Sashe 1
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Da sauri Aunty ta waro ido ta ce
"An d'aura fa kace Daddy!."
"Kwarai kuwa an d'aura yanzu, cikin yardar Allah Fad'imatu,
Bappa Salihu ne ya ce a d'aura yanzu dan wani jinkirin ba alhaki bane, musamman a gab'ar da ake yanzu."
jiki a sanyaye Aunty ta ce
"Daddy ni dai ina fargabar abin da zaije ya dawo."
Daddy ya katseta
"Kiyi fatan alkhairi Allah zai wuce gaba,
yanzu abin da nake so dake je ki kira min Feeryal d'in."
Aunty ta mike jiki ba kwari ta nufi d'akin Feeryal ta tarar da ita tana bacci, ta dawo ta sanar masa ya ce a barta sai ta tashi.
Kaf matasan gidan suka fito daga masallacin, dake kofar gidan jiki a sanyaye.
dan lamarin d'aurin auren ya zo wa kowa a matukar bazata, shi kansa Daddy bai san a take Bappa Salihu zai ce a d'aura ba.
Zaraddin ne yabiyo Dad d'insa da sauri kamar wani zararre yana cewa
"Yanzu kana ji kayi shiru aka d'aura auren yarinyar da nake so, na rantse bazan yadda ba,
wannan munafurci ne kawai ai an sanni ni nake son ta saboda shi yana da kud'i shine za'a bashi ita, to wlh bazan yadda ba sai an juya aurennan yadawo kaina."
Dad ya harareshi ya ce "Shashashan banza matsa kabani guri, wanda baisan abin da yake yi ba, anata kokari a kanku bakwa gani,
ina ruwanka idan an bashi ita,
kar ka sake naji wani magana ka yadda ka b'ata min shiri kagani,
shashasha kawai."
Zaraddin ya tsaya daga hanya, Dad ya shige sashin sa bai fasa surutu ba.
Mom ta ce
"Kai da waye kuma kake fad'a?."
ya ce "Ni da wancan shashashan d'an naki mana, wai dan an d'aura wa Abdulrahim aure da wancan yarinyar da suka so kashe kansu a kanta, shine yake hauka wai sai an maida auren ya dawo kansa,
jimin shashanci fa auren da babu wanda yasani kamar auren munafurci ana idar da salla Bappa Salihu ya miko goro da minti ya ce a d'aura yanzu."
Mom ta rike baki ta ce
"Feeryal d'in aka d'aurawa Abdulrahim aure da ita?."
sai kuma ta shiga tafa hannu tana fad'in
"Tabd'i jam lallai akwai babbar matsala,
yanzu shi Yaya Abubakar d'in har ya lamunce ya d'aurawa d'ansa aure da 'yar da ba'asan asalinta bama,
'yar da aka tsinta cikin ruwa, yarinya mara daraja ya yadda ya amince ya had'ata aure da mutum kamar Abdulrahim,
ai ko shi Zaraddin d'in da akewa kallon mai rawar kai bazan yadda na lamunce a had'a shi aure da ita ba,
kuma Hajiya Halima tana gidan ta zuba ido akayi wannan aure."
"Can musu suje can su karata, ni yanzu hidimar dana sa agabana kad'ai nake kwarara."
Mom ta zauna tana ta jinjina lamarin...
Can bakin masallaci kuwa.
Ajmal yayi kokarin dai-dai nutsuwarsa,
yana ta kokarin yaki da zuciyar sa.
ya iso in da Abdulrahim ke sunkuye gaban Bappa Salihu da ke zaune kan dakalin masallaci,
yana masa magana kasa-kasa.
murmushi Ajmal ya yi yana fad'in
"Congratulations bro."
Faisal da Shamsuddin ma suka karaso gurin suna fad'in
"Muna tayaka murna Ya Abdulrahim."
bai yi magana ba sai fuska daya dad'a murtukewa.
Bappa Salihu ya ce "Shiga ciki Abdulrahim Allah dai yamaka albarka yasa 'ya'yanka suyi maka biyayya fiye da yadda kakeyiwa iyayen ka."
ya mike ya nad'e hannunsa a kirji ya soma takawa zuwa ciki.
Daga masallaci in da aka gama d'aurin auren, Bappa Salihu ya tafi sashin Hajiya.
ya kai mata goro da minti yakuma shaida mata an d'aura auren Abdulrahim da Feeryal, shi yabada umurnin a d'aura nan take bayan an idar da sallar asuba.
Hajiya dake kan kujera ta zamo kasa tayi zaman dirshem, ta kwalalo ido tare da buga kirji ta ce
"Auren ka d'aura masa da yarinyar da rabin ta mutum rabin ta aljana, kasan waye wannan yarinyar kuwa,
to wlh ni dai ban amince ba,
ta in da aka hau tanan za'a sauka yadda kuka d'aura haka zaku kunce, dan kunyi aikin banza ne,
dan billahillazi, abokin turawa bazai zauna da yarinyar nan ba."
Bappa Salihu ya mike yana fad'in
"Idan ke baki aminta ba ni da 'yan'uwa na Jibir da Ali duk mun amince,
kuma mun yanke hukunci akan d'anmu Abubakar da jikan mu Abdulrahim, dan baki fimu karfi da iko a kansu ba."
Bappa Salihu ya juya ya fita.
Hajiya da harbakin ta na kumfa ta ke fad'in
"Zancen banza kai wlh bazata sab'u ba, yadda kuka d'aura haka zaku kunce."
Bappa Salihu na fita sashin Mommy ya tafi.
Mommy ta tarbi mahaifin nata, bayan ta cika shi da kayan karin kumallo ta zauna suka shiga gaisawa, kasancewar daren jiya da ya iso bata samu sun gaisa ba.
Bappa Salihu bai tab'a komai daga cikin abincin ba.
gani bai ci komai ba Mommy ta ce
"Baba ga abinci fa an kawo maka."
ya ce
"Aa bar wannan yanzu haka nasan Abubakar ya kai min abinci can d'aki na, idan naje zanci acan."
Mommy ta d'anyi dariyar yake a kasan ranta kuwa haushi ne tam dan tasan abincin daga gun Aunty zai fito.
dan duk iyayen nasu idan suka zo Daddy ke d'awainiya da su da kansa,
daga sashin Aunty kuma yake fita da abincinsu.
tayi kwafa a kasan ranta ita da take 'yar su wai sai wata ce can za'a rika d'aukar abinci daga gurin ta ana kai musu.
ta wani jijjiga kai tana kuma jan kwafa a kasan ranta
Mommy ta d'an muskuta tare da kwakulo murmushi ta ce
"Baba ko kazo yin wani abu ne, naga baka shigo da wuri ba jiya sai dare,
ko jirgi ne aka rasa sai na dare?."
ya ce
"Tafiyar ce dai da ba'ayi masa shiri ba, shi yasa ban sami jirgi mai tasowa da rana ba,
lokacin da na iso Jos jirgi har ya tashi,
na bari sai gari yawaye kuma ina ganin b'ata lokaci ne, shiyasa nabi jirgin da zai taso da daddare,
dan nazo na aiwatar da abin da ya kamata da wuri."
Mommy tayi murmushi ta ce
"Ai kuwa kasha hanya mutan gidan kowa lafiya."
ya ce "Lafiya lau suke."
ya saka hannu a aljuhu yana cigaba da fad'in
"Yauwa ga goron auren d'anki da aka d'aura d'azu da asuba d'in nan."
wani irin mike wa a haukace Mommy tayi ta buga kirji
"Aure Baba! wai dama abun da ya kawo ka garinnan ke nan? wlh Baba bazai yuwuba yazama dole a wargaza auren nan!."
Mommy tana maganar a haukace tana jin kamar kanta zai bud'e.
Bappa Salihu ya ce
"Ke Halima zauna wani haukar banza ce wannan,kamar wanda aka fad'a miki mutuwar d'an naki,
abun da Allah ya hukunta kin isa kice ba haka ba, shirmen banza kawai."
Mommy ta zauna tana fad'in
"Baba a gaskiya ni ban yadda da wannan auren ba, ni kwata-kwata yarinyar ce bana kaunar ta."
"Au haka ne shine ke kika iya nemo masa mata ya aura, dan mahaifin sa ya bashi zab'in sa, sai ya zamo abin tada hankali,
shi yasa nace a d'aura auren nan take sabo da irin wannan shiriritar taku,
ke zaki zauna masa da matar,
shi Abdulrahim d'in da akayiwa dirar mikiya cikin rayuwar sa, ba'a jira jin ta bakinsa ba, ba'a jira jin ko da wacce yake so ba, aka zab'ar masa bai yi irin wannan haukar ba,
to ki maida hankalin ki baki isa ki hana abin da Allah ya hukunta ba."
Mommy da gaba d'aya kwakwalwarta ya cakud'e ta ce
"Baba wannan abun fa makirci ne kawai, duk shirin Hajiya Fatima ce, so take ta juya shi ta juya ubansa,
ban san me yasa ake son lallai sai ya aure ta ba, in dai auren ake son a kara yi masa a nima masa wata amma ba ita ba."
"Kaji shirmen banza kawai ita mahaifinsa yaso ya aura masa, karki kuskura kice zaki d'agawa mutane hankali kinji nagaya miki,
shirmen banza kawai shi yasa na d'aura auren d'iyanin sabo da gudun irin wannan shirmen,
zaku hana abin da Allah ya hukunta ne."
Bappa Salihu ya mike yana cigaba da fad'a.
Kuraiba ta fad'o parlour Mommy a hargitse tana fad'in
"Mommy wata magana nake jihaka, wai da gaske Abdulrahim aure yayi?
yaushe ne mukayi auren ko shekara bamu rufa ba shine zai kuma aure, wai kuma wannan yarinyar mai kama da aljanun,
Mommy kice min karya ne bama auren ya yi ba bare ace ita yarinyar ce ya aura."
Bappa Salihu ya daka masa tsawa
"Wace irin shashanci ne wannan zaki fad'o guri babu sallama, haukar banza kawai shine me idan ya yi aure matan ubansa nawa ne gasu nan kina ganin su rai uku,
kuma har yanzu yana da ikon karo d'aya bare shi mai mata d'aya,
haukar banza kawai."
Bappa Salihu ya fita yana cigaba da fad'a.
"An d'aura fa kace Daddy!."
"Kwarai kuwa an d'aura yanzu, cikin yardar Allah Fad'imatu,
Bappa Salihu ne ya ce a d'aura yanzu dan wani jinkirin ba alhaki bane, musamman a gab'ar da ake yanzu."
jiki a sanyaye Aunty ta ce
"Daddy ni dai ina fargabar abin da zaije ya dawo."
Daddy ya katseta
"Kiyi fatan alkhairi Allah zai wuce gaba,
yanzu abin da nake so dake je ki kira min Feeryal d'in."
Aunty ta mike jiki ba kwari ta nufi d'akin Feeryal ta tarar da ita tana bacci, ta dawo ta sanar masa ya ce a barta sai ta tashi.
Kaf matasan gidan suka fito daga masallacin, dake kofar gidan jiki a sanyaye.
dan lamarin d'aurin auren ya zo wa kowa a matukar bazata, shi kansa Daddy bai san a take Bappa Salihu zai ce a d'aura ba.
Zaraddin ne yabiyo Dad d'insa da sauri kamar wani zararre yana cewa
"Yanzu kana ji kayi shiru aka d'aura auren yarinyar da nake so, na rantse bazan yadda ba,
wannan munafurci ne kawai ai an sanni ni nake son ta saboda shi yana da kud'i shine za'a bashi ita, to wlh bazan yadda ba sai an juya aurennan yadawo kaina."
Dad ya harareshi ya ce "Shashashan banza matsa kabani guri, wanda baisan abin da yake yi ba, anata kokari a kanku bakwa gani,
ina ruwanka idan an bashi ita,
kar ka sake naji wani magana ka yadda ka b'ata min shiri kagani,
shashasha kawai."
Zaraddin ya tsaya daga hanya, Dad ya shige sashin sa bai fasa surutu ba.
Mom ta ce
"Kai da waye kuma kake fad'a?."
ya ce "Ni da wancan shashashan d'an naki mana, wai dan an d'aura wa Abdulrahim aure da wancan yarinyar da suka so kashe kansu a kanta, shine yake hauka wai sai an maida auren ya dawo kansa,
jimin shashanci fa auren da babu wanda yasani kamar auren munafurci ana idar da salla Bappa Salihu ya miko goro da minti ya ce a d'aura yanzu."
Mom ta rike baki ta ce
"Feeryal d'in aka d'aurawa Abdulrahim aure da ita?."
sai kuma ta shiga tafa hannu tana fad'in
"Tabd'i jam lallai akwai babbar matsala,
yanzu shi Yaya Abubakar d'in har ya lamunce ya d'aurawa d'ansa aure da 'yar da ba'asan asalinta bama,
'yar da aka tsinta cikin ruwa, yarinya mara daraja ya yadda ya amince ya had'ata aure da mutum kamar Abdulrahim,
ai ko shi Zaraddin d'in da akewa kallon mai rawar kai bazan yadda na lamunce a had'a shi aure da ita ba,
kuma Hajiya Halima tana gidan ta zuba ido akayi wannan aure."
"Can musu suje can su karata, ni yanzu hidimar dana sa agabana kad'ai nake kwarara."
Mom ta zauna tana ta jinjina lamarin...
Can bakin masallaci kuwa.
Ajmal yayi kokarin dai-dai nutsuwarsa,
yana ta kokarin yaki da zuciyar sa.
ya iso in da Abdulrahim ke sunkuye gaban Bappa Salihu da ke zaune kan dakalin masallaci,
yana masa magana kasa-kasa.
murmushi Ajmal ya yi yana fad'in
"Congratulations bro."
Faisal da Shamsuddin ma suka karaso gurin suna fad'in
"Muna tayaka murna Ya Abdulrahim."
bai yi magana ba sai fuska daya dad'a murtukewa.
Bappa Salihu ya ce "Shiga ciki Abdulrahim Allah dai yamaka albarka yasa 'ya'yanka suyi maka biyayya fiye da yadda kakeyiwa iyayen ka."
ya mike ya nad'e hannunsa a kirji ya soma takawa zuwa ciki.
Daga masallaci in da aka gama d'aurin auren, Bappa Salihu ya tafi sashin Hajiya.
ya kai mata goro da minti yakuma shaida mata an d'aura auren Abdulrahim da Feeryal, shi yabada umurnin a d'aura nan take bayan an idar da sallar asuba.
Hajiya dake kan kujera ta zamo kasa tayi zaman dirshem, ta kwalalo ido tare da buga kirji ta ce
"Auren ka d'aura masa da yarinyar da rabin ta mutum rabin ta aljana, kasan waye wannan yarinyar kuwa,
to wlh ni dai ban amince ba,
ta in da aka hau tanan za'a sauka yadda kuka d'aura haka zaku kunce, dan kunyi aikin banza ne,
dan billahillazi, abokin turawa bazai zauna da yarinyar nan ba."
Bappa Salihu ya mike yana fad'in
"Idan ke baki aminta ba ni da 'yan'uwa na Jibir da Ali duk mun amince,
kuma mun yanke hukunci akan d'anmu Abubakar da jikan mu Abdulrahim, dan baki fimu karfi da iko a kansu ba."
Bappa Salihu ya juya ya fita.
Hajiya da harbakin ta na kumfa ta ke fad'in
"Zancen banza kai wlh bazata sab'u ba, yadda kuka d'aura haka zaku kunce."
Bappa Salihu na fita sashin Mommy ya tafi.
Mommy ta tarbi mahaifin nata, bayan ta cika shi da kayan karin kumallo ta zauna suka shiga gaisawa, kasancewar daren jiya da ya iso bata samu sun gaisa ba.
Bappa Salihu bai tab'a komai daga cikin abincin ba.
gani bai ci komai ba Mommy ta ce
"Baba ga abinci fa an kawo maka."
ya ce
"Aa bar wannan yanzu haka nasan Abubakar ya kai min abinci can d'aki na, idan naje zanci acan."
