Sashe 43
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Me ya kawo ka?."
Major Sadam ya ce
"Gurin ta nazo."
gimtse fuska ya kuma yana cewa
"Kar ka kara zuwa gurin ta, idan bakaji ba kuma zan d'au mataki a kan ka."
Major Sadam ya ce
"Akan wani dalili zaka hanani zuwa gurin ta, a da take matar ka yanzu kuma ta mai rabo ce,
ka shiga sawun manema mu fafata wanda Allah ya bashi sa'a ya aureta,
babu dalilin da zai ka ka hanani zuwa inda take, dan ni na fara sonta, kuma har gobe bazan daina son ta ba, kuma sai na aure ta."
wani irin shaka yayi wa kwalar Major Sadam cikin fusatacciyar murya ya ce
"Zan iya kashe ka idan ka kara cewa zaka aureta,
sabo da ita d'in matata ce!."
Major Sadam shima ya shake kwalar sa.
da sauri
Inspector Nasir ya shiga kokawar rabasu yana fad'in
"Haba ku kuwa meye haka sai kace wasu kananun yara,
Major sake shi tun da ya ce matar sa ce,
zamu so sanin dalilin sa na fad'in haka."
"Karya ne so yake na hakura na bar masa ita, a da take matarsa ba yanzu ba, ni zan auri Feeryal ni zan aure ta yanzu, na bata kulawar da ya kasa iya bata, cikin wata biyu ya mai da ita karamar bazawa."
ran Abdulrahim ya matur b'aci yanayin da yake shiga idan ransa ya b'aci suka soma bayyana.
damasun sa suna bud'awa yayin da jijiyo yin hannunsa suka mike rad'a-rad'a, zufa yana sassafuwa ta cikin sumar kansa.
wani irin had'a Sadam ya yi da jikin motar da suka zo cikin sa, ya shake wuyansa, idanunsa suka firfito, tamkar zasu zazzago kasa.
Major Sadam ya shiga kokarin kwatar kansa, Inspector Nasir yayi-yayi ya iya b'anb'are hannunsa a wuyan Major Sadam ya kasa.
da karfi ya shiga kiran security ganin numfashin abokin nasa yana kokarin barin jikin sa.
Daddy da ya fito daga side d'in sa zai tafi masallaci ya yi saurin isa inda suke yana fad'in
"Kai Abdulrahim wani irin shashanci ne wannan, sake shi sake shi na ce."
yayi maganar yana jan bayan rigarsa.
ganin baya da niyyar sake shi, baya ma jin me yake fad'a.
Daddy ya kai masa mari yana fad'in
"Kashe shi zakayi? sake shi nace!."
kan sa ya gara da jikin gilashin motar da sai da glass d'in tayi sara ta tsage, sannan ya saki wuyar sa ya juya yana taka kasa da karfi ya nufi side nashi.
Sadam ya durkushe kasa yana dafe wuyansa gami da yin tari.
Daddy ya shi yi masa sannu da bashi hakuri yana tambayar me ya had'a su.
Inspector Nasir ne ya sanar masa abun da ke faruwa.
Daddy ya ce
"Kaji shashanci da shirmen banza, kayi hakuri ku je idan da bukatar na ne me ku zan neme ku, in banda shiririta mace ai allurar cikin ruwa ce,
tashi sannu kaje yi hakuri."
Daddy ya d'ago kafad'ar sa ya mike yana gyara zaman kwalar rigar sa.
ya kad'a yatsun sa yana fad'in
"Bazan kyale shi ba."
ya shiga mota suka bar gidan.
Daddy ya juya yana fad'in
"In banda Abdulrahim ina kai ina fad'a da hukuma,
ai baka isa ka hana wani zuwa gurin ta ba tun da ba auren ka a kanta."
Yau bai tafi asibiti ba sai bayan sallar azahar, sakamakon b'acin ran da yake ciki yau,
ana yin sallar la'asar kuma ya dawo.
sashin Hajiya ya wuce fuska ba annuri.
Hajiya na ganin sa ta ce
"Wai kai abokin turawa yaushe ne fuskarka zata canza?
kullum ya kullum fuska a turnike babu annuri,
da na d'auka had'aka da wancan 'yar da akeyiwa tunanin aljana ce yasa kake b'ata rai,
na mance da dama haka kake,
haba kasaki rai kullum mutum babu walwala, ko akwai wani abun da yake damun ka ne?."
Zama ya yi yana kuma gimtse fuska
"D'anki yasan bazai iya da Mommy ba ya had'a ni da ita, ansan aljanar ce aka bani ita gashi ai tana kan addabata, idan nasa kafa na bar kasar nan bazaku sake gani na ba."
ya yi maganar yana mikewa tsaye ya nufi kofar fita.
Hajiya ta rike hab'a tana fad'in
"To kaji min d'a,
aljanun nata ne suka shige jikin ka suke addabar ka,
to ai gara da ka fad'a da wuri a nemo masu rokiyya, ai da ne muka d'auka aljanar ce ita, yanzu kam mun gano kyawunta ne yasa aljanu shafarta,
dama ba kai kad'ai kake iya tarar su ba, ai dole su shige jikinka,
ashe dai yarinyar kirki ce,
tun da ta hana wancan munafukar Karima'r kashe babanka."
Dadday da ke shigowa ta d'aya kofar parlour'n Hajiya yajiyo hirar tasu, ya jinjina kai tare da yin murmushi irin nasu na manya......!
Mommyn Twins ce
Aunty na tsaye suna waya da Maryam
"Eh Feeryal fa tun d'azu da safe ta shigo tace min gasu Nasir sun zo, sun ce a gaya min zasu shigo amma shiru ban gansu ba,
ashe komawa sukayi to me yasa suka koma kuma, basu shugo ba?."
Shigowar Daddy yana fad'in
"Abdulrahim ne ya kora su."
Aunty ta zaro wayar a kunnen ta tana cewa
"Ina zuwa Maryam zan kira ki."
kallon Daddy ta yi ta ce
"Ya kore su kuma akan me?."
"Sabo da har da manemin Feeryal a cikin su."
shiru Aunty ta yi tana juya batun, Daddy ya ce
"Bansan meye nufin sa na yin hakan ba, bayan babu auren sa a kanta, in ba na ja masa layi ba bazai dai na kora mata mane ma ba."
kai Aunty ta jinjina ta zauna suka kama wani hirar da Daddy.
Shirye-shiryen bikin Zaraddin da Saddiqa yana dad'a kankama, duba da lokaci nata karatowa.
sosai Aunty ta bada himma wajen ganin komai ya tafi yadda ake bukata, dan itace uwar tasu yanzu.
kamar yanda Daddy ya saba a duk sanda za'ayi biki a gidan, kaf 'yan gidan shi yake musu ashobe, adadin yadda suka tsara yin ashoben su ko da yakai kala goma-goma ne. ko yanzu ma hakan ta kasance,
teloli suna ta zuwa karb'ar d'inkin 'yan gidan.
dan bikin saura sati guda ke nan.
Mom da ke tsaye tana kaiwa da kawo wa cikin parlour, waya na rike a hannunta tana ta kiran number Dad.
Dad ya shigo yana fad'in
"Haba kina ta kira tun da nace miki gani zuwa ai zanzo."
"Gara dai na d'aga ma hankali kazo, ni ban gane al'walan kifi a ruwa ba, yau fa saura sati d'aya auren nan, banga wani matakin da kace zaka d'auka ba, in kasan bazaka d'auki wani mataki ba, gara na fita nayi hauka a fasa auren nan, dan na rantse bazan bari a had'a d'ana da karuwa ba, zan d'aga hauka da bori na d'agawa kowa hankali,
tun da kai ka zama matsoraci sai yadda akayi da kai, kazamo kamar rakumi da akala,
sai yadda akayi da kai."
"Matsala ta dake gajen hakuri, ki saurara ki zuba ido kiji."
Dad ya juya ya fita Mom ta d'aga murya tana fad'in
"Idan baka san yadda zakayi ba ni nasan yadda zanyi,
gara ma kasan in da dare ya maka."
"Feeryal fito mutafi mana ke fa shirin ki sai a hankali ni nama fi son ke ki fara shiri sabo da shirin ki sai an jiraki,
kin san halin telan nan idan bamu je ba bazai yi da wuri ba."
"Kai Miemie ai na gama muje."
Feeryal tayi maganar tana gyara zaman gyalen abayar jikinta.
suka fito.
direban Mommy ne zai kaisu Ameerah na zaune a motar tana jiran su, suka karaso.
duka baya suka shiga direba na kokarin tada mota, aka bud'e murfin gefen da Feeryal take.
duk suka juyo da sauri dan ganin wanda ya bud'en.
fuska a gimtse babu wasa yayi wa Feeryal alama da hannu ta fito.
yi tayi kamar bata fahimci a bun da yake nufi ba.
Miemie da Ameerah kuwa kowa ya shiga taitayin sa.
"Fito na ce."
ya fad'a idanunsa a kanta yana kuma gimtse fuska.
kallon motar tayi ta tuna da motar Mommy'n sa ce,
a ranta take fad'in
sabo da motar mamarsa ce ya ce ta fita musu a mota, da sauri ta zura kafarta waje ta sako kafar daf da nashi, soba da yana tsaye daf bakin kofar sosai, ta rab'a gefe ta tafi da sauri ta nufi side d'in Aunty.
ya rufa kofar yayi wa direban alama da su tafi.
ya juya ya na kalmashe hannunsa a kirji idanunsa a kanta harta shige.
Da sauri ta fad'o cikin parlour'n.
Aunty na ganin ta ta ce "Baku tafi ba har yanzu Feeryal?."
baki ta kuma cunowa tana fad'in
"Ammie bani key'n motar ki, Sahab d'in nan dan yaga na shiga motar Mommy'n sa ne zai ce na fita, bazan kara shiga motar bama dama Miemie ce ta ce muje a ciki."
Aunty ta zuba mata ido kamar mai nazarin wani abu sannan ta ce
"Yana d'aki je ki d'auka."
ta wuce da sauri tana kunkuni itafa ya b'ata mata rai abunda ya mata, sabo su kannen sa ne kuma motar mamarsa ne shi yasa ya fito da ita.
ta d'au makullin tayi waje.
Aunty ta ce
"Kije a hankali banda gudu."
Major Sadam ya ce
"Gurin ta nazo."
gimtse fuska ya kuma yana cewa
"Kar ka kara zuwa gurin ta, idan bakaji ba kuma zan d'au mataki a kan ka."
Major Sadam ya ce
"Akan wani dalili zaka hanani zuwa gurin ta, a da take matar ka yanzu kuma ta mai rabo ce,
ka shiga sawun manema mu fafata wanda Allah ya bashi sa'a ya aureta,
babu dalilin da zai ka ka hanani zuwa inda take, dan ni na fara sonta, kuma har gobe bazan daina son ta ba, kuma sai na aure ta."
wani irin shaka yayi wa kwalar Major Sadam cikin fusatacciyar murya ya ce
"Zan iya kashe ka idan ka kara cewa zaka aureta,
sabo da ita d'in matata ce!."
Major Sadam shima ya shake kwalar sa.
da sauri
Inspector Nasir ya shiga kokawar rabasu yana fad'in
"Haba ku kuwa meye haka sai kace wasu kananun yara,
Major sake shi tun da ya ce matar sa ce,
zamu so sanin dalilin sa na fad'in haka."
"Karya ne so yake na hakura na bar masa ita, a da take matarsa ba yanzu ba, ni zan auri Feeryal ni zan aure ta yanzu, na bata kulawar da ya kasa iya bata, cikin wata biyu ya mai da ita karamar bazawa."
ran Abdulrahim ya matur b'aci yanayin da yake shiga idan ransa ya b'aci suka soma bayyana.
damasun sa suna bud'awa yayin da jijiyo yin hannunsa suka mike rad'a-rad'a, zufa yana sassafuwa ta cikin sumar kansa.
wani irin had'a Sadam ya yi da jikin motar da suka zo cikin sa, ya shake wuyansa, idanunsa suka firfito, tamkar zasu zazzago kasa.
Major Sadam ya shiga kokarin kwatar kansa, Inspector Nasir yayi-yayi ya iya b'anb'are hannunsa a wuyan Major Sadam ya kasa.
da karfi ya shiga kiran security ganin numfashin abokin nasa yana kokarin barin jikin sa.
Daddy da ya fito daga side d'in sa zai tafi masallaci ya yi saurin isa inda suke yana fad'in
"Kai Abdulrahim wani irin shashanci ne wannan, sake shi sake shi na ce."
yayi maganar yana jan bayan rigarsa.
ganin baya da niyyar sake shi, baya ma jin me yake fad'a.
Daddy ya kai masa mari yana fad'in
"Kashe shi zakayi? sake shi nace!."
kan sa ya gara da jikin gilashin motar da sai da glass d'in tayi sara ta tsage, sannan ya saki wuyar sa ya juya yana taka kasa da karfi ya nufi side nashi.
Sadam ya durkushe kasa yana dafe wuyansa gami da yin tari.
Daddy ya shi yi masa sannu da bashi hakuri yana tambayar me ya had'a su.
Inspector Nasir ne ya sanar masa abun da ke faruwa.
Daddy ya ce
"Kaji shashanci da shirmen banza, kayi hakuri ku je idan da bukatar na ne me ku zan neme ku, in banda shiririta mace ai allurar cikin ruwa ce,
tashi sannu kaje yi hakuri."
Daddy ya d'ago kafad'ar sa ya mike yana gyara zaman kwalar rigar sa.
ya kad'a yatsun sa yana fad'in
"Bazan kyale shi ba."
ya shiga mota suka bar gidan.
Daddy ya juya yana fad'in
"In banda Abdulrahim ina kai ina fad'a da hukuma,
ai baka isa ka hana wani zuwa gurin ta ba tun da ba auren ka a kanta."
Yau bai tafi asibiti ba sai bayan sallar azahar, sakamakon b'acin ran da yake ciki yau,
ana yin sallar la'asar kuma ya dawo.
sashin Hajiya ya wuce fuska ba annuri.
Hajiya na ganin sa ta ce
"Wai kai abokin turawa yaushe ne fuskarka zata canza?
kullum ya kullum fuska a turnike babu annuri,
da na d'auka had'aka da wancan 'yar da akeyiwa tunanin aljana ce yasa kake b'ata rai,
na mance da dama haka kake,
haba kasaki rai kullum mutum babu walwala, ko akwai wani abun da yake damun ka ne?."
Zama ya yi yana kuma gimtse fuska
"D'anki yasan bazai iya da Mommy ba ya had'a ni da ita, ansan aljanar ce aka bani ita gashi ai tana kan addabata, idan nasa kafa na bar kasar nan bazaku sake gani na ba."
ya yi maganar yana mikewa tsaye ya nufi kofar fita.
Hajiya ta rike hab'a tana fad'in
"To kaji min d'a,
aljanun nata ne suka shige jikin ka suke addabar ka,
to ai gara da ka fad'a da wuri a nemo masu rokiyya, ai da ne muka d'auka aljanar ce ita, yanzu kam mun gano kyawunta ne yasa aljanu shafarta,
dama ba kai kad'ai kake iya tarar su ba, ai dole su shige jikinka,
ashe dai yarinyar kirki ce,
tun da ta hana wancan munafukar Karima'r kashe babanka."
Dadday da ke shigowa ta d'aya kofar parlour'n Hajiya yajiyo hirar tasu, ya jinjina kai tare da yin murmushi irin nasu na manya......!
Mommyn Twins ce
Aunty na tsaye suna waya da Maryam
"Eh Feeryal fa tun d'azu da safe ta shigo tace min gasu Nasir sun zo, sun ce a gaya min zasu shigo amma shiru ban gansu ba,
ashe komawa sukayi to me yasa suka koma kuma, basu shugo ba?."
Shigowar Daddy yana fad'in
"Abdulrahim ne ya kora su."
Aunty ta zaro wayar a kunnen ta tana cewa
"Ina zuwa Maryam zan kira ki."
kallon Daddy ta yi ta ce
"Ya kore su kuma akan me?."
"Sabo da har da manemin Feeryal a cikin su."
shiru Aunty ta yi tana juya batun, Daddy ya ce
"Bansan meye nufin sa na yin hakan ba, bayan babu auren sa a kanta, in ba na ja masa layi ba bazai dai na kora mata mane ma ba."
kai Aunty ta jinjina ta zauna suka kama wani hirar da Daddy.
