Sashe 38
Siyasa Ko Kabilanci Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amatallah Na sauka tayi hamdala ga ubangiji data kubtar da ita.
Nace, "humm".
******
Abinda yabani mamaki koda Na lek'a wajen Aneesa saina taddata hankali kwance, tana zaune a falo tanama Siddiqa shirin barci, harda 'yar wak'ama take rerawa abinta, sai dai kuma baitin wak'ar yasakani fahimtar bata jin dad'i baceba.
Lalla6awa nayi Na fito, itama Uwargida Na lek'ata.
zaune take ta zuba tagumi tana kallon 'ya'yanta, itakam ban fahimci mike damuntaba.
Fitowa nayi itama nabi bayan Amatallah.
Na isketa tayo brosh tafito daga toilet, harma ta cire kayanta tasaka riga da wando Na barci pink, wandon iyakarsa gwiwa, sai rigarma batada girma sosai mai hannun shimi, itama dai 'yar wak'arta naji tanayi harta bud'e Waldrob d'inta ta d'akko hula tasaka a kanta kafin ta daka tsale ta haye gadonta, duk acikin murnar Uncle baice ta kwana d'akinsaba.....
zakiyi bayani.
Uncle kam tana fita shima ya mik'e, TV ya kashe danji yay labaranma sun fita kansa, dama gawani abinda ake nunawa daya Sosa zuciyarsa akan MATASA, fitar Amatallah d'in saita sakashi a kewa, ya saba zama a irin wannan lokacin da matarsa zaune gefensa suna 'yar hirar rayuwa da soyayyarsu. yabar Amatallah ta tafine danya kula takasa sakewa, shikuma baya buk'atar abinda zai k'untata rayuwarta. amma mi saiyaji bazai iya kwana shikad'ai ba gaskiya, bayan kuma ga mata har uku suna amsa sunan halalinsa, bedroom d'insa yashiga ya canja kayansa zuwa na barci, vest ne da boxer, saiya d'aura jallabiya a sama kawai, yad'an fesa turare kafin yashiga toilet yayo brosh, wayoyinsa ya d'auka ya zuba a aljihu, dan shi baya kashe waya sai dai abisa kuskure ko rashin caji. Yakashe komai Na 6angaren nasa yafito. Sai dai yana fara sakkowa daga benen ana d'auke wuta, "ya salam" yafad'a yana dafe kansa. Ya zaro wayarsa daga aljihu ya kunna fitila sannan ya ida sauka, dolenema ya kunna Generator kodan Sahib dabaya k'aunar zafi, koyaya zafi ya isheshi zaitashi yaytama mutane kuka, yaron yanada masifar jin zafi, gakuma Fateema da ciki kansata zufar babu gaira babu dalili. harya kama hanyar k'ofar fita kuma yadawo baya, 6angaren Fateema yashiga da sallama.
Amsawa tayi tana cire taguminta da saita kanta gudun karya fuskanci halin datake ciki, yak'araso cikin bedroom d'in idonsa akan yaran.
"Wai yanzu kuma su Ummita sun dawo nanne da kwana?".
Kallonsa tayi tace, " a'a, kawai dai kwana biyunnan ne, amma zasu koma d'akinsu ai".
Kansa kawai ya jinjina, ya matsa kusadasu yana lek'a fuskar kowa, ya gyarama Abulkhairi kwanciya daya dawo bakin kadon sosai wajen murje-murjen barci. "Nikam d'azun Shehu yakawo fetur gidannan?".
" kai, anya kuwa, gaskiya banga shehu a gidannanba, sai dai idan kuma bai shigo bane kokuma yakawo ina d'aki, amma ka tambayi Momynsu dai watak'il taga zuwansa".
''Okay, to zaman mikikeyi baki kwantaba?".
Guntun tsaki tayi kafin tace, "wlhy hakanan dai".
Matsowa yayi kusada ita ya taimaka mata ta kwanta, sannan ya tofesu da addu'a, yabisu d'ai'd'ai ya sumbata kafin yamata saida safe.
Yana shirin fita Sahib yafara motsawa yana k'unk'unin kuka, da baya ya dawo ya haskashi, harya fara tara zufa, yanad'an kad'a hannunsa alamar yima kansa firfita. " to sarkin jin zafi, zaka fara ko?" Uncle yay maganar yana sinkuyowa kansa yacire ma6allan rigar barcinsa ya cire masa.
Ita dai Fateema batace komaiba tana daga kwance tana kallonsu harya gama.
Da d'an hanzari yafita yana fad'in "bara dai Na bincika fetur d'in".
6angaren Aneesa yashiga, har yanzu tana falo zaune, sai dai tagamama Siddiqa shiri tuni, tana kan cinyarta dai har yanzu, idonta a lumshe, dan tunda aka d'auke wuta bata motsaba bare ta kunna fitila, sallamarsa tasata amsawa amma bata kalleshiba dukda haska fuskarta dayayi da fitilar wayarsa kafin ya maida Kallonsa ga Saifudden dake kwance a kujera doguwa, kuma maida kallonsa yayi kanta itada Siddiqa. Fuskarsa babu walwala yace, " shehu yakawo fetur d'azune?".
Kamar bazata tankaba, saikuma tace, "ban saniba nima, Dan bai shigo cikiba, amma ka tambayi umman yara mana".
Zai k'ara maganama aka maido wuta, ajiyar zuciya kawai ya sauke yace " Alhmdllh" ya kashe wayar yasaka aljihu, Saifudden ya d'auka yay cikin bedroom d'inta dashi, haryaje k'ofa yajuyo yana kallonsa bayan yata6a d'uwawun Saifudden. "Wai sai yaushe zaki daina sakama yaronnan Pampas ne?".
Baki tad'an tunzuro, " amma dai kasan fitsari yakemin a gado, kaga dole na saka masa pampas".
"Humm amma ai nafad'a miki ki maidashi 6angaren Fateema yana kwana cikin 'yan uwansa, tundasu katifarsu fitsari baya hudawa, tunda bazai yuwu yadinga kwana shi kad'aiba anan".
" ammafa dear kasa......."
Saikuma tayi shiru bata k'arasaba.
Yace, "nasan mi?".
Shiru tayi bata tankaba, amma idonta a kansa.
Shima shigewarsa yayi ya shifid'e Saifudden, yadawo ya d'auka Siddiqa itama, itadai Aneesa kallonsa kawai takeyi, bai fitoba saida yayi musu addu'oi kamar yanda ya saba.
Koda yafito bai kulataba yanufi hanyar ficewa.
Da sauri ta ruk'i hannunsa na dama, cak ya tsaya amma bai juyoba, sai kawai tamatsa ta rungumeshi ta baya tareda sakin wani marayan kuka.
Shiru yayi yana saurarenta dukda kukan NATA na sukar zuciyarsa, sai kawai ya lumshe idanu, kusan mintuna 3 kafin yasa hannu ya janyeta a bayansa, takuma rik'eshi da k'yau yanda bazai guduba.
"Please dear kadaina fushi dani Dan ALLAH na tuba".
Kallonta yayi ya kauda kansa, dukda tabashi tausayi bai tankaba yakuma yunk'urin fita. Sai kawai tazube a gabansa takuma sakin kuka. tamau yakuma tamke fuska, " Aneesa bani hanya na wuce" yay maganar a d'an tsawace.
"Babu inda zanje Muhammad, sai dai mu kwana anan".
Wani murmushi yasaki yana shafa gemunsa, yace "sai dai ke d'in ki kwana anan amma baniba mai amarya, tunda baki shirya fad'amin abinda ya had'aki da khadeeja ba muyita zama ahaka".
Dukda maganar ta soki zuciyarta haka ta danne, tamik'e tana fad'in "shikenan zan sanar maka, saikamin hukunci, amma ina fatan hakan bazai sakaka d'aukar wani sabon fushinba?". A tausashe take maganar, kuma dolene tabaka tausayi.
Kallon agogon falon yayi kafin ya kalleta, " kibari saida safe, yanzukam barci nakeji" ya kai karshen maganar da kama hannunta zuwa bedroom d'in ta, dama tayi shirin barci, dan haka ya taimaka mata ta kwanta, goshinta ya sumbata yafita yana fad'in "ALLAH yabamu alkairi".
Bata tanka mishiba, sai wasu hawaye masu zafi dasuka kwaranyo a kumatunta, tasan babu makawa yau zai angwance abinsa, a fili tace, "ya ALLAH ka sassautamin kishinan dai".
ALLAH saita bani tausayi masu karatu
. Harna amsa da amin Aneesa. Dan zafin kishi bala'ine.
Komai na falonta yakashe sannan yafito babban falo, nanma yakashe abinda zai kashe, fitilar kitchen ya hango a kunne, itama ya k'arasa ya kashe tareda jawo k'ofar, saida ya tabbatar komai dai-dai sannan yanufi 6angaren Amatallah.
Ba barci takeba, tana zaune tsakkiyar gadon tana karatu, harta kwanta aka maido wuta, shine ta tashi kawai tana bincika takardunta na school, Dan watak'il gobe amusu test.
Shigowarsa babu zato sai sallamarsa dataji kusan dab da ita yasakata diriricewa, tafara laluben abundan zata rufe jikinta, saidai babu komai akusa da ita, bargone kuma ta turashi can k'arshen gadon lokacin datayi tsalle.
Shikam kallon k'yawun halittar da ALLAH yamata yasakashi manta gabanma wa yakene, saida tafara k'ok'arin sauka daga gadon Dan d'aukar hijjabi sannan ya dawo hayyacinsa.
Saurin rik'ota yayi ya maidata kan gadon, shima ya zauna gefen yana kallon takardun data baje a gadon, "dama bakiyi barciba" yay maganar murya a sanyaye kuma yana kallonta.
Kasa magana tayi, sai jijjiga masa kai datayi tanata wani takurewa da gyagygyara wuyan rigarta tamkar tamata yawa, alhalin kuma cif take a jikinta tamkar an gwadatama.
Murmushi yayi yana hayewa sosai kan gadon, ya tattare takardun waje d'aya yamaida kan drowan gefen gadon ya ajiye.
Muryarta na d'an rawa tace, "Uncle ina karatun test ne fa".
Hannu yakai yarik'o nata yana wani k'ank'ance idanu, "tunda miji yazo sai'a barshi aii ko, nima wani text d'in zamuyi yanzun aii".
Gabanta ya fad'i, ta tuno maganar Fa'iza, gefe kuma tana mamakin dama haka Uncle yake Wai?...."
Bata kai k'arshen tunanintaba tajita a jikinsa, sosai jikinta yafara rawa, hannu kawai yakai saman bango kusada fuskar gadon ya kashe fitilar d'akin.
Mi cikin Amatallah zaiyi banda k'ara kuuuuuu!!!.
Tamkar ya kwashe da dariya haka yaji, amma saiya dake ya gyara mata kwanciya sosai ajikinsa bayan yazame jallabiyar jikinsa ya zauna dagashi sai vest da boxer.
Kasa cewa uffan Amatallah tayi, saidai jikinta har yanzu rawa yakeyi, bata k'ara tsorataba saida taji babu alamar kaya a jikinsa, kasa daurewa tayi muryarta na zuga na alamar tahowar kuka tace, "please Uncle ALLAH I......
Bai bari takai k'arsheba ya d'ora hannunsa akan le6enta, acikin kunnenta yace, " ya isa haka, ni barci kawai nazo muyi madam pinky....."
'Dan k'ank'ame jikinta tayi saboda maganarsa tasaka tsigar jikinta yin yarrr. luf tayi bata kuma yunk'urin yin maganaba, taji ya janye hannunta daya d'ora saman k'irjinta ya d'ara yatsansa a bakinta.
Shirune ya biyo baya a d'akin, sai k'arar fanka kawai, shi addu'a yakeyi, itakam tunanin da fargabar wannan lamari ga d'unbin mamakin rashin kawaici na namiji sun cika kwalwar kanta, hummm komin matsayin Namiji a wajenka kafin aure, labari yakan koma bayan kazama matarsa, saisu ture Duk wata kunya da karar girmansu a wajenka su nuna maka sunma manta, kujifa Uncle yanzu harda wani cemata madam pinky, saboda komai nata pink har kayan barci kenan, wayyo Uncle zaka kasheni da kunya wlhy........
Cak tunaninta ya tsaya danjin hannunsa indama batayi zatoba da sunan yana shafa mata addu'a, k'ank'ame jikinta tayi waje guda.
Yasaki murmushi mai sauti yana janye hannun daga inda ya d'ora. Koda ya kammala addu'ar sai kawai ya rungumeta da k'yau ya lumshe ido batareda yace da ita uffanba.
Dan danan barci mai dad'i yay gaba dashi, Amatallah kam sai sak'e-sak'e takeyi, hankalinta bai kwantaba saida taji saukar numfashinsa a hankali alamar barci ya d'aukeshi, addu'a tayi tad'an tattaofa batareda ta shafaba ta lumshe idanu, barci yace muje zuwa.........
Asuba tagari Uncle and Ama........
Nace, "humm".
******
Abinda yabani mamaki koda Na lek'a wajen Aneesa saina taddata hankali kwance, tana zaune a falo tanama Siddiqa shirin barci, harda 'yar wak'ama take rerawa abinta, sai dai kuma baitin wak'ar yasakani fahimtar bata jin dad'i baceba.
Lalla6awa nayi Na fito, itama Uwargida Na lek'ata.
zaune take ta zuba tagumi tana kallon 'ya'yanta, itakam ban fahimci mike damuntaba.
Fitowa nayi itama nabi bayan Amatallah.
Na isketa tayo brosh tafito daga toilet, harma ta cire kayanta tasaka riga da wando Na barci pink, wandon iyakarsa gwiwa, sai rigarma batada girma sosai mai hannun shimi, itama dai 'yar wak'arta naji tanayi harta bud'e Waldrob d'inta ta d'akko hula tasaka a kanta kafin ta daka tsale ta haye gadonta, duk acikin murnar Uncle baice ta kwana d'akinsaba.....
zakiyi bayani.
Uncle kam tana fita shima ya mik'e, TV ya kashe danji yay labaranma sun fita kansa, dama gawani abinda ake nunawa daya Sosa zuciyarsa akan MATASA, fitar Amatallah d'in saita sakashi a kewa, ya saba zama a irin wannan lokacin da matarsa zaune gefensa suna 'yar hirar rayuwa da soyayyarsu. yabar Amatallah ta tafine danya kula takasa sakewa, shikuma baya buk'atar abinda zai k'untata rayuwarta. amma mi saiyaji bazai iya kwana shikad'ai ba gaskiya, bayan kuma ga mata har uku suna amsa sunan halalinsa, bedroom d'insa yashiga ya canja kayansa zuwa na barci, vest ne da boxer, saiya d'aura jallabiya a sama kawai, yad'an fesa turare kafin yashiga toilet yayo brosh, wayoyinsa ya d'auka ya zuba a aljihu, dan shi baya kashe waya sai dai abisa kuskure ko rashin caji. Yakashe komai Na 6angaren nasa yafito. Sai dai yana fara sakkowa daga benen ana d'auke wuta, "ya salam" yafad'a yana dafe kansa. Ya zaro wayarsa daga aljihu ya kunna fitila sannan ya ida sauka, dolenema ya kunna Generator kodan Sahib dabaya k'aunar zafi, koyaya zafi ya isheshi zaitashi yaytama mutane kuka, yaron yanada masifar jin zafi, gakuma Fateema da ciki kansata zufar babu gaira babu dalili. harya kama hanyar k'ofar fita kuma yadawo baya, 6angaren Fateema yashiga da sallama.
Amsawa tayi tana cire taguminta da saita kanta gudun karya fuskanci halin datake ciki, yak'araso cikin bedroom d'in idonsa akan yaran.
"Wai yanzu kuma su Ummita sun dawo nanne da kwana?".
Kallonsa tayi tace, " a'a, kawai dai kwana biyunnan ne, amma zasu koma d'akinsu ai".
Kansa kawai ya jinjina, ya matsa kusadasu yana lek'a fuskar kowa, ya gyarama Abulkhairi kwanciya daya dawo bakin kadon sosai wajen murje-murjen barci. "Nikam d'azun Shehu yakawo fetur gidannan?".
" kai, anya kuwa, gaskiya banga shehu a gidannanba, sai dai idan kuma bai shigo bane kokuma yakawo ina d'aki, amma ka tambayi Momynsu dai watak'il taga zuwansa".
''Okay, to zaman mikikeyi baki kwantaba?".
Guntun tsaki tayi kafin tace, "wlhy hakanan dai".
Matsowa yayi kusada ita ya taimaka mata ta kwanta, sannan ya tofesu da addu'a, yabisu d'ai'd'ai ya sumbata kafin yamata saida safe.
Yana shirin fita Sahib yafara motsawa yana k'unk'unin kuka, da baya ya dawo ya haskashi, harya fara tara zufa, yanad'an kad'a hannunsa alamar yima kansa firfita. " to sarkin jin zafi, zaka fara ko?" Uncle yay maganar yana sinkuyowa kansa yacire ma6allan rigar barcinsa ya cire masa.
Ita dai Fateema batace komaiba tana daga kwance tana kallonsu harya gama.
Da d'an hanzari yafita yana fad'in "bara dai Na bincika fetur d'in".
6angaren Aneesa yashiga, har yanzu tana falo zaune, sai dai tagamama Siddiqa shiri tuni, tana kan cinyarta dai har yanzu, idonta a lumshe, dan tunda aka d'auke wuta bata motsaba bare ta kunna fitila, sallamarsa tasata amsawa amma bata kalleshiba dukda haska fuskarta dayayi da fitilar wayarsa kafin ya maida Kallonsa ga Saifudden dake kwance a kujera doguwa, kuma maida kallonsa yayi kanta itada Siddiqa. Fuskarsa babu walwala yace, " shehu yakawo fetur d'azune?".
Kamar bazata tankaba, saikuma tace, "ban saniba nima, Dan bai shigo cikiba, amma ka tambayi umman yara mana".
Zai k'ara maganama aka maido wuta, ajiyar zuciya kawai ya sauke yace " Alhmdllh" ya kashe wayar yasaka aljihu, Saifudden ya d'auka yay cikin bedroom d'inta dashi, haryaje k'ofa yajuyo yana kallonsa bayan yata6a d'uwawun Saifudden. "Wai sai yaushe zaki daina sakama yaronnan Pampas ne?".
Baki tad'an tunzuro, " amma dai kasan fitsari yakemin a gado, kaga dole na saka masa pampas".
"Humm amma ai nafad'a miki ki maidashi 6angaren Fateema yana kwana cikin 'yan uwansa, tundasu katifarsu fitsari baya hudawa, tunda bazai yuwu yadinga kwana shi kad'aiba anan".
" ammafa dear kasa......."
Saikuma tayi shiru bata k'arasaba.
Yace, "nasan mi?".
Shiru tayi bata tankaba, amma idonta a kansa.
Shima shigewarsa yayi ya shifid'e Saifudden, yadawo ya d'auka Siddiqa itama, itadai Aneesa kallonsa kawai takeyi, bai fitoba saida yayi musu addu'oi kamar yanda ya saba.
Koda yafito bai kulataba yanufi hanyar ficewa.
Da sauri ta ruk'i hannunsa na dama, cak ya tsaya amma bai juyoba, sai kawai tamatsa ta rungumeshi ta baya tareda sakin wani marayan kuka.
Shiru yayi yana saurarenta dukda kukan NATA na sukar zuciyarsa, sai kawai ya lumshe idanu, kusan mintuna 3 kafin yasa hannu ya janyeta a bayansa, takuma rik'eshi da k'yau yanda bazai guduba.
"Please dear kadaina fushi dani Dan ALLAH na tuba".
Kallonta yayi ya kauda kansa, dukda tabashi tausayi bai tankaba yakuma yunk'urin fita. Sai kawai tazube a gabansa takuma sakin kuka. tamau yakuma tamke fuska, " Aneesa bani hanya na wuce" yay maganar a d'an tsawace.
"Babu inda zanje Muhammad, sai dai mu kwana anan".
Wani murmushi yasaki yana shafa gemunsa, yace "sai dai ke d'in ki kwana anan amma baniba mai amarya, tunda baki shirya fad'amin abinda ya had'aki da khadeeja ba muyita zama ahaka".
Dukda maganar ta soki zuciyarta haka ta danne, tamik'e tana fad'in "shikenan zan sanar maka, saikamin hukunci, amma ina fatan hakan bazai sakaka d'aukar wani sabon fushinba?". A tausashe take maganar, kuma dolene tabaka tausayi.
Kallon agogon falon yayi kafin ya kalleta, " kibari saida safe, yanzukam barci nakeji" ya kai karshen maganar da kama hannunta zuwa bedroom d'in ta, dama tayi shirin barci, dan haka ya taimaka mata ta kwanta, goshinta ya sumbata yafita yana fad'in "ALLAH yabamu alkairi".
Bata tanka mishiba, sai wasu hawaye masu zafi dasuka kwaranyo a kumatunta, tasan babu makawa yau zai angwance abinsa, a fili tace, "ya ALLAH ka sassautamin kishinan dai".
ALLAH saita bani tausayi masu karatu
. Harna amsa da amin Aneesa. Dan zafin kishi bala'ine.
Komai na falonta yakashe sannan yafito babban falo, nanma yakashe abinda zai kashe, fitilar kitchen ya hango a kunne, itama ya k'arasa ya kashe tareda jawo k'ofar, saida ya tabbatar komai dai-dai sannan yanufi 6angaren Amatallah.
Ba barci takeba, tana zaune tsakkiyar gadon tana karatu, harta kwanta aka maido wuta, shine ta tashi kawai tana bincika takardunta na school, Dan watak'il gobe amusu test.
Shigowarsa babu zato sai sallamarsa dataji kusan dab da ita yasakata diriricewa, tafara laluben abundan zata rufe jikinta, saidai babu komai akusa da ita, bargone kuma ta turashi can k'arshen gadon lokacin datayi tsalle.
Shikam kallon k'yawun halittar da ALLAH yamata yasakashi manta gabanma wa yakene, saida tafara k'ok'arin sauka daga gadon Dan d'aukar hijjabi sannan ya dawo hayyacinsa.
Saurin rik'ota yayi ya maidata kan gadon, shima ya zauna gefen yana kallon takardun data baje a gadon, "dama bakiyi barciba" yay maganar murya a sanyaye kuma yana kallonta.
Kasa magana tayi, sai jijjiga masa kai datayi tanata wani takurewa da gyagygyara wuyan rigarta tamkar tamata yawa, alhalin kuma cif take a jikinta tamkar an gwadatama.
Murmushi yayi yana hayewa sosai kan gadon, ya tattare takardun waje d'aya yamaida kan drowan gefen gadon ya ajiye.
Muryarta na d'an rawa tace, "Uncle ina karatun test ne fa".
Hannu yakai yarik'o nata yana wani k'ank'ance idanu, "tunda miji yazo sai'a barshi aii ko, nima wani text d'in zamuyi yanzun aii".
Gabanta ya fad'i, ta tuno maganar Fa'iza, gefe kuma tana mamakin dama haka Uncle yake Wai?...."
Bata kai k'arshen tunanintaba tajita a jikinsa, sosai jikinta yafara rawa, hannu kawai yakai saman bango kusada fuskar gadon ya kashe fitilar d'akin.
Mi cikin Amatallah zaiyi banda k'ara kuuuuuu!!!.
Tamkar ya kwashe da dariya haka yaji, amma saiya dake ya gyara mata kwanciya sosai ajikinsa bayan yazame jallabiyar jikinsa ya zauna dagashi sai vest da boxer.
Kasa cewa uffan Amatallah tayi, saidai jikinta har yanzu rawa yakeyi, bata k'ara tsorataba saida taji babu alamar kaya a jikinsa, kasa daurewa tayi muryarta na zuga na alamar tahowar kuka tace, "please Uncle ALLAH I......
Bai bari takai k'arsheba ya d'ora hannunsa akan le6enta, acikin kunnenta yace, " ya isa haka, ni barci kawai nazo muyi madam pinky....."
'Dan k'ank'ame jikinta tayi saboda maganarsa tasaka tsigar jikinta yin yarrr. luf tayi bata kuma yunk'urin yin maganaba, taji ya janye hannunta daya d'ora saman k'irjinta ya d'ara yatsansa a bakinta.
Shirune ya biyo baya a d'akin, sai k'arar fanka kawai, shi addu'a yakeyi, itakam tunanin da fargabar wannan lamari ga d'unbin mamakin rashin kawaici na namiji sun cika kwalwar kanta, hummm komin matsayin Namiji a wajenka kafin aure, labari yakan koma bayan kazama matarsa, saisu ture Duk wata kunya da karar girmansu a wajenka su nuna maka sunma manta, kujifa Uncle yanzu harda wani cemata madam pinky, saboda komai nata pink har kayan barci kenan, wayyo Uncle zaka kasheni da kunya wlhy........
Cak tunaninta ya tsaya danjin hannunsa indama batayi zatoba da sunan yana shafa mata addu'a, k'ank'ame jikinta tayi waje guda.
Yasaki murmushi mai sauti yana janye hannun daga inda ya d'ora. Koda ya kammala addu'ar sai kawai ya rungumeta da k'yau ya lumshe ido batareda yace da ita uffanba.
Dan danan barci mai dad'i yay gaba dashi, Amatallah kam sai sak'e-sak'e takeyi, hankalinta bai kwantaba saida taji saukar numfashinsa a hankali alamar barci ya d'aukeshi, addu'a tayi tad'an tattaofa batareda ta shafaba ta lumshe idanu, barci yace muje zuwa.........
Asuba tagari Uncle and Ama........