Sashe 34
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Nan da nan aka soma shirya yi mata CS, in da likitan da wasu ma'aikatan sa suka soma gudanar da C'S d'in.
Aunty da Daddy suna tsaye a bakin kofar hankali tashe.
sai anbaton sunan Allah suke da nima mata sassauci daga Allah.
motarsa ne ya shigo asibitin a guje,bai tsaya wani dai-dai parking ba ya fito da sauri.
Daddy ya bishi da kallon me ya kawo ka, fuska a d'aure.
cikin tafiya mai kamada gudu ya shige cikin operation room theater theater d'in da sauri.
yana shiga
sauran ma'aikatan suka juyo, dan ganin wanda ya shigo musu kai tsaye,
shiko likitan bai d'ago ba yana ta kan tsaga ta.
da sauri ya isa gaban wani hanga ya janyo rigar da likitoti suke sakawa idan zasuyi
operation, ya d'aura kan kayan jikinsa. kana ya zaro hand glove da facemask ya nufi gadon ya na saka hand guluf da facemask.
da sauri ya shige gaban sauran ma'aikatan ya tsaya gefen likitan, dai-dai san da likitan yake tsaga fatar karshe.
yayi saurin kai hannunsa guda kan hannunsa ya ruko askar. yayin da
hannunsa guda ya kai fuskarsa ya ja facemask d'in kasa likitan ya juyo ya kalleshi, sanin ko waye shi
sai ya sakar masa ya d'an ja gefe. ya gyara zaman facemask d'in, cikin kwarewa da sanin aikin sa ya idda karasawa ya zaro babyn, wanda tuni ya calla kara yana wutsil-wutsil da kafafu da hannaye.
ya lumshe ido yana bud'e wa a kansa, kana
ya mikawa likitar bayan ya rabashi da cibiyar,
shiko likitan ya mikawa sauran ma'aikatan, suka kai shi gadon da aka tanada domin gyara jarirai.
ya gyara tsayuwarsa da kyau yana bud'a hanyar tare da kuma zaro wani d'an.
ya sauke wani ajiyam zuciya a fili, yayin da idanunsa ke kan d'an.
bayan ya kuma mi ka musu, nan da nan ya soma d'in ke ta
in da likitan ya cigaba da taimaka masa da karb'ar kayan aikin da miko masa abun da yake bukata.
nurse biyu mata suna tsaye daga kanta suna ta janta da hira,
jifa-jifa take amsasu cikin tsiririyar muryarta.
cikin kankanin lokaci ya gama, ya matso ta kanta idanunta a lumshe take basu amsar magar da suka matsa mata da yin sa.
hannunta ya kama ya had'e hannayen nasu kana ya sake a hankali ya juya.
a sannu ta bud'e idanunta tabi bayan sa da kallo, bawai ko dan ta gane ko waye bane sakamakon shigar dake jikinsa irin na sauran likitotin.
ya taka gaban gadon da jariran suke, wanda tuni an kimsasu cikin kaya masu kyau da tsada wan da Aunty ta taho da shi.
ido ya kura musu suna ta shure kafafu da kokarin tura hannu a baki.
a sannu ya mika hannayen sa ya ruko hannayen su.
ya kura musu ido sosai yana d'an jijjiga hannun nasu, fuskarsa a yalwace da annuri yana ta sakin tsiririn murmushi wa yaran.
wasu nurse mata biyu suka karaso gurin cikin girmamawa suka ce
"Sir bari mu d'auke su iyayen patent d'in suna waje, tun d'azu suke cewa a fito musu da su, anyi musu albishir twins aka ciro."
baiyi magana ba bai kuma fasa wasan da yake da hannayen su ba.
yakai 10second kafin ya zame hannun sa daga nasu, yad'an matsa gefe.
suka d'auke su suka fito sa su.
Daddy da Aunty har suna rige-rigen karb'ar su.
Aunty ta rungume wanda aka mika mata tana fad'in
"Alhamdulillah!."
Daddy ma haka bakinsa ya kasa rufuwa.
bayan ya yi wa nurse's d'in tukuici da kud'i masu yawa.
Abdulrahim ya fito yana warware hannun rigarsa.
Aunty ta bishi da murmushi da farincikin daya gaza b'oyuwa a fuskarta, tana fad'in
"Sannun ku da aiki Abdulrahim."
Daddy kuwa bai kalli in da yake ba, idanunsa akan jikarsa, daya gaza janye ido a kansa.
kai ya jinjina ya wuce ya tafi can gefe yana d'aga kiran yada shigo wayarsa.
aka fito da Feeryal a ture a kan gado aka wuce da ita wani room.
su Daddy suka bi bayan su da sauri, yana tsaye yana kallon wucewar su.
Ajmaal da Shamsuddin da Faisal ne su shigo da sauri suka karoso in da yake cike da matukar farinciki suke fad'in
"Ya Abdulrahim ina baby's d'in mu, ina twins d'in mu suke!."
sukayi maganar cike da matukar farinciki sosai.
dan tuni Daddy ya kira ya fad'a musu tun kafin a fito da ita.
murmushin gefen baki yayi ganin yadda suke maganar kamar kananun yara suna wani tsalle ya ce
"Suna can."
ya nuna musu kofar room d'in da aka shige da Feeryal.
ai ko da sauri suka juya suna rige-rigen shiga.
shiko ya fice ya shiga motarsa ya bar asibitin.
su Ajmaal
suka karb'e yaran a hannun su Aunty kamar zasu had'iye su dan farinciki.
sai yabawa da zuzuta kyan su suke.
