Sashe 33
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata mota ce ta sauke Kuraiba ta shigo gidan su, a parlour ta tadda Hajiya Luba.
Hajiya Luba ta bita da kallon bakinciki.
ta kasara ta zube kan kujera tana fad'in
"Wai dan Allah Momma yau she ne zaki je ki sami Mommy ki bata hakuri na koma d'aki na,
wlh ni nagaji da zaman gidan nan, ko ba komai a can ina ganin Abdulrahim naji dad'i,
haba dan Allah ni wlh nagaji ina son Abdulrahim shi d'in had'ad'd'en gaye ne,
ganin sa ma kawai yakan iya gusar da karamin kishi,
kar iddata ta cika azo kuma dole sai an sake d'aura aure."
wani uban harara uwar tata ta doka masa tare da jan dogon tsaki ta ce
"Ai kin banza wai ke a hakan har kina tuanin Abdulrahim zai maida ki,
tun da kika dawo gidan nan fa kullum a kan hanyar fita kike,
kullum mai d'aukar ki daban mai dawowa da ke daban,
a hakan zaki koma ki cigaba da kasancewa a matsayin surukar gidan AA FIYA,
ai tun da kika rushe min shirina ke ma bazaki sami abun da kike so ba,
sai ki mike kafa mucigana da zama dake a cikin gidan nan,
ke da Abdulrahim kuwa har a bada."
Kuraiba ta mike tana cewa
"To ai shi ke nan ni nasan yadda zanyi na koma."
ta wuce d'akin ta....
A hankali cikin Feeryal ke dad'a wayo, kusan kullum tana tare da Ammie'n suna waya video call tana ganin lafiyar.
Maryam ta koma gun mijin ta can Ogun State bayan tayi wata biyu da haihuwa. yanzu ita d'aya ce tare suke kwana da Hajja Umma, ita ke kula da ita sosai, wata nayi zata kaita gun awu a duba cikin aga lafiyar sa.
san da Major Sadam yasan da cikin yaji ba dad'i dan yasan dole yanzu sai ta hife cikin kafin ya samu damar aurenta.
ya kudara wa ransa zai jira ta haihu amma ba zai jira har sai ta yaye ba, zai aure ta tazo da abun da ta haifa gidan sa.
san da cikin ya kai watanni 8 Daddy ya yi tattaki yazo garin Abuja.
ya ce yazo tafiya da ita yana so ta haihu a can Lagos.
Abba ya ce sam bazai tafi da itaba, a nan zata haihu su da suka kasa iya rike ta.
da kyar Daddy ya shawo kan Abba ya aminta su tafi da ita.
karfe 8 na safiya jirginsu ya tashi zuwa Logos.
karfe goma saura suka iso Lagos, wanda tuni mota ya iso airport yana zaman jiran saukowar su.
direban Daddy ya kwashe su suka nufi AA FIYA STREET.
Aunty na tsaye a farfajiyar side d'in ta tana zaman jiran isowarsu.
tun kafin motar ya gyara parking ta taho da sauri mai had'e da gudu ta taho jikin motar.
motar na tsayuwa ta bud'e da sauri tana fad'in
"Oyoyo 'Yammatan Ammie."
Feeryal da farincikin ganin Ammien ta ya lullub'e ta tafi to da sauri, zata rungume ta Aunty ta ce
"Tsaya tsaya bi a hankali."
tayi maganar tana kallon katon cikin ta.
kallonta bai isheta ba wai Feeryal d'in ta ce haka Allah buwayi.
Daddy ko Dariya ya yi ganin yadda gaba d'aya ta tsaya kallon ta.
cikin tsigar zolaya ya ce
"To kaka Fad'imatu a kaita ciki ta huta mana."
Aunty ta yi murmushi tare da janyo hannunta suka shige ciki.. Daddy ko ya koma motar direba ya kaishi side d'in sa.
a parlour Aunty tasa ta zauna kasan carpet ta mike kafafunta, da suka d'an kumbura.
ta je dinning ta kwaso mata lafiyayyun cake data shirya mana na musamman, gami da yogurt na musamman ta dire shi a gabanta.
kana ta zauna gefen ta tana ta yi mata sannu, kallon Feeryal baya isar ta wai 'yar ita ce da katon ciki irin wannan."
ta kuma fad'in
"Sannu kinji Feeryal Allah ya sauke ki lafiya, ga ababen kaunar ki na musamman na shirya miki."
murmushi ta yi ta ce
"Ammie yanzun fa ina cin abinci musamman tuwo sosai nake ci."