Shirye-shiryen bikin Zaraddin da Saddiqa yana dad'a kankama, duba da lokaci nata karatowa.
sosai Aunty ta bada himma wajen ganin komai ya tafi yadda ake bukata, dan itace uwar tasu yanzu.
kamar yanda Daddy ya saba a duk sanda za'ayi biki a gidan, kaf 'yan gidan shi yake musu ashobe, adadin yadda suka tsara yin ashoben su ko da yakai kala goma-goma ne. ko yanzu ma hakan ta kasance,
teloli suna ta zuwa karb'ar d'inkin 'yan gidan.
dan bikin saura sati guda ke nan.
Mom da ke tsaye tana kaiwa da kawo wa cikin parlour, waya na rike a hannunta tana ta kiran number Dad.
Dad ya shigo yana fad'in
"Haba kina ta kira tun da nace miki gani zuwa ai zanzo."
"Gara dai na d'aga ma hankali kazo, ni ban gane al'walan kifi a ruwa ba, yau fa saura sati d'aya auren nan, banga wani matakin da kace zaka d'auka ba, in kasan bazaka d'auki wani mataki ba, gara na fita nayi hauka a fasa auren nan, dan na rantse bazan bari a had'a d'ana da karuwa ba, zan d'aga hauka da bori na d'agawa kowa hankali,
tun da kai ka zama matsoraci sai yadda akayi da kai, kazamo kamar rakumi da akala,
sai yadda akayi da kai."
"Matsala ta dake gajen hakuri, ki saurara ki zuba ido kiji."
Dad ya juya ya fita Mom ta d'aga murya tana fad'in
"Idan baka san yadda zakayi ba ni nasan yadda zanyi,
gara ma kasan in da dare ya maka."
"Feeryal fito mutafi mana ke fa shirin ki sai a hankali ni nama fi son ke ki fara shiri sabo da shirin ki sai an jiraki,
kin san halin telan nan idan bamu je ba bazai yi da wuri ba."
"Kai Miemie ai na gama muje."
Feeryal tayi maganar tana gyara zaman gyalen abayar jikinta.
suka fito.
direban Mommy ne zai kaisu Ameerah na zaune a motar tana jiran su, suka karaso.
duka baya suka shiga direba na kokarin tada mota, aka bud'e murfin gefen da Feeryal take.
duk suka juyo da sauri dan ganin wanda ya bud'en.
fuska a gimtse babu wasa yayi wa Feeryal alama da hannu ta fito.
yi tayi kamar bata fahimci a bun da yake nufi ba.
Miemie da Ameerah kuwa kowa ya shiga taitayin sa.
"Fito na ce."
ya fad'a idanunsa a kanta yana kuma gimtse fuska.
kallon motar tayi ta tuna da motar Mommy'n sa ce,
a ranta take fad'in
sabo da motar mamarsa ce ya ce ta fita musu a mota, da sauri ta zura kafarta waje ta sako kafar daf da nashi, soba da yana tsaye daf bakin kofar sosai, ta rab'a gefe ta tafi da sauri ta nufi side d'in Aunty.
ya rufa kofar yayi wa direban alama da su tafi.
ya juya ya na kalmashe hannunsa a kirji idanunsa a kanta harta shige.
Da sauri ta fad'o cikin parlour'n.
Aunty na ganin ta ta ce "Baku tafi ba har yanzu Feeryal?."
baki ta kuma cunowa tana fad'in
"Ammie bani key'n motar ki, Sahab d'in nan dan yaga na shiga motar Mommy'n sa ne zai ce na fita, bazan kara shiga motar bama dama Miemie ce ta ce muje a ciki."
Aunty ta zuba mata ido kamar mai nazarin wani abu sannan ta ce
"Yana d'aki je ki d'auka."
ta wuce da sauri tana kunkuni itafa ya b'ata mata rai abunda ya mata, sabo su kannen sa ne kuma motar mamarsa ne shi yasa ya fito da ita.
ta d'au makullin tayi waje.
Aunty ta ce
"Kije a hankali banda gudu."