Daddy yayi murmushi yana kallon yadda suke yi kamar zasu had'iye yaran.
ya ce "Iye anyi 'ya'ya sai murna ake."
sukayi dariya Shamsuddin ya ce
"Wayyo kalle su fa kyawawa wlh duk kama da Ya Abdulram suke, suka d'auko farin Feeryal."
"Asalin kama ma kuwa."
cewar Ajmaal da Faisal.
Aunty tayi murmushi dan ko ba karya 'ya'yan asalin kama da uban su suke.
sai sannan suka masa bakin gado in da Feeryal ke kwance suka gaisheta suna yi mata ya jiki.
murmushi tayi musu tana lumshe idanunta tare da juya fuskarta ta jikin garo.
Daddy ya ce
"To mu fitan ku waje likita ya ce a barta ta huta, ku bawa Aunty'n ku yaran ta kwantar da su suma suna bukatar hutu."
suna shirin fita Hajiya da Goggo Bishira Ammah Miemie Kulu mai aikin Hajiya da Sumayya suka shigo.
Miemie kamar zatayi tsalle dan murna Sumayya ma haka, dan ita halinta da sauki dan wani lokaci bata d'aukar zugar Ameerah.
ko da suka fito zata biyo su Hajiya Ameerah ce mata tayi wai zataje kallon 'ya'yan aljanu ita ba inda zata.
ita Sumayya na son yaran tun bata gansu ba, tana ji a ranta ko ba komai dai 'ya'yan yayansu ne, dan bata daga cikin 'yan'uwan ta masu cewa ba cikin yayan nasu bane.
Miemie da Sumayya suka riga kowa d'aukar yaran.
da kyar goggo Bishira ta karb'i na hannun Sumayya dan Miemie kam ta rike na hannunta gam.
Hajiya ta leko fuskar su ta tana fad'in
"Eh to ga kamar abokin turawa a jikin su, ah to yanzu kam hankali zai kwanta."
Ammah ta girgiza kai.
Aunty ko Murmushi kawai tayi.
sai da likita ya shigo ya ce su bata guri ta huta kafin kowa ya fita aka bar Aunty da ita.
da zasu tafi Sumayya da Miemie suka ce su bazasu tafi ba,
suna tare da Aunty a asibitin.
Sumayya tana like da yaran da har cikin ranta take jin kaunarsu.
Aunty ta kira su Hajja Umma ta video call.
Abba da Hajja Umma sunyi matukar farinciki Aunty ta hasko musu yaran sunata yabawa da fatan Allah ya raya.
lokacin bacci ya d'auki Feeryal suka ce idan ta tashi zasu kira.
Aunty na kashewa ta kira Maryam, Maryam kamar zata fasa wayar da ihu
"Wai da gaske Aunty Faty Feeryal twin's ta haifa?."
cewar Maryam cike da zallar farinciki.
Aunty tayi dariya tana fad'in
"Gasu kuwa kina gani."
ta ce "Jibi ina hanya inasha'allah."
Aunty ta kashe tana mata dariya.
Aunty da Daddy suna tsaye a bakin kofar hankali tashe.
sai anbaton sunan Allah suke da nima mata sassauci daga Allah.
motarsa ne ya shigo asibitin a guje,bai tsaya wani dai-dai parking ba ya fito da sauri.
Daddy ya bishi da kallon me ya kawo ka, fuska a d'aure.
cikin tafiya mai kamada gudu ya shige cikin operation room theater theater d'in da sauri.
yana shiga
sauran ma'aikatan suka juyo, dan ganin wanda ya shigo musu kai tsaye,
shiko likitan bai d'ago ba yana ta kan tsaga ta.
da sauri ya isa gaban wani hanga ya janyo rigar da likitoti suke sakawa idan zasuyi
operation, ya d'aura kan kayan jikinsa. kana ya zaro hand glove da facemask ya nufi gadon ya na saka hand guluf da facemask.
da sauri ya shige gaban sauran ma'aikatan ya tsaya gefen likitan, dai-dai san da likitan yake tsaga fatar karshe.
yayi saurin kai hannunsa guda kan hannunsa ya ruko askar. yayin da
hannunsa guda ya kai fuskarsa ya ja facemask d'in kasa likitan ya juyo ya kalleshi, sanin ko waye shi
sai ya sakar masa ya d'an ja gefe. ya gyara zaman facemask d'in, cikin kwarewa da sanin aikin sa ya idda karasawa ya zaro babyn, wanda tuni ya calla kara yana wutsil-wutsil da kafafu da hannaye.
ya lumshe ido yana bud'e wa a kansa, kana
ya mikawa likitar bayan ya rabashi da cibiyar,
shiko likitan ya mikawa sauran ma'aikatan, suka kai shi gadon da aka tanada domin gyara jarirai.
ya gyara tsayuwarsa da kyau yana bud'a hanyar tare da kuma zaro wani d'an.
ya sauke wani ajiyam zuciya a fili, yayin da idanunsa ke kan d'an.
bayan ya kuma mi ka musu, nan da nan ya soma d'in ke ta
in da likitan ya cigaba da taimaka masa da karb'ar kayan aikin da miko masa abun da yake bukata.
nurse biyu mata suna tsaye daga kanta suna ta janta da hira,
jifa-jifa take amsasu cikin tsiririyar muryarta.
cikin kankanin lokaci ya gama, ya matso ta kanta idanunta a lumshe take basu amsar magar da suka matsa mata da yin sa.
hannunta ya kama ya had'e hannayen nasu kana ya sake a hankali ya juya.
a sannu ta bud'e idanunta tabi bayan sa da kallo, bawai ko dan ta gane ko waye bane sakