin wuyanta, yace, "indai kunyace yau d'innan zan cireta kowama ya huta". yana gama fad'a yashigewarsa toilet yana wani murmushi mai k'ayatarwa. Rufe k'ofarce tadawo da Amatallah hayyacinta, tabi k'ofar da kallo tana cigaba da juya maganganunsa, sometimes takanyi mamakin Uncle da halayensa, gaba d'aya ya canja mata yanzu, kai tsaye yake mata abubuwa ko kunya babu, maganarsa ta k'arshe tafad'o mata arai, sai kuma taji gabanta ya fad'i. a fili ta furta ''ALLAH yasa ba abinda nake zaton bane". Bata bar wajenba saida taji motsin zai fito ta gudu falo. Baiyi mamakin rashin ganintaba, dan yasan dama bazata tsayaba, d'an murmushi yayi yacigaba da goge jikinsa da k'aramin towel. Amatallah Na zaune afalo ta k'urama TV ido, saidai azahiri hankalinta bama akansa yakeba, yana kan tunanin maganar Uncle ne, dukda wani 6angare Na zuciyarta yana fad'a mata ba haka bane. Jin anjawota yasakata yin firgigit tadawo hayyacinta, da sauri ta kallesa dukda daddad'an kamshinsa ya tabbatar mata shine. baiyi maganaba, sai hijjabinta daya cire. "Kai my best! wai ina kika sami turaren nan mai narkar danine?". Yayi maganar cikin kunnenta. Hannu tasa tarufe fuskarta tana murmushi, ''kai Uncle naka ai yafi nawa dad'i". Ya murmusa a karo Na barkatai tare da kuma jawota sosai a jikinsa yana shinshinar wuyanta, tuni ya fara sakar mata wasu zafafan kisses, daga haka aka koma (abinda Malam ya hanani fad'a Tunfa Amatallah Na kallon lamarin a matsayin k'arami harya koma fin k'arfin, turarenta, gaba d'aya yagama birkita boss bayaji baya gani, ya mantafa (Khadija ce d'iyar brother), saida ya rud'ar mata dadukkan jiki da.......sannan ya fara Ankara a falon suke, kuma koyaushe cikin yaran wani zai iya shigowa dan k'ofar abud'e take. daga ita harshi tagwayen ajiyar zuciya suke saki, jikin Amatallah sai 6ari yakeyi, ta duk'ar dakai ta kasa kallonsa ko sau d'aya. Shikansa kunyace takamashi, amma saiya Fiske ya sauka k'asa yana fad'in ''sakko kibani abinci yunwa nakeji my best". Yay maganar murya a shak'e tamkar mai Mura. Tamkar Amatallah ta FASA kuka haka ta sakko tazuba masa sakwara dataji daka tayi luk'uy, tuni k'amshi ya gauraye hancin Uncle, harma ya k'agara tazuba ya fara zubama cikinsa. Aiko tasha mamakin yanda taga yaci abincin sosai, sannan bai matsa mataba datace ta k'oshi, saiya tura mata Leda d'aya acikin ledojin da Sahib ya kawo. Shiru tayi tana kallon ledar, yad'ago kai yana kallonta, suna had'a ido tayi azamar janye nata tana d'an tura Baki gaba. Yayi murmushi mai sauti yana fad'in "garama kichi yarinya, shikuma bakin anjima kad'an zaimin bayani dalla-dalla". Kuma tunzuro baking tayi, yajawo ledar yana bud'ewa, kazace datasha gashi mai kyau sai k'amshin dad'i takeyi, ga kayan had'i Na musamman tasha na salad, sai yoghurt mai sanyi Na hollandia. Gabanta ya tura yacigaba dacin sakwararsa yana zuba mata Santi. Tun tana gimtse dariya harta fara yinta a fili. dole yashagala a kallonta, harya kammala batakoci lauma d'ayaba akazar, ya wanke hannunsa tare da ture kwanikan gefe ya jawota jikinsa. Da Kansa yaciyar da ita kazan, tun tana basarwa harta saki jiki taci, shima yoghurt d'in tasha babu laifi. Nace, " habawa Ama....sai Uncle yamiki irin ta (Ya khaleel Na *Ciki da gaskiya* ya tsareki kibiyasa kazarsa tamkar yanda Sholly tabiya ya Khaleel itama). Bayan sun gama ta tattara wajen, ta d'auki kwanikan zata sauka dasu. Harta kama handle d'in k'ofar yace, "sauran kuma saina biyoki yauma". Shiru tayi batace komaiba, sannan kuma bata fitaba. Harya d'auke kansa yakuma kallonta, " Yaya dai?". Idonta tab da kwalla tace, "Uncle yaufa su Anty maijidda anan zasu kwana". " to saimi yafaru dan anan zasu kwana? hakan Na nufin bazaki kwana d'akin mijinki ba kenan?". Kasa cewa komai tayi. Yace, "minti talatin nabaki kacal, idan zaki dawo kizomin da Lipton". Kallonsa tayi zatayi magana taga yayi kicin-kicin da face. A sanyaye tafice. Tana dire kayan a kitchen Anty maijidda ta shigo, hannunta kawai takama batareda tayi maganaba suka shige 6angarenta. Mamaki ya kama Amatallah data tadda abubuwa saman gadonta, nanma Anty maijidda batayi maganarba tabata Abu a kofi tace shaye. Kar6a Amatallah tayi babu musu ta shanye, tasandai Anty maijidda bazata cutar da itaba, abinkam yamata dad'i sosai, kamar madara kamar waken