Mommy ta d'anyi dariyar yake a kasan ranta kuwa haushi ne tam dan tasan abincin daga gun Aunty zai fito.
dan duk iyayen nasu idan suka zo Daddy ke d'awainiya da su da kansa,
daga sashin Aunty kuma yake fita da abincinsu.
tayi kwafa a kasan ranta ita da take 'yar su wai sai wata ce can za'a rika d'aukar abinci daga gurin ta ana kai musu.
ta wani jijjiga kai tana kuma jan kwafa a kasan ranta
Mommy ta d'an muskuta tare da kwakulo murmushi ta ce
"Baba ko kazo yin wani abu ne, naga baka shigo da wuri ba jiya sai dare,
ko jirgi ne aka rasa sai na dare?."
ya ce
"Tafiyar ce dai da ba'ayi masa shiri ba, shi yasa ban sami jirgi mai tasowa da rana ba,
lokacin da na iso Jos jirgi har ya tashi,
na bari sai gari yawaye kuma ina ganin b'ata lokaci ne, shiyasa nabi jirgin da zai taso da daddare,
dan nazo na aiwatar da abin da ya kamata da wuri."
Mommy tayi murmushi ta ce
"Ai kuwa kasha hanya mutan gidan kowa lafiya."
ya ce "Lafiya lau suke."
ya saka hannu a aljuhu yana cigaba da fad'in
"Yauwa ga goron auren d'anki da aka d'aura d'azu da asuba d'in nan."
wani irin mike wa a haukace Mommy tayi ta buga kirji
"Aure Baba! wai dama abun da ya kawo ka garinnan ke nan? wlh Baba bazai yuwuba yazama dole a wargaza auren nan!."
Mommy tana maganar a haukace tana jin kamar kanta zai bud'e.
Bappa Salihu ya ce
"Ke Halima zauna wani haukar banza ce wannan,kamar wanda aka fad'a miki mutuwar d'an naki,
abun da Allah ya hukunta kin isa kice ba haka ba, shirmen banza kawai."
Mommy ta zauna tana fad'in
"Baba a gaskiya ni ban yadda da wannan auren ba, ni kwata-kwata yarinyar ce bana kaunar ta."
"Au haka ne shine ke kika iya nemo masa mata ya aura, dan mahaifin sa ya bashi zab'in sa, sai ya zamo abin tada hankali,
shi yasa nace a d'aura auren nan take sabo da irin wannan shiriritar taku,
ke zaki zauna masa da matar,
shi Abdulrahim d'in da akayiwa dirar mikiya cikin rayuwar sa, ba'a jira jin ta bakinsa ba, ba'a jira jin ko da wacce yake so ba, aka zab'ar masa bai yi irin wannan haukar ba,
to ki maida hankalin ki baki isa ki hana abin da Allah ya hukunta ba."
Mommy da gaba d'aya kwakwalwarta ya cakud'e ta ce
"Baba wannan abun fa makirci ne kawai, duk shirin Hajiya Fatima ce, so take ta juya shi ta juya ubansa,
ban san me yasa ake son lallai sai ya aure ta ba, in dai auren ake son a kara yi masa a nima masa wata amma ba ita ba."
"Kaji shirmen banza kawai ita mahaifinsa yaso ya aura masa, karki kuskura kice zaki d'agawa mutane hankali kinji nagaya miki,
shirmen banza kawai shi yasa na d'aura auren d'iyanin sabo da gudun irin wannan shirmen,
zaku hana abin da Allah ya hukunta ne."
Bappa Salihu ya mike yana cigaba da fad'a.
Kuraiba ta fad'o parlour Mommy a hargitse tana fad'in
"Mommy wata magana nake jihaka, wai da gaske Abdulrahim aure yayi?
yaushe ne mukayi auren ko shekara bamu rufa ba shine zai kuma aure, wai kuma wannan yarinyar mai kama da aljanun,
Mommy kice min karya ne bama auren ya yi ba bare ace ita yarinyar ce ya aura."
Bappa Salihu ya daka masa tsawa
"Wace irin shashanci ne wannan zaki fad'o guri babu sallama, haukar banza kawai shine me idan ya yi aure matan ubansa nawa ne gasu nan kina ganin su rai uku,
kuma har yanzu yana da ikon karo d'aya bare shi mai mata d'aya,
haukar banza kawai."
Bappa Salihu ya fita yana cigaba da fad'a.