Sashe 24
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ko da ya sanarwa Mom abun da ke faruwa, Mom tayi tsalle ta dire ta ce
wlh ba dai a had'a Zaraddin da 'yar da aka zubar wa ciki ba.
labari ya isarwa Umma Karima ta niko garin ta tayiyo sashin Mom.
yau anga Mom da Umma Karima a rana dan kuwa fad'a sukayi har da fad'e-fad'e da tone-tone da yiwa juna gori.
Hajiya kuwa ta ce in zasu kashe kansu Zaraddin na dawowa za'a d'aura mishi aure Saddiqa.
Tun da Feeryal ta dawo Aunty ke turo musu da abinci, wajen satin ta guda kenan da dawowa.
bata sashi a idanunta ba, tun a ranar da ta dawo ya shigo ya yi mata allura.
tana daga cikin bedroom wani sa'in zata jiyo motsin sa ya shigo d'ibar abinci da Sudan tea d'in sa.
hakan kuwa ya mata dad'i har ta d'an saki jikinta, kullum tana tare da kawayen ta Chuchu da Chulu.
Miemie ma tana shigowa jifa-jifa.
Feeryal na d'aki tajiyo muryar Miemie da gudu ta fito ta rungume ta tana fad'in
"Oyoyo Miemie shine ina jiya baki zo ba."
ta janye tana tura baki.
Miemie ta zauna kan kujera tana harar Feeryal da fad'in
"Ko yaushe zaki fahimci ke ma mata ce oho,
gata can wancan matar tasa naganta tafito yi masa rakiya zai fita, sai wani mannuwa da shi take, ke kuma gaki nan sai dai ki shiga ki kulle kanki a d'aki,
bazaki tsaya ki kula da mijin ki kinuna masa soyayya ba, kin fita komai da komai kin tsaya wasa, sai kin zamo 'yar kallo ai."
baki Feeryal ta tab'e ta zauna kan hanun kujera ta ce
"To ni na ce miki ina son yayan ku ne bare ma ya dame ni, kinga ita da take son sa ai ta damu da shi."
"Ai wlh kinyi asara Feeryal, ke har zakice bakya son Ya Abdulrahim ai Ya Abdulrahim abun so ne,
in ni ce na sami miji kamar Ya Abdurrahim na rantse rigimar da zanyi ma bazai fad'u ba, itama da take kinibibin ai dan tasan wani irin miji take aure,
Murad d'ina ma kenan da bai kai ko kwatan Ya Abdurrahim ba nake tattalashi bare kuma had'ad'd'en miji irin mijin ki,
in nice da miji kamar Ya Abdurrahim na rantse za'a sha kallo."
Feeryal dai baki tab'e tana cewa
"Ni Miemie ba wannan ba so nake kirakani gyaran gashi gobe."
Miemie ta waro ido ta ce
"Wa ni rufa min asiri kisa mijin ki ya kai ki, in kuma baki san yadda zakiyi ki tarairaye shi ya kai ki ba sai kiyi ta zama."
baki Feeryal ta rike ta ce
"Shine zai kai ni?."
"Ke ai bansan yaushe zaki shigo birni ba, Allah ya ganar min da ke."
dariya Feeryal tayi ta ce
"Da a kauye nake?."
"Kusan hakan ai."
cewar Miemie tana hararar ta, ta mike tana fad'in
"Ni na tafi ma, bazan sake zuwa ba idan baki gyara kinsan ke matar Dr AA FIYA bace."
ita dai da murmushi ta bita...
Tun da aka maida Feeryal d'akin ta Umma Karima bata zauna ba, tana ta kai kawo a gurin bokanta, har yau da Feeryal ta cika watanni biyu da dawowa.
hakan kuwa yayi dai-dai da lokacin tafiya umura,
masu niyya duk an tafi ciki kuwa harda Daddy.
bayan tafiyar Daddy da kwana biyu,
Umma Karima tayi sammakon tafiya gurin bokan ta.
koda ta dawo sashin Mommy ta zarce.
ganin yadda ta fad'o parlour'n Mommy ta mike zumbur tana fad'in
"Yaya dai Hajiya Karima lafiya?."
kirji ta buga ta ce
"Ina ko lafiya gurin wani malami na fito yanzun nan, yagaya min wani magana mai tada hankali, wlh Hajiya Halima idan baki farka daga nannauyar baccin nan da kike ba, ana daf da shafe ki ke da d'an ki, ya ce kwana biyu ya rage wa d'anki a gama da shi har abada, san nan a waiwayo kanki, ni dai na isar da sako na, zab'i ya rage naki, idan kin so ki barsu su ga bayan shi sannan su juyo kanki, kwana biyu ya rage muku."
Mommy ta ce
"Tabd'i jam! Hajiya Fatima kinyi kad'an yanzu zan nuna miki ni na haifi Abdulrahim."
ta juya fuuu sai sashin Abdulrahim, kai tsaye gefen Feeryal tawuce tun kan ta karaso ciki ta ke fad'in
"Ina kike fito nan aljanar ruwa, aje a kare rayuwa a in da aka fito,
d'ana yafi karfin ki narantse da Allah yau sai kin bar sashin nan, yau zama da d'ana ya kare miki."
Mommy ta karaso ta bubbuga kofar bedroom d'in ta da karfi tana fad'in
"Fito munafuka yau karshen makircin ku ya zo, sai dai kibi wani sarkin ba dai d'anaba wlh."
Feeryal jiki na rawa ta fito.
Mommy ta bita da kallon banza ta ce
"Tattara inaki-inaki yau bazaki sake kwanan sashin nan ba, munafukar Allah ta'ala yau kulle-kullen ku ya kare yau zakibar sashin nan."
Abdulrahim da ke kokarin shigowa gefen nata cikin shirin tafiya asibiti, yajiyo muryar Mommy yana karasowa Mommy ta juyo kansa
"Yauwa dama daga nan gurin ka zanyi, na rantse maka da Allah yau yarinyar nan bazata kara kwana sashin nan ba sai ka saketa."
Mommy ta gyara tsayuwar ta da kyau sannan ta ce
"Abdulrahim!."
ta kira sunan sa cikin kakkausar murya.
ya d'ago ya kalleta, ta ce
"Yanzu yanzun nan umurni nake baka bana so ka kara minti biyu ka rubuta mata takardan saki yanzu ka bata!
Abdulrahim na ce ka saketa ko na tsine maka!!."."
kasa yayi da kansa yana damke side bag d'in system nashi dake sakale a bayan sa gefen kafad'ar sa.
rumtse idanunsa yayi da karfi jin kalamar Mommy na karshe yana shirin tarwasa kwakwalwarsa.
"Zaka saketa ne ko sai na sine maka!."
Mommy ta kuma jifansa da kalmar.
da karfi ya bud'e idanunsa da suka rine sukayi jajir nan take.
jakar ya sauke daga bayan sa jininsa na wani irin tafarfasa,
jijiyoyin kansa zuwa na hanayensa suka mike sukayi rad'a-rad'a.
ya bud'e jakar ya ciro takarda da biro hannunsa na kakkarwa ya d'aura biron kan takardan ya rubuta ya d'ago, yayi taku biyu yazo gaban Feeryal dake tsaye ta toshe bakinta da tafin hannunta,
jikin ta na kyarma hawaye na zuba a idon ta,
lamarin ya bala'in tsorata ta.
jajayen idanunsa ya zuba mata tare da mika mata takardan.
ta ciro hannunta dake toshe da bakin ta ta karb'a.
da sauri ya juya yana gyara rukon jakansa ya fice daga parlour'n.
Mommy ta ce "Tom kama hanya kiyi gaba bake ba d'ana yanzu, mayya aljanar banza, burinku bazai cika ba."
Mommy ta sata gaba ta kad'ata tayi sashin Aunty.......!
Aunty dake zaune a parlour ta mike zumbur ta taro Feeryal da ta shigo da gudu tana waigen bayan ta.
hankali tashe Aunty take fad'in
"Ke Feeryal mene ne kina lafiyar ki kuwa?."
rirrike Aunty tayi gam tana fad'in
"Ammie Mommy ce."
sai kuma ta sake ta tana kuma juyawa ta kalli kofa, ganin bata biyo ta nan ba ta sauke numfashi.
Aunty tace
"Mommy kuma Hajiya Halima ce ta biyo ki to a dalilin me?."
ta kardan ta mika mata ta ce
"Ammie ya sake ni ita ta ce Sahab ya sake ni."
wani irin girgiza Aunty tayi da jin abun da Feeryal d'in ke fad'a, hannu na rawa ta karb'i takardan tana cewa
"Innalillahi wa innailaihirraji'un saki kuma!."
Feeryal ta gyad'a kai.
Aunty gaba d'aya ta rud'e takasa ko da iya bud'e takardan sai rikeshi da tayi gam cikin hannunta hannun na rawa.
sai ambaton sunan Allah take.
Feeryal ko wucewa cikin bedroom d'in ta na side d'in tayi, tana mamakin ganin yadda Aunty ta rud'e gaba d'aya ita fa dama ba sakin bane ya razanata,
ganin yadda Mommy take masifa ce ya razana ta tana tsoron kada ta bigeta.
ta shige d'aki tayi kwanciyar ta hankali kwance.
Kan kace me gidan ya d'auki zancen sakin Feeryal.
Umma karima tayi tsalle tayi murna tashigo sashin Mommy da farincikin ta tana fad'in
"Yau kin nunawa Hajiya Fatima iyakar ta, yau kinyi abun da ya dace, har yaushe dama zaki cigaba da zuba ido d'anki ya salwanta, gara da kika nuna mata ke kika haifi Abdulrahim kuma kina da ikon sashi duk abun da kika so da hanashi,
an yadda kwallon mangwaro an huta da kuda, sai susan in da dare ya yi musu,
ana ji ana gani a zalinci yaro a had'a shi da aljanar ruwa masu tsafe-tsafe haba dan Allah."
Mommy ta ce "Ai yanzu kam ya kare har naji hankali na ya kwanta, kai Hajiya Karima nagode miki, wlh badun taimako da sani a hanya da kike ba da ban san ya zan yi ba, yan zu badun kin je kin jiyo wannan labarin ba, da sai dai aji mutuwarsa ace haka Allah ya hukunta, daga nan nima na bakwanci lahira."
Umma karima tayi wani dariyar makirci tana cewa
"Kai haba Hajiya Halima ai babu godiya sakanin mu, ni masoyiyar ki ce ta hakika shekara nawa muna tare mun zamo abu guda, bazan so ganin abun da zai cutar dake ko yayan mu ba, shi yasa tun farko banso had'ata aure da nagartaccen yaro irin Abdulrahim ba."
"Yanzu kam ai zance ya kare suje can su karaci tsiyar su, badai da jinina ba wlh."
cewar Mommy tana buga cinya..
Umma karima ta mike tana fad'in
"Ah to ai gara da kika ankare tun kafin lokaci ya kure miki, ni bari na je dan dole na kaiwa malamin nan labari, nayi masa tukuici na musamman,
dan ya taimake mu ya ankarar da mu tun kafin lokaci ya kure."
Mommy ta ce
"D'an jirani ina zuwa."
ta shige d'aki ta fito da d'aurin kud'i 'yan dubu-dubu da suka kai guda d'ari ta damka mata ta ce
"Ga wannan ki basa kiyi masa godiya dan Allah."
