Sashe 8
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Hankalin Feeryal bai kara tashi ba sai da dare yayi, Aunty Ammah suka sata a gaba suna mata nasiha.
kuka sosai take da gaske dai mafarkin nason zamowa gaskiya.
Aunty ta gaza daurewa itama ta fashe da kuka, ta rungume Feeryal suna kuka kamar wacce mutuwa zata rabasu da d'ayan su.
Ammah ta rika baiwa Aunty baki itama tana share hawaye dan duk wanda ya gansu sai sun bashi tausayi.
Daddy da kansa ya shigo ya kama hannun Feeryal tana tirjewa tana mikawa Aunty hannu.
da kyar ya lallab'a ta tasassauta kukan,
ya dubi goggo Bishira da Ammah ya damka musu ita a hannunsu ya ce
"Ku kaita d'akin ta."
Feeryal takuma fashewa da kuka.
wannan karon sai da Daddy shima ya share guntun kwalla.
goggo Bishira da Ammah suna rike da hannunta har sashin Abdulrahim suka shige da ita gefen ta.
nasiha suka kuma yi mata kana sukayi mata saida safe suka janyo mata kofa.
Feeryal ta fad'a kan lafiyayyen gadon ta ta kuma fashewa da kuka tana kankame pillow.........!
Allah ya bamu aron rai ya nuna mana bayan sallah da rai da lafiya.
Abun da take ganin sa kamar mafarki sai gashi ya zamo gaskiya, yau ta rabu da Ammien ta gata a side d'in Abdulrahim kuma wai a matsayin matarsa.
wani kukan takuma fashewa da shi, tana dad'a kankame jikin pillow gami da kiran sunan Ammie'n ta.
a haka bacci yasami nasar d'aukar ta,
sai dai tayi ta juyi dan sam bata saba bacci da kaya masu nauyi ba,
dole ta mike ta isa jikin wardrobe tashiga bubbud'ewa tana lalumo ta in da Sleeping dress yake.
bata sha wuya wajen nemaba kuwa ta gani sabbi cikin kwalaye da laidodinsu, a jere kamar za'a bud'e kanti.
ta d'au d'aya mai riga vest da wando har kasa.
a sannu ta nufi kofar da take hango shi na glass.
a hankali takai hannunta jikin kofar gilashin da take tunanin nan ne bathroom.
tana kai hannunta jikin gilashin ya zuge, tasa kai ta shige a hankali.
ta tub'e kayan jikinta ta wasa ruwa kana ta saka kayan baccin, ta fito.
a hankali ta kwanta gefen gado ta rakub'e.
takai zamani guda da tunani ire-ire kafin bacci ya sami nasarar d'aukar ta...
Ab'angaren Kuraiba kuwa, ta kasa zaune ta kasa tsaye.
tun da taji an kawo Feeryal hankalin ta yayi mugun tashi.
karfe 12 ta fito ta nufi bedroom d'in sa.
ganin sa kwance yana bacci bata san san da ta saki wani ajiyar zuciya ba, dan tayi zaton yana can gurin ta ko ita Feeryal d'in tazo d'akin nasa suna tare.
ta janyo masa kofar ta juya tana jin dad'i a ranta.
Feeryal ba ita ta farka ba sai asuba.
bayan ta idar da sallah a hankali ta kifa kanta jin gado tana azqar, takai awa guda zaune sai da ta fara gyangyad'i. kafin ta mike a hankali ta kwanta bakin gado batare da ta cire hijab d'in jikinta ba.
Sai wajen karfe 10 da rabi ta farka.
ta shige bayi tayi wanka tafito, ta shirya cikin doguwar rigar atamfa data d'auka cikin sabbin kayan da suke cike tam cikin wardrobe din d'akin.
rigar ya zauna sosai a jikin ta yamata kyau matuka.
turarukan dake gaban mirror ta shafa masu dad'i gami da sanyin kamshi.
daga su bata kara komai ba, abinka da me kyau tamkar ta zauna ta tsara wani rantsastsen kwalliya haka take kyalli.
karfe 11 dai-dai ta shafa cikin ta data fara jin yunwa, wanda rabon ta da tasa wani abu a cikin tun jiya da rana.
ta mike a hankali ta je ta d'au gyale ta yafa a kanta ta nufi kofa, da zumbar tafiya sashin Ammie'nta.
Tana fitowa Baba Rabi na shigowa niki-niki da kulolin abinci, gami da flax's.
tayi saurin isa ta taimaka mata da wasu.
tana fad'in
"Sannu Baba Rabi ina kwana."
"Lafiya lau 'yar nan ya kwanan bakunta?."
batayi magana ba suka karasa saman dinning suka jera kulolin.
Baba Rabi ta d'ago ta dube ta tana fad'in
"Ammie'n ki ta ce na gaida ki ga breakfast d'in ku."
kai tad'an langwab'ar
tayi rau-rau da ido cike da yanayin ta mai kama da shagwab'a kamar a gaban Ammie'n nata take.
Baba Rabi tayi murmushi ta juya tana fad'in
"Nabarki lafiya."
har Baba Rabi takai kofa tana tsaye jiki ba kwari, sai da taga ficewar ta kana
a hankali taja kujera ta zauna.
Kulolin tashiga bud'e wa had'ad'd'un abinci ne kala-kala d'aya daga cikin flax's d'in kuwa Sudan tea ne a ciki.
sai da takai kan abun da tafi bukata wato cake da Ammie'n ta ta shirya mata shi a mazubi na musamman.
tayi serving
tasoma ci da tea d'in da tad'an had'a rabin mug.
tana kammalawa ta mike ta gyara mayafin kanta ta fita, ta nufi sashin Aunty.
Aunty na zaune cike da kewar ta sai ganin ta tayi.
ta mike tsaye tare da rike baki tana binta da kallon mamaki.
itako kai ta langwab'e tare da cuno d'an karamin kyakkyawan bakin ta.
Aunty tayi saurin ruko hannunta tana fad'in
"Ke Feeryal me ya fito dake ke da jiya aka kaiki? maza koma d'akin ki, kar ki sake fitowa sai in shi yace ki fito."
baki takuma turowa cikin yanayin ta gami da shagwab'a ta ce
"Ammie ni dai so nake na ganki, ni dai zan zauna a nan kawai, ni kad'ai babu kowa tsoro nake ji."
Aunty ta d'anyi jim sai kuma ta saki murmushi tana cewa
"In banda abin ki Feeryal nima bakiga ni kad'ai ce a nan side d'ina ba, haka nayi ta rayuwa a lokacin da babu ke bakima zo duniyar ba, da haka zaki saba har ke ma ki haifo 'yar ki, ko 'yanmatan Ammie."
ta karasa maganar da jan kumatun ta.
baki ta kuma cunowa tana make kafad'a.
Aunty ta janyo hannunta
"Zo ki koma d'akin ki anjima Miemie zatazo ta tayaki hira,
basai kin fito ba ma, ke baki san kin girma ba yanzu,
yanzu duk abin da zaki aikata a d'akin ki na alkhairi ninkin lada za'a rubuta miki,
lallai zaki sami lada da yawa amma zamu raba ladan ne ko, ko rowa zakiyi min?."
ta gyad'a kai tana sakin kyakkyawar murmushin ta,
Aunty ta yi murmushi itama.
haka tayi ta lallab'in ta gami da 'yan dabaru, har ta rakata kusa da side d'in ta.
tana tsaye sai da taga shigarta kafin ta juya ta koma nata side d'in...
A hankali take takowa tana wasa da bakin mayafin ta.
kamar ance ta d'ago karaf suka had'a ido da shi yana tsaye cikin garden, rike da mug yayin da d'aya hannunsa ke zure cikin aljuhun sa.
da sauri ta janye idanunta takara sauri,
ta shige ciki.
a hankali yakai mug d'in bakin sa ya kurb'i Sudan tea d'in sa, kana ya soma takowa ya nufi gefen sa.
kuka sosai take da gaske dai mafarkin nason zamowa gaskiya.
Aunty ta gaza daurewa itama ta fashe da kuka, ta rungume Feeryal suna kuka kamar wacce mutuwa zata rabasu da d'ayan su.
Ammah ta rika baiwa Aunty baki itama tana share hawaye dan duk wanda ya gansu sai sun bashi tausayi.
Daddy da kansa ya shigo ya kama hannun Feeryal tana tirjewa tana mikawa Aunty hannu.
da kyar ya lallab'a ta tasassauta kukan,
ya dubi goggo Bishira da Ammah ya damka musu ita a hannunsu ya ce
"Ku kaita d'akin ta."
Feeryal takuma fashewa da kuka.
wannan karon sai da Daddy shima ya share guntun kwalla.
goggo Bishira da Ammah suna rike da hannunta har sashin Abdulrahim suka shige da ita gefen ta.
nasiha suka kuma yi mata kana sukayi mata saida safe suka janyo mata kofa.
Feeryal ta fad'a kan lafiyayyen gadon ta ta kuma fashewa da kuka tana kankame pillow.........!
Allah ya bamu aron rai ya nuna mana bayan sallah da rai da lafiya.
Abun da take ganin sa kamar mafarki sai gashi ya zamo gaskiya, yau ta rabu da Ammien ta gata a side d'in Abdulrahim kuma wai a matsayin matarsa.
wani kukan takuma fashewa da shi, tana dad'a kankame jikin pillow gami da kiran sunan Ammie'n ta.
a haka bacci yasami nasar d'aukar ta,
sai dai tayi ta juyi dan sam bata saba bacci da kaya masu nauyi ba,
dole ta mike ta isa jikin wardrobe tashiga bubbud'ewa tana lalumo ta in da Sleeping dress yake.
bata sha wuya wajen nemaba kuwa ta gani sabbi cikin kwalaye da laidodinsu, a jere kamar za'a bud'e kanti.
ta d'au d'aya mai riga vest da wando har kasa.
a sannu ta nufi kofar da take hango shi na glass.
a hankali takai hannunta jikin kofar gilashin da take tunanin nan ne bathroom.
tana kai hannunta jikin gilashin ya zuge, tasa kai ta shige a hankali.
ta tub'e kayan jikinta ta wasa ruwa kana ta saka kayan baccin, ta fito.
a hankali ta kwanta gefen gado ta rakub'e.
takai zamani guda da tunani ire-ire kafin bacci ya sami nasarar d'aukar ta...
Ab'angaren Kuraiba kuwa, ta kasa zaune ta kasa tsaye.
tun da taji an kawo Feeryal hankalin ta yayi mugun tashi.
karfe 12 ta fito ta nufi bedroom d'in sa.
ganin sa kwance yana bacci bata san san da ta saki wani ajiyar zuciya ba, dan tayi zaton yana can gurin ta ko ita Feeryal d'in tazo d'akin nasa suna tare.
ta janyo masa kofar ta juya tana jin dad'i a ranta.
Feeryal ba ita ta farka ba sai asuba.
bayan ta idar da sallah a hankali ta kifa kanta jin gado tana azqar, takai awa guda zaune sai da ta fara gyangyad'i. kafin ta mike a hankali ta kwanta bakin gado batare da ta cire hijab d'in jikinta ba.
Sai wajen karfe 10 da rabi ta farka.
ta shige bayi tayi wanka tafito, ta shirya cikin doguwar rigar atamfa data d'auka cikin sabbin kayan da suke cike tam cikin wardrobe din d'akin.
rigar ya zauna sosai a jikin ta yamata kyau matuka.
turarukan dake gaban mirror ta shafa masu dad'i gami da sanyin kamshi.
daga su bata kara komai ba, abinka da me kyau tamkar ta zauna ta tsara wani rantsastsen kwalliya haka take kyalli.
karfe 11 dai-dai ta shafa cikin ta data fara jin yunwa, wanda rabon ta da tasa wani abu a cikin tun jiya da rana.
ta mike a hankali ta je ta d'au gyale ta yafa a kanta ta nufi kofa, da zumbar tafiya sashin Ammie'nta.
Tana fitowa Baba Rabi na shigowa niki-niki da kulolin abinci, gami da flax's.
tayi saurin isa ta taimaka mata da wasu.
tana fad'in
"Sannu Baba Rabi ina kwana."
"Lafiya lau 'yar nan ya kwanan bakunta?."
batayi magana ba suka karasa saman dinning suka jera kulolin.
Baba Rabi ta d'ago ta dube ta tana fad'in
"Ammie'n ki ta ce na gaida ki ga breakfast d'in ku."
kai tad'an langwab'ar
tayi rau-rau da ido cike da yanayin ta mai kama da shagwab'a kamar a gaban Ammie'n nata take.
Baba Rabi tayi murmushi ta juya tana fad'in
"Nabarki lafiya."
har Baba Rabi takai kofa tana tsaye jiki ba kwari, sai da taga ficewar ta kana
a hankali taja kujera ta zauna.
Kulolin tashiga bud'e wa had'ad'd'un abinci ne kala-kala d'aya daga cikin flax's d'in kuwa Sudan tea ne a ciki.
sai da takai kan abun da tafi bukata wato cake da Ammie'n ta ta shirya mata shi a mazubi na musamman.
tayi serving
tasoma ci da tea d'in da tad'an had'a rabin mug.
tana kammalawa ta mike ta gyara mayafin kanta ta fita, ta nufi sashin Aunty.
Aunty na zaune cike da kewar ta sai ganin ta tayi.
ta mike tsaye tare da rike baki tana binta da kallon mamaki.
itako kai ta langwab'e tare da cuno d'an karamin kyakkyawan bakin ta.
Aunty tayi saurin ruko hannunta tana fad'in
"Ke Feeryal me ya fito dake ke da jiya aka kaiki? maza koma d'akin ki, kar ki sake fitowa sai in shi yace ki fito."
baki takuma turowa cikin yanayin ta gami da shagwab'a ta ce
"Ammie ni dai so nake na ganki, ni dai zan zauna a nan kawai, ni kad'ai babu kowa tsoro nake ji."
Aunty ta d'anyi jim sai kuma ta saki murmushi tana cewa
"In banda abin ki Feeryal nima bakiga ni kad'ai ce a nan side d'ina ba, haka nayi ta rayuwa a lokacin da babu ke bakima zo duniyar ba, da haka zaki saba har ke ma ki haifo 'yar ki, ko 'yanmatan Ammie."
ta karasa maganar da jan kumatun ta.
baki ta kuma cunowa tana make kafad'a.
Aunty ta janyo hannunta
"Zo ki koma d'akin ki anjima Miemie zatazo ta tayaki hira,
basai kin fito ba ma, ke baki san kin girma ba yanzu,
yanzu duk abin da zaki aikata a d'akin ki na alkhairi ninkin lada za'a rubuta miki,
lallai zaki sami lada da yawa amma zamu raba ladan ne ko, ko rowa zakiyi min?."
ta gyad'a kai tana sakin kyakkyawar murmushin ta,
Aunty ta yi murmushi itama.
haka tayi ta lallab'in ta gami da 'yan dabaru, har ta rakata kusa da side d'in ta.
tana tsaye sai da taga shigarta kafin ta juya ta koma nata side d'in...
A hankali take takowa tana wasa da bakin mayafin ta.
kamar ance ta d'ago karaf suka had'a ido da shi yana tsaye cikin garden, rike da mug yayin da d'aya hannunsa ke zure cikin aljuhun sa.
da sauri ta janye idanunta takara sauri,
ta shige ciki.
a hankali yakai mug d'in bakin sa ya kurb'i Sudan tea d'in sa, kana ya soma takowa ya nufi gefen sa.