"Ai dole kici abinci Feeryal wannan ciki, dole ya saki cin abinci."
sunkuyar da kamta tayi tana kai loman cake bakin ta.
Aunty ta d'au waya ta kira Ammah ta shaida mata isowar Feeryal d'in.
kan kace me Miemie ta shigo.
ta bud'e baki da hanci tana kallon ta.
"Kai Miemie babu oyoyo."
Feeryal ta fad'a tana mata murmushi.
"Hum Feeryal ke ce haka?."
Miemie ta fad'a tana rike hab'a tare da zama kusa da ita, cike da farinciki mai had'e da mamakin ganin ciki ya bayyana sosai a jikin ta.
Ammah data shigo yamzu itama tsayuwa kallon Feeryal d'in tayi da mamaki.
kana ta rangad'a gud'a tana fad'in
"Kaga d'an duma ko a fad'e ka ko ayi shiru zaka bayyana kanka,
anyi sake d'an zaki ya girma,
Allah sarki Feeryal sannu da kokari Allah ya kauda idon makiya."
Aunty ta yi dariya tana fad'in
"Kai Ammah'n Miemie irin wanan gud'a da kirari irin haka."
"Barni na fad'i da babban murya lokacin fad'ar ne yayi, kaga ikon Allah ba'ayi wa Allah dabara, shi ke tsara komai yadda yaso baya shawari da kowa."
Ammah tayi maganar tana zama da ci gaba da fad'in
"Amma ace cikin nan bai kai na haihuwa ba duk girmansa."
Aunty ta ce
"Ai kuwa dai kam da sauran wata d'aya nan gaba."
"To Allah ya bud'i ido lafiya."
Aunty ta amsa da "Amin ya rabbil alamina."
Tuni labari ya karad'e gidan Feeryal ta dawo da ciki rukuku.
hankalin Umma karima ya tashi, yaran gidan kuwa sai zuwa suke kallonta 'ya'yan Umma karima suka kai mata rohoto ciki ne babba a jikin Feeryal, hankalin ta ya dad'a dugunzuma.
Ajmaal na dawo daga gurin aiki bai wuce sashin su ba ya shigo sashin Aunty.
baki ya bud'e yana kallon Feeryal da katon ciki.
cikin ya zauna d'as ya yi mata kyau duk da girman sa,
ta kara haske sosai.
murmushi ta yi masa ta ce
"Sannu Ya Ajmaal."
ya karaso yana fad'in
"Sannu Feeryal ke ce da gaisuwa ai,
muna godiya da maraba da zuwan babyn mu."
murmushi ta kuma tana sunkuyar da kanta kasa.
Shamsuddin da Faisal da suka biyo bayan sa, suma duk suka tsaya kallon ta.
duk ta gaishe su kanta a kasa, suna yimata barka da zuwa.
da nuna farincikin su da ganin cikin.
Aunty ta fito ta ce
"Ku zauna mana Shamsuddin."
Ajmaal ya ce
"Dawowan mu ke nan daga gun aiki, zamu shigo anjima."
suka fita.
"Fito muje Bishira kar a ajiye abun fad'a, tun da ya amsa cikin nashi ne, ai shike nan maje mu dubota kar ace dai babu je, har ta kwana, yaro da kalen fitina da son sa mutane wahala."
Hajiya dake tsaye tana jiran fitowar goggo Bishira tayi maganar.
goggo Bishira ta fito tana gyara mayafin ta suka nufi side d'in Aunty.
suna sallama Aunty ta tare su cike da karramawa suka zauna,
Aunty ta zamo bakin kujera tana gaida Hajiya.
ba yabo ba fallasa ta amsa.
suka gaisa da goggo Boshira,
Hajiya ta ce "Ina ita yarinyar take?."
Aunty ta mike ta ce "Yanzu ta shiga ciki bari a kira ta."
Goggo Bishira ta ce
"Aunty Faty in bacci take ki barta."
"Aa ba bacci take ba, yanzunnan ta shiga."
Aunty ta shige d'aki suka fito da Feeryal.
Hajiya ta bita da ido har ta zauna kasan carpet.
Hajiya data rike baki ta ce "To haka abun yayi, to sannu ya nauyin jiki."
Feeryal ta sunkuyar da kai tana cewa "Ina kwana."
Hajiya bata amsa ba sai kallon ta da take. tana cewa
"Da gaske dai cikin ne."
goggo Bishira ta dube ta ta ce
"Sannu Feeryal ya nauyin jikin."
kai takuma sunkuyar wa tana wasa da 'yan yatsunta.
sannan ta gaishe ta.
goggo Bishira ta amsa tana kuma tambayar ta ya nauyin jiki.
nan ma kai ta kuma sunkuyar wa.
Hajiya ta mike tana cewa
"To Allah ya bud'i ido lafiya."
goggo Bishira tayi wa Aunty sallama suka tafi.
Umma karima bata iya hakuri ba sai da tazo sashin Aunty ta gane wa idanunta zahiri.
Aunty na ganin ta tayi wani murmushi ta ce
"Ki karaso mana Hajiya Karima ya zaki tsaya daga bakin kofa,
ga gurin zama ki zauna."
Umma karima data dibirbirce da ganin Feeryal zaune da katon ciki a gaba.
ta juya har tana cin karo ta fita.
Aunty ta yi dariya tana girgiza kai.
Kwanan Feeryal biyar da zuwa, bata fita ko kofa daga parlour sai bedroom d'in kwanan ta.
suna zaune da Miemi suna hira, Miemie ta mike ta ce zata tafi, Feeryal ta rako ta har wajen get d'in Aunty wan da tun zuwanta bata fito nan ba.
suna tsaye a bakin get d'in ta waje Miemie ta ce
"Feeryal wannan katon ciki yaushe ne zaki haifo shi,
ni yau sai naga cikin ya karamin girma, ko zaki haihu ne? ni nayi zaton a ranar da kika zo ma Allah haihuwa zakiyi, sai numfashi kike da kyar."
Feeryal tayi murmushi.
"Miemie ni kam zan koma nagaji da tsayuwa."
"Ke ai yanzu ko abin gudu ya zo sai dai a gudu a barki."
"Kai Miemie me zai hana ni iya gudu."
ta juya tana dariya.
cak ta tsaida dariyar da take, hango shi yana tahowa da alama masallaci zai tafi, dan ana kokarin shiga sallar la'asar.
da sauri ta kawar da kanta ganin idanunsa a kanta,
tasa kai ta shige dad'an sauri...
Tun da Feeryal ta shiga watan haihuwan ta, bata bacci kullum ciwon baya ciwon mara,
yau kuwa ta tashi da ciwon dayafi na kullum.
hankalin Aunty ya bala'in tashi.
Daddy ya ce maza a wuce da ita asibiti.
asibitin Dr family'n su aka wuce da ita, dan Daddy ya ce baza'a kaita asibitin Abdulrahim ba.
yana dubata ya ce C'S za'ayi mata batare da b'ata lokaci ba aka shige da ita operation room.....!
Hajiya Luba ta bita da kallon bakinciki.
ta kasara ta zube kan kujera tana fad'in
"Wai dan Allah Momma yau she ne zaki je ki sami Mommy ki bata hakuri na koma d'aki na,
wlh ni nagaji da zaman gidan nan, ko ba komai a can ina ganin Abdulrahim naji dad'i,
haba dan Allah ni wlh nagaji ina son Abdulrahim shi d'in had'ad'd'en gaye ne,
ganin sa ma kawai yakan iya gusar da karamin kishi,
kar iddata ta cika azo kuma dole sai an sake d'aura aure."
wani uban harara uwar tata ta doka masa tare da jan dogon tsaki ta ce
"Ai kin banza wai ke a hakan har kina tuanin Abdulrahim zai maida ki,
tun da kika dawo gidan nan fa kullum a kan hanyar fita kike,
kullum mai d'aukar ki daban mai dawowa da ke daban,
a hakan zaki koma ki cigaba da kasancewa a matsayin surukar gidan AA FIYA,
ai tun da kika rushe min shirina ke ma bazaki sami abun da kike so ba,
sai ki mike kafa mucigana da zama dake a cikin gidan nan,
ke da Abdulrahim kuwa har a bada."
Kuraiba ta mike tana cewa
"To ai shi ke nan ni nasan yadda zanyi na koma."
ta wuce d'akin ta....
A hankali cikin Feeryal ke dad'a wayo, kusan kullum tana tare da Ammie'n suna waya video call tana ganin lafiyar.
Maryam ta koma gun mijin ta can Ogun State bayan tayi wata biyu da haihuwa. yanzu ita d'aya ce tare suke kwana da Hajja Umma, ita ke kula da ita sosai, wata nayi zata kaita gun awu a duba cikin aga lafiyar sa.
san da Major Sadam yasan da cikin yaji ba dad'i dan yasan dole yanzu sai ta hife cikin kafin ya samu damar aurenta.
ya kudara wa ransa zai jira ta haihu amma ba zai jira har sai ta yaye ba, zai aure ta tazo da abun da ta haifa gidan sa.
san da cikin ya kai watanni 8 Daddy ya yi tattaki yazo garin Abuja.
ya ce yazo tafiya da ita yana so ta haihu a can Lagos.
Abba ya ce sam bazai tafi da itaba, a nan zata haihu su da suka kasa iya rike ta.
da kyar Daddy ya shawo kan Abba ya aminta su tafi da ita.
karfe 8 na safiya jirginsu ya tashi zuwa Logos.
karfe goma saura suka iso Lagos, wanda tuni mota ya iso airport yana zaman jiran saukowar su.
direban Daddy ya kwashe su suka nufi AA FIYA STREET.
Aunty na tsaye a farfajiyar side d'in ta tana zaman jiran isowarsu.
tun kafin motar ya gyara parking ta taho da sauri mai had'e da gudu ta taho jikin motar.
motar na tsayuwa ta bud'e da sauri tana fad'in
"Oyoyo 'Yammatan Ammie."
Feeryal da farincikin ganin Ammien ta ya lullub'e ta tafi to da sauri, zata rungume ta Aunty ta ce
"Tsaya tsaya bi a hankali."
tayi maganar tana kallon katon cikin ta.
kallonta bai isheta ba wai Feeryal d'in ta ce haka Allah buwayi.
Daddy ko Dariya ya yi ganin yadda gaba d'aya ta tsaya kallon ta.
cikin tsigar zolaya ya ce
"To kaka Fad'imatu a kaita ciki ta huta mana."
Aunty ta yi murmushi tare da janyo hannunta suka shige ciki.. Daddy ko ya koma motar direba ya kaishi side d'in sa.
a parlour Aunty tasa ta zauna kasan carpet ta mike kafafunta, da suka d'an kumbura.
ta je dinning ta kwaso mata lafiyayyun cake data shirya mana na musamman, gami da yogurt na musamman ta dire shi a gabanta.
kana ta zauna gefen ta tana ta yi mata sannu, kallon Feeryal baya isar ta wai 'yar ita ce da katon ciki irin wannan."
ta kuma fad'in
"Sannu kinji Feeryal Allah ya sauke ki lafiya, ga ababen kaunar ki na musamman na shirya miki."
murmushi ta yi ta ce
"Ammie yanzun fa ina cin abinci musamman tuwo sosai nake ci."
"Ai dole kici abinci Feeryal wannan ciki, dole ya saki cin abinci."
sunkuyar da kamta tayi tana kai loman cake bakin ta.
Aunty ta d'au waya ta kira Ammah ta shaida mata isowar Feeryal d'in.
kan kace me Miemie ta shigo.
ta bud'e baki da hanci tana kallon ta.
"Kai Miemie babu oyoyo."
Feeryal ta fad'a tana mata murmushi.
"Hum Feeryal ke ce haka?."
Miemie ta fad'a tana rike hab'a tare da zama kusa da ita, cike da farinciki mai had'e da mamakin ganin ciki ya bayyana sosai a jikin ta.
Ammah data shigo yamzu itama tsayuwa kallon Feeryal d'in tayi da mamaki.
kana ta rangad'a gud'a tana fad'in
"Kaga d'an duma ko a fad'e ka ko ayi shiru zaka bayyana kanka,
anyi sake d'an zaki ya girma,
Allah sarki Feeryal sannu da kokari Allah ya kauda idon makiya."
Aunty ta yi dariya tana fad'in
"Kai Ammah'n Miemie irin wanan gud'a da kirari irin haka."
"Barni na fad'i da babban murya lokacin fad'ar ne yayi, kaga ikon Allah ba'ayi wa Allah dabara, shi ke tsara komai yadda yaso baya shawari da kowa."
Ammah tayi maganar tana zama da ci gaba da fad'in
"Amma ace cikin nan bai kai na haihuwa ba duk girmansa."
Aunty ta ce
"Ai kuwa dai kam da sauran wata d'aya nan gaba."
"To Allah ya bud'i ido lafiya."
Aunty ta amsa da "Amin ya rabbil alamina."
Tuni labari ya karad'e gidan Feeryal ta dawo da ciki rukuku.
hankalin Umma karima ya tashi, yaran gidan kuwa sai zuwa suke kallonta 'ya'yan Umma karima suka kai mata rohoto ciki ne babba a jikin Feeryal, hankalin ta ya dad'a dugunzuma.
Ajmaal na dawo daga gurin aiki bai wuce sashin su ba ya shigo sashin Aunty.
baki ya bud'e yana kallon Feeryal da katon ciki.
cikin ya zauna d'as ya yi mata kyau duk da girman sa,
ta kara haske sosai.
murmushi ta yi masa ta ce
"Sannu Ya Ajmaal."
ya karaso yana fad'in
"Sannu Feeryal ke ce da gaisuwa ai,
muna godiya da maraba da zuwan babyn mu."
murmushi ta kuma tana sunkuyar da kanta kasa.
Shamsuddin da Faisal da suka biyo bayan sa, suma duk suka tsaya kallon ta.
duk ta gaishe su kanta a kasa, suna yimata barka da zuwa.
da nuna farincikin su da ganin cikin.
Aunty ta fito ta ce
"Ku zauna mana Shamsuddin."
Ajmaal ya ce
"Dawowan mu ke nan daga gun aiki, zamu shigo anjima."
suka fita.
"Fito muje Bishira kar a ajiye abun fad'a, tun da ya amsa cikin nashi ne, ai shike nan maje mu dubota kar ace dai babu je, har ta kwana, yaro da kalen fitina da son sa mutane wahala."
Hajiya dake tsaye tana jiran fitowar goggo Bishira tayi maganar.
goggo Bishira ta fito tana gyara mayafin ta suka nufi side d'in Aunty.
suna sallama Aunty ta tare su cike da karramawa suka zauna,
Aunty ta zamo bakin kujera tana gaida Hajiya.
ba yabo ba fallasa ta amsa.
suka gaisa da goggo Boshira,
Hajiya ta ce "Ina ita yarinyar take?."
Aunty ta mike ta ce "Yanzu ta shiga ciki bari a kira ta."
Goggo Bishira ta ce
"Aunty Faty in bacci take ki barta."
"Aa ba bacci take ba, yanzunnan ta shiga."
Aunty ta shige d'aki suka fito da Feeryal.
Hajiya ta bita da ido har ta zauna kasan carpet.
Hajiya data rike baki ta ce "To haka abun yayi, to sannu ya nauyin jiki."
Feeryal ta sunkuyar da kai tana cewa "Ina kwana."
Hajiya bata amsa ba sai kallon ta da take. tana cewa
"Da gaske dai cikin ne."
goggo Bishira ta dube ta ta ce
"Sannu Feeryal ya nauyin jikin."
kai takuma sunkuyar wa tana wasa da 'yan yatsunta.
sannan ta gaishe ta.
goggo Bishira ta amsa tana kuma tambayar ta ya nauyin jiki.
nan ma kai ta kuma sunkuyar wa.
Hajiya ta mike tana cewa
"To Allah ya bud'i ido lafiya."
goggo Bishira tayi wa Aunty sallama suka tafi.
Umma karima bata iya hakuri ba sai da tazo sashin Aunty ta gane wa idanunta zahiri.
Aunty na ganin ta tayi wani murmushi ta ce
"Ki karaso mana Hajiya Karima ya zaki tsaya daga bakin kofa,
ga gurin zama ki zauna."
Umma karima data dibirbirce da ganin Feeryal zaune da katon ciki a gaba.
ta juya har tana cin karo ta fita.
Aunty ta yi dariya tana girgiza kai.
Kwanan Feeryal biyar da zuwa, bata fita ko kofa daga parlour sai bedroom d'in kwanan ta.
suna zaune da Miemi suna hira, Miemie ta mike ta ce zata tafi, Feeryal ta rako ta har wajen get d'in Aunty wan da tun zuwanta bata fito nan ba.
suna tsaye a bakin get d'in ta waje Miemie ta ce
"Feeryal wannan katon ciki yaushe ne zaki haifo shi,
ni yau sai naga cikin ya karamin girma, ko zaki haihu ne? ni nayi zaton a ranar da kika zo ma Allah haihuwa zakiyi, sai numfashi kike da kyar."
Feeryal tayi murmushi.
"Miemie ni kam zan koma nagaji da tsayuwa."
"Ke ai yanzu ko abin gudu ya zo sai dai a gudu a barki."
"Kai Miemie me zai hana ni iya gudu."
ta juya tana dariya.
cak ta tsaida dariyar da take, hango shi yana tahowa da alama masallaci zai tafi, dan ana kokarin shiga sallar la'asar.
da sauri ta kawar da kanta ganin idanunsa a kanta,
tasa kai ta shige dad'an sauri...
Tun da Feeryal ta shiga watan haihuwan ta, bata bacci kullum ciwon baya ciwon mara,
yau kuwa ta tashi da ciwon dayafi na kullum.
hankalin Aunty ya bala'in tashi.
Daddy ya ce maza a wuce da ita asibiti.
asibitin Dr family'n su aka wuce da ita, dan Daddy ya ce baza'a kaita asibitin Abdulrahim ba.
yana dubata ya ce C'S za'ayi mata batare da b'ata lokaci ba aka shige da ita operation room.....!