Umma karima ta karb'a tana cewa "Ai ni ma ko dole na kara masa bari naje yanzu."
wlh ba dai a had'a Zaraddin da 'yar da aka zubar wa ciki ba.
labari ya isarwa Umma Karima ta niko garin ta tayiyo sashin Mom.
yau anga Mom da Umma Karima a rana dan kuwa fad'a sukayi har da fad'e-fad'e da tone-tone da yiwa juna gori.
Hajiya kuwa ta ce in zasu kashe kansu Zaraddin na dawowa za'a d'aura mishi aure Saddiqa.
Tun da Feeryal ta dawo Aunty ke turo musu da abinci, wajen satin ta guda kenan da dawowa.
bata sashi a idanunta ba, tun a ranar da ta dawo ya shigo ya yi mata allura.
tana daga cikin bedroom wani sa'in zata jiyo motsin sa ya shigo d'ibar abinci da Sudan tea d'in sa.
hakan kuwa ya mata dad'i har ta d'an saki jikinta, kullum tana tare da kawayen ta Chuchu da Chulu.
Miemie ma tana shigowa jifa-jifa.
Feeryal na d'aki tajiyo muryar Miemie da gudu ta fito ta rungume ta tana fad'in
"Oyoyo Miemie shine ina jiya baki zo ba."
ta janye tana tura baki.
Miemie ta zauna kan kujera tana harar Feeryal da fad'in
"Ko yaushe zaki fahimci ke ma mata ce oho,
gata can wancan matar tasa naganta tafito yi masa rakiya zai fita, sai wani mannuwa da shi take, ke kuma gaki nan sai dai ki shiga ki kulle kanki a d'aki,
bazaki tsaya ki kula da mijin ki kinuna masa soyayya ba, kin fita komai da komai kin tsaya wasa, sai kin zamo 'yar kallo ai."
baki Feeryal ta tab'e ta zauna kan hanun kujera ta ce
"To ni na ce miki ina son yayan ku ne bare ma ya dame ni, kinga ita da take son sa ai ta damu da shi."
"Ai wlh kinyi asara Feeryal, ke har zakice bakya son Ya Abdulrahim ai Ya Abdulrahim abun so ne,
in ni ce na sami miji kamar Ya Abdurrahim na rantse rigimar da zanyi ma bazai fad'u ba, itama da take kinibibin ai dan tasan wani irin miji take aure,
Murad d'ina ma kenan da bai kai ko kwatan Ya Abdurrahim ba nake tattalashi bare kuma had'ad'd'en miji irin mijin ki,
in nice da miji kamar Ya Abdurrahim na rantse za'a sha kallo."
Feeryal dai baki tab'e tana cewa
"Ni Miemie ba wannan ba so nake kirakani gyaran gashi gobe."
Miemie ta waro ido ta ce
"Wa ni rufa min asiri kisa mijin ki ya kai ki, in kuma baki san yadda zakiyi ki tarairaye shi ya kai ki ba sai kiyi ta zama."
baki Feeryal ta rike ta ce
"Shine zai kai ni?."
"Ke ai bansan yaushe zaki shigo birni ba, Allah ya ganar min da ke."
dariya Feeryal tayi ta ce
"Da a kauye nake?."
"Kusan hakan ai."
cewar Miemie tana hararar ta, ta mike tana fad'in
"Ni na tafi ma, bazan sake zuwa ba idan baki gyara kinsan ke matar Dr AA FIYA bace."
ita dai da murmushi ta bita...
Tun da aka maida Feeryal d'akin ta Umma Karima bata zauna ba, tana ta kai kawo a gurin bokanta, har yau da Feeryal ta cika watanni biyu da dawowa.
hakan kuwa yayi dai-dai da lokacin tafiya umura,
masu niyya duk an tafi ciki kuwa harda Daddy.
bayan tafiyar Daddy da kwana biyu,
Umma Karima tayi sammakon tafiya gurin bokan ta.
koda ta dawo sashin Mommy ta zarce.
ganin yadda ta fad'o parlour'n Mommy ta mike zumbur tana fad'in
"Yaya dai Hajiya Karima lafiya?."
kirji ta buga ta ce
"Ina ko lafiya gurin wani malami na fito yanzun nan, yagaya min wani magana mai tada hankali, wlh Hajiya Halima idan baki farka daga nannauyar baccin nan da kike ba, ana daf da shafe ki ke da d'an ki, ya ce kwana biyu ya rage wa d'anki a gama da shi har abada, san nan a waiwayo kanki, ni dai na isar da sako na, zab'i ya rage naki, idan kin so ki barsu su ga bayan shi sannan su juyo kanki, kwana biyu ya rage muku."
Mommy ta ce
"Tabd'i jam! Hajiya Fatima kinyi kad'an yanzu zan nuna miki ni na haifi Abdulrahim."
ta juya fuuu sai sashin Abdulrahim, kai tsaye gefen Feeryal tawuce tun kan ta karaso ciki ta ke fad'in
"Ina kike fito nan aljanar ruwa, aje a kare rayuwa a in da aka fito,
d'ana yafi karfin ki narantse da Allah yau sai kin bar sashin nan, yau zama da d'ana ya kare miki."
Mommy ta karaso ta bubbuga kofar bedroom d'in ta da karfi tana fad'in
"Fito munafuka yau karshen makircin ku ya zo, sai dai kibi wani sarkin ba dai d'anaba wlh."
Feeryal jiki na rawa ta fito.
Mommy ta bita da kallon banza ta ce
"Tattara inaki-inaki yau bazaki sake kwanan sashin nan ba, munafukar Allah ta'ala yau kulle-kullen ku ya kare yau zakibar sashin nan."
Abdulrahim da ke kokarin shigowa gefen nata cikin shirin tafiya asibiti, yajiyo muryar Mommy yana karasowa Mommy ta juyo kansa
"Yauwa dama daga nan gurin ka zanyi, na rantse maka da Allah yau yarinyar nan bazata kara kwana sashin nan ba sai ka saketa."
Mommy ta gyara tsayuwar ta da kyau sannan ta ce
"Abdulrahim!."
ta kira sunan sa cikin kakkausar murya.
ya d'ago ya kalleta, ta ce
"Yanzu yanzun nan umurni nake baka bana so ka kara minti biyu ka rubuta mata takardan saki yanzu ka bata!
Abdulrahim na ce ka saketa ko na tsine maka!!."."
kasa yayi da kansa yana damke side bag d'in system nashi dake sakale a bayan sa gefen kafad'ar sa.
rumtse idanunsa yayi da karfi jin kalamar Mommy na karshe yana shirin tarwasa kwakwalwarsa.
"Zaka saketa ne ko sai na sine maka!."
Mommy ta kuma jifansa da kalmar.
da karfi ya bud'e idanunsa da suka rine sukayi jajir nan take.
jakar ya sauke daga bayan sa jininsa na wani irin tafarfasa,
jijiyoyin kansa zuwa na hanayensa suka mike sukayi rad'a-rad'a.
ya bud'e jakar ya ciro takarda da biro hannunsa na kakkarwa ya d'aura biron kan takardan ya rubuta ya d'ago, yayi taku biyu yazo gaban Feeryal dake tsaye ta toshe bakinta da tafin hannunta,
jikin ta na kyarma hawaye na zuba a idon ta,
lamarin ya bala'in tsorata ta.
jajayen idanunsa ya zuba mata tare da mika mata takardan.
ta ciro hannunta dake toshe da bakin ta ta karb'a.
da sauri ya juya yana gyara rukon jakansa ya fice daga parlour'n.
Mommy ta ce "Tom kama hanya kiyi gaba bake ba d'ana yanzu, mayya aljanar banza, burinku bazai cika ba."