suya dai, kai tagaza gane minene. Wani d'an kad'an kuma Anty maijidda ta kuma bata, shima dai akwai dad'i, tabata wasu turarurruka kala hud'u, kowanne tamata bayanin inda zata shafashi, (ko kunya Anty maijidda bataji) cewar Amatallah a zuciya....... Maganar Anty maijidda ta kuma katseta, idan kingama ki fesa wannan turaren kuma dukkan jikinki sannan ki saka wannan rigar barci, ga zani nan ga hijjab nan, in kin k'iyi kuma zangane". tana gama fad'a tafice ta barta. Binta kawai Amatallah tayi da kallo, kafin tatashi tafara yin duk yanda tace tayi. Cikin mintuna 20 Amatallah ta had'e, ga wani k'amshi daya kusa bugamin kwanya tana zubawa, (jinai inama ta sanmin nima na birkita my Abdull ...lol). Zani ta saka da hijjabin dasuma keta k'amshi sannan tafito falonta, tsaye tayi tana tunani, waikuma yanzun dolene tajefa gaban Uncle ahaka? Itafa rigar barcinan kunyama take bata. Kodayake bazata cire zani da hijjab d'inba komi Uncle zai mata. Da wannan tunanin tanufi kitchen, black tea ta had'a masa kamar yanda ya buk'ata, ta d'ora akan k'aramin tire tafito. A falo sukaci karo da Aneesa, kallan kallo akaima juna, Amatallah tawuce batareda ta tankaba. Aneesa ma tashige nata 6angaren rai a 6ace, a ganinta da biyu Amatallah ta mata haka, ga wani k'amshi na masifa daya baje gidan ajikin Ama..... (Hhhhhh to mita miki Anee? Kodai kishinne ya motsa? Tad'an dad'e tsaye a bakin k'ofa tanata sak'awa da kwancewa, Uncle kam duk yana kallonta ta labule, dan tunda tafara tako steps d'in k'amshinta ya iso masa. Ganin tak'i shigowa yace, "kona kawo miki bargon kwanciya my bes...... Ai bata bari ya k'arasaba ta shigo falon. Kauda kansa yayi yana danne dariyar dake taho masa. Shan tea yake yana satar kallonta, saida yagama tsaf sannan yatashi yashiga bedroom d'insa, mintuna kusan 5 yafito da alamar alwala yayi. Kallonta yayi yace, " shiga kiyo alwala". "Uncle nafayi isha'i har shafa'i da wutirima". " nasani aii, jeki dai kiyi". Bata kuma cewa komai ba taje tayo alwala a toilet d'insa. Yajasu sallah raka'a biyu yad'ora da addu'oin fatan alkairi da zaman lafiya agaresu, da had'in kan iyalansa, yay addu'a mai tsawon gaske akan mahaifinta, harda 'yan kwallansa kuwa, Amatallah kam kuka takeyi rurus harda shashsheka. Bayan sun shafa ya rungumeta yana lallashi da fad'a mata kalamai masu kwantar da hankali, daga nan aka zarce da soyayya saboda kukanta ya kasa k'arewa, jin bakinsa cikin nata kuwa yasata had'iye kukan tilas. (abinda yabiyo baya kuma Malam yahana fad'a Ganin fa za'ai abin kunya a falo ya cukuykuyi kayarsa sukai d'akinsa. Inason binsu ina tsoron kar garin Neman gira arasa ido, kafinma Na yunk'ura Na tashin najiyo Uncle M.A ya Mirza makulli alamar basa buk'atar kallon k'urilla , inba so kuke kuma Uncle yafad'ama Malam Na lek'aba.... to mu hak'ura kawai idan Ama... tafito tabamu labari , hanyar lafiya a bita da shekara ). Koya kukace my guys Kukan dana jiyo na Amatallah da kwala d'an wani ihunta wanda nake addu'ar ALLAH yasa nikad'ai naji banda (Aneesa ko Uwargida fateema ), yasani fad'ar shikenan Uncle ya wuce wajen, (Amatallah team yaufa kune aciki su Aneesa a kwana ) masoyan Anee amin afuwa. Ina nan zaune na zabga tagumi da jiran fitowar Uncle idan yagama ta6argarzar Anja wani d'an lokaci nalek'a da k'yau ta kafar makulli, can na hango Uncle rungume da Amatallah tana zabga kuka tamkar ranta zai fita, shiko babu abinda yake fad'a sai "ALLAH ya albarkaci rayuwarki my Heartbeat, Jazakallahu khairan! Jazakallahu bil jannah Amintacciya ma abociyar kame mutunci da bin dokokin Ubangiji, tabbas nayi k'yak'yk'yawan zato akanki, kumma kin tabbatar min hakan yau, yakuma k'ank'ameta da bata wasu zafafan kisses Wanda yasaka Amatallah tsaida kukanta dole saikuma shashsheka. Cikin kunnenta yacigaba da fad'a mata sirrin zuciyarsa (banajinsu fa Adaren dai Alhaji Muhammad bai bar Amatallah ba saida ya taimaka mata tagyara jikinta tsaf tana zuba masa shagwa6a wadda ke sake dulmiyasa a k'aunarta Yabata sauran yoghurt d'in tasha da Paracetamol sannan ta kwanta. Lalla6ata yaytayi har tayi barcinta tanata sauke ajiyar zuciya lokaci-lokaci. Ahankali yake shafa kanta yana murmushi, ya sumbaci la66anta da goshi akaro na babu adadi " I love you so much my heartbeat, ALLAH ka
Chapter 46 · 0% Book details