← Book details Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 61

Sashe 41

Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gaba d'aya kallon Umma Karima ake kamar TV, zuciyoyi da fuskoki duk sun ciki da d'inbin mamaki mara misaltuwa.
ba'a ankara ba akaga Umma Karima tayi sama, kamar wacce aka janyota da kugiya.
Feeryal tayi baya da sauri dai dai san da Umma Karima ta b'ace a ka daina ganin ta.
da karfi Feeryal ta ce
"Ku matsa za'a sako ruwa kada ya jika ku."
tayi maganar idanunta a sama.
bata rufa baki ba ruwa ya zubo dai dai inda Umma Karima tayi ta zubar da jinin bakinta da take magana tana goga bakin a kasa.
a take kuma ruwan ya shanye kamar komai bai tab'a gun ba.
ido ta rumtse da karfi tana fad'in
"Wayyo suna dukanta."
ji tayi an damke hannunta da sauri ta bud'e idanunta ta waiga gefen da aka rike hannun nata.
suka had'a ido kai ya girgiza mata tare da mata alama da tayi shiru kada ta kuma magana.
fuska ta kwab'e tare da cuno lips d'in ta gaba, ta kuma d'aga kanta sama babu kowa sun b'acewa ganin ta.
baki ta kuma cunowa ta zame hannunta, ta matsa gefe.
shiko ya taka ya wuce side d'in sa.
tuni gurin ya kaure da hayaniya.
'ya'yan Umma Karima sai kuka musamman Nabila, da take jin kamar ta kashe kanta ta huta.
Sule direba ya sud'ad'a yana kokarin gudu security sukayi ram da shi suka soma dukansa.
Daddy ya ce su kyale shi ya d'auki 'yarsa su tafi.
Hajiya da tayi zaman dirshem a kasa ta ce
"Da kata Sule zo ka had'a da sauran duk ku tafi, dan ni ban yarda da sauran yaran ma na Abubakar bane, ashe duk shegu a ka tara a gidan shi yasa duk suka kasa auruwa, tattara su ku tafi Allah ya had'aka da musifa Sule munafuki maciyi amana, tattara shegun duk ku koma kasarku Niger."
Bappa Salihu ya ce
"Aa baza'ayi haka ba Hajiya Hanne, ai bata ce da wata bayan Nabila ba, ita d'in dai ya d'auki 'yarsa su tafi."
Nabila ta kuma fashewa da kuka.
Aunty ta girgiza kai tana share hawayen da suka zubo mata,
ina amfanin bad'i ba rai......!

Nabila mai ikirari da gadara da gidan uba, sai gashi tabar gidan babu tsuntsu babu tarko.
Sule direba yasata gaba cike da d'inbin kunya suka bar gidan,
tana kuka da waigen gidan tana ji tana gani tasa kafa tabar cikin daular data rayu cikinsa take d'agawa da kafafa da nuna ita wata ce,
da nuna gaskanci da kyara wa Feeryal da suke wa kallon ita ba kowa bace,
face tsintacciya mara galihu...

Mommy ta fashe da kuka ta zube bisa goiwawin ta na fad'in
"Hajiya Karima ta cuce ni, ta jima tana d'aurani a hanyar halaka, tana amfani da ni wajen cimma burin ta,
ban tab'a jin cewa wayo take min tana sarata ta kasa ba,
sai bayan data ingizani har na kaiga kashe jikoki na da hannuna."
ta rarrafo gaban Aunty da Feeryal tana cewa
"Hakika na aikata abubuwa masu yawa, wanda a yau nake jin kunyar tuna duk abun da na aikata,
dan girman Allah Hajiya Fatima kiyi hakuri ki yafe min abubuwan dana jima ina aikata miki,
wlh sharrin zuciya ce da zugar Hajiya Karima, ita take angiza ni wajen aikata komai,
ashe zurani take arami tana kokarin afka min kasa a ka,
wlh nayi nadama nayi dana sani, naji kunya matuka dan Allah kiyi hakuri ki yafe min dan nasan na cutar da ke."
Aunty ta girgiza kai tana cewa
"Wlh ni ban tab'a rike d'ayanku a zuciya ba, duk abun da kukayi min a gurin nake wasar da shi,
abu d'aya na kasa mancewa yaran da kika salwantar da su."
Aunty ta share kwalla tana cigaba da fad'in
"Naji mugun zafin rasa yarannan a lokacin da nake murna da farincikin samin su,
nake ji a raina nima yanzu nasamu nawa ta hanyar 'yata Feeryal,
sai dai ina dama ba masu rayuwa bane Allah yasa hakan shine mafi alkhairi, Allah ya yafe mana baki d'aya."

Mommy ta sharb'e hanci tana rarrafowa gaban Feeryal ta had'e hannayen ta bibbiyu tana fad'in
"Bansan ta ya zanyi na roki gafarar ki ba,
abun da na sani dai na cutar da ke, na zalunceki zalunci mafi muni,
idan kinso zaki iya yafe min amma nasan ban cancanci yafiya a gare ki ba,
amma wlh shine Allah nayi nadama da danasani."
Mommy tafashe da kuka mai ban tausayi tana cigaba da fad'in
"Feeryal kiyi hakuri ki yafe min, idan baki yafe min ba nasan rayuwata bazatayi kyau ba."
ta rike kafafunta ta kifa fuskarta saman kafafunta tana wani irin gunjin kuka, da fad'in
"Ki yafe ni, ki yafe ni, ki yafe ni, Feeryal!."
Feeryal tayi saurin sunkuyawa ta dafa kafad'ar ta
tayi matukar jin nauyin ganin babba kamar Mommy a durkushe a gabanta tana niman yafiyan ta.
cikin yanayin ta mai sanyi ta ce
"Mommy ki tashi dan Allah."
"Feeryal bazan tashi ba har sai sanda kika so kika ya fe min."
cewar Mommy tana kuma kifa fuskarta jikin kafarta.
da sauri Feeryal ta ce
"Ni kam na yafe Mommy na yafe."
Mommy ta d'ago tana share hawaye had'i da yin murmushi.
ta ce "Nagode Allah da yasa kika d'auko zuciya irin na uwar da ra raine ki,
badun haka ba da ban san ina zan sa rayuwa ta ba."
ta mike ta zo gaban Daddy ta durkusa.
ta had'e hannu biyu tashiga ni man gafarar Daddy.
"Alhaji dan girma da darajar Allah, kayi hakuri ka yafe min duk abun da nayi maka, tun daga farkon zaman mu har kawo yau,
kayi hakuri ka yafe min dan Allah in sha Allah zan gyara zan zamo yadda kake so."
Daddy ya juya batare da ya ce komai ba ya nufi sashinsa.
Mommy ta share kwalla tana bin bayan sa da kallo.
kana ta rarrafo gaban Bappa Salihu kafin tayi magana, ya d'aga mata hannu ya ce
"Kije ki fara dai-dai ta sakanin ki da mijin ki da kuma d'anki,
wala Allah da yuwuwar na iya yafe miki."
Bappa Salihu shima ya juya yabar gurin.
tazo gurin Hajiya tana fad'in
"Dan Allah Hajiya ki tayani ki ce su yafe min,
wlh na tuba anyi walkiya anga kowa gaskiya ya bayya."
Hajiya ta sharb'e hanci sannan ta ce
"Zasu yafe miki Halima ai tun da aka gano gaskiya zance ya kare,
kije kiyi abun da babanki ya fad'a, je ki sami abokin turawa, sannan ki koma ki sami Abubakar."
Mommy ta juya ta nufi sashin Abdulrahim.
Duk 'yan gidan jikin su ya sanyaya musamman Ameerah da Farida data zo ana saka da lamarin, Sumayya ce ta kirata ta zo cikin gaggawa.
tana tsaye rungume da 'yarta jiki a sanyaye.
Ajmaal sai murmushi yake yana jin komai ya zo karshe,
Mommy'n su ta gane gaskiyar daya dad'e yana son ganar da ita.
Bilkisu Rahma Saddiqa sun kasa dai na kuka, sun rab'e gefe guda sun rasa madafa.
Aunty ta kalle su sanan ta girgiza kai, duniya ke nan me mai da akawu kuku,
yau ba uwar da zasu fake a jikin ta.

A hankali aka rika watsewa kowa yana cike da alhinin lamarin.
Bilkisu da Rahma da Saddiqa suka bi Hajiya sashinta, tamkar marayun da suka rasa uwa da uba.

A parkour'n sa Mommy ta iske shi, ta zube kasa tana niman yafiyar sa.
"Abdulrahim na kasance azzalumar uwa a gare ka, duk da haka bai hanaka yimin biyayya a matsayi na na mahaifiyarka ba,
ka yafe ni d'ana ka yafe ni,
wlh zugan Hajiya Karima ce da biyewa sharrin zuciya,
yakai ni ga aikata maka komai har ya kai ni ga kashe maka yayan ka, jikoki na na kashe da hannu na! kaico na hakika ni Halima nayi asara a rayuwa ta."
Mommy ta fashe da kuka tana rike hannun d'an nata.
ido ya lumshe ya bud'e sannan ya gyara zaman ya ce
"Shike nan Mommy."
kalmar daya furta ke nan a takaice.
Mommy ta dad'a kankame hannun sa tana fad'in
"Nagode nagode Feeryal ma tace ta yafe min."
ta mike ta fita da sauri.

Ta tafi gurin Daddy tayi ta niman yafiyar sa, da kyar ya ce ya yafe mata.
naga nan ta je gurin Bappa Salihu ta shaida masa kowa ya yafe mata, sanna shima ya yafe mata.

Tun daga ranar Ameerah ta kwantar da kai,
ta yada makaman rashin mutuncin ta.
ta dawo bin Miemie ta sami kofar shishigewa Feeryal.
Farida ma yanzu idan tazo gidan sai ta je sashin Aunty.
tayi ta kwantar da kai rashin mutunci an aje shi a gefe.
su Bilkisu kuwa suna nan rab'e a gefen Hajiya, Aunty mace mai dattako haka tarika jan su a jiki, tana sakar musu fuska, suna zuwa sashinta sosai suyi hira, kyauta kuwa sosai take yi musu, musamman take d'aukarsu su tafi shopping.
a kwan a tashi sai ga Aunty ta zame musu ginshiki fiye da uwar da ta haife su,
dan sabon tarbiyya take basu, wacce Umma Karima ta gaza basu.
cikin kankanin lokaci gidan ya dawo normal, irin gidan da ko wani magidanci yake fatar gidansa ta kasan ce.
sosai Mommy take jan Feeryal a jiki, duk da har yanzu Feeryal bata sake da ita ba,
Mommy
tana jin dama ace ta koma auren d'anta, sai dai tabar hakan a ranta dan batasan wazata tinkara da batun ba..

Kamar yadda Abdulrahim ya fad'a idan Zaraddin ya kai uzu sitti zai dawo da shi gida,
hakan ta kasance a ranar yaje ya d'auko sa ya dawo da shi gida.
anyi mamakin ganin su tare,
da ganin yadda Zaraddin ya zamo shiryayye a zahiri, domin kuwa farar jallabiya har kasa ne a jikinsa,
da hula a kansa, hannunsa kuwa rike da carbi, sai sunkuyar da kai kasa yake yana gaida kowa cikin girmamawa, da maganar sa daya koma irin na ustazai.
ko da Daddy ya tambaye sa in da ya samo shi, bai b'oye ba ya ce shi ya d'auke sa ya b'oye sa,
ya bashi horo ya kuma sa arika koyar da shi.
Bappa Salihu da ya sami labari ya kirasa a waya yayi ta sanya masa albarka, yana cewa
"Ko yau iyayan ku suka mutu kai zaka zame musu uba na gari."
Chapter 41 · 0% Book details