Mommy ta sata gaba ta kad'ata tayi sashin Aunty.......!
Aunty dake zaune a parlour ta mike zumbur ta taro Feeryal da ta shigo da gudu tana waigen bayan ta.
hankali tashe Aunty take fad'in
"Ke Feeryal mene ne kina lafiyar ki kuwa?."
rirrike Aunty tayi gam tana fad'in
"Ammie Mommy ce."
sai kuma ta sake ta tana kuma juyawa ta kalli kofa, ganin bata biyo ta nan ba ta sauke numfashi.
Aunty tace
"Mommy kuma Hajiya Halima ce ta biyo ki to a dalilin me?."
ta kardan ta mika mata ta ce
"Ammie ya sake ni ita ta ce Sahab ya sake ni."
wani irin girgiza Aunty tayi da jin abun da Feeryal d'in ke fad'a, hannu na rawa ta karb'i takardan tana cewa
"Innalillahi wa innailaihirraji'un saki kuma!."
Feeryal ta gyad'a kai.
Aunty gaba d'aya ta rud'e takasa ko da iya bud'e takardan sai rikeshi da tayi gam cikin hannunta hannun na rawa.
sai ambaton sunan Allah take.
Feeryal ko wucewa cikin bedroom d'in ta na side d'in tayi, tana mamakin ganin yadda Aunty ta rud'e gaba d'aya ita fa dama ba sakin bane ya razanata,
ganin yadda Mommy take masifa ce ya razana ta tana tsoron kada ta bigeta.
ta shige d'aki tayi kwanciyar ta hankali kwance.
Kan kace me gidan ya d'auki zancen sakin Feeryal.
Umma karima tayi tsalle tayi murna tashigo sashin Mommy da farincikin ta tana fad'in
"Yau kin nunawa Hajiya Fatima iyakar ta, yau kinyi abun da ya dace, har yaushe dama zaki cigaba da zuba ido d'anki ya salwanta, gara da kika nuna mata ke kika haifi Abdulrahim kuma kina da ikon sashi duk abun da kika so da hanashi,
an yadda kwallon mangwaro an huta da kuda, sai susan in da dare ya yi musu,
ana ji ana gani a zalinci yaro a had'a shi da aljanar ruwa masu tsafe-tsafe haba dan Allah."
Mommy ta ce "Ai yanzu kam ya kare har naji hankali na ya kwanta, kai Hajiya Karima nagode miki, wlh badun taimako da sani a hanya da kike ba da ban san ya zan yi ba, yan zu badun kin je kin jiyo wannan labarin ba, da sai dai aji mutuwarsa ace haka Allah ya hukunta, daga nan nima na bakwanci lahira."
Umma karima tayi wani dariyar makirci tana cewa
"Kai haba Hajiya Halima ai babu godiya sakanin mu, ni masoyiyar ki ce ta hakika shekara nawa muna tare mun zamo abu guda, bazan so ganin abun da zai cutar dake ko yayan mu ba, shi yasa tun farko banso had'ata aure da nagartaccen yaro irin Abdulrahim ba."
"Yanzu kam ai zance ya kare suje can su karaci tsiyar su, badai da jinina ba wlh."
cewar Mommy tana buga cinya..
Umma karima ta mike tana fad'in
"Ah to ai gara da kika ankare tun kafin lokaci ya kure miki, ni bari na je dan dole na kaiwa malamin nan labari, nayi masa tukuici na musamman,
dan ya taimake mu ya ankarar da mu tun kafin lokaci ya kure."
Mommy ta ce
"D'an jirani ina zuwa."
ta shige d'aki ta fito da d'aurin kud'i 'yan dubu-dubu da suka kai guda d'ari ta damka mata ta ce
"Ga wannan ki basa kiyi masa godiya dan Allah."
Umma karima ta karb'a tana cewa "Ai ni ma ko dole na kara masa bari naje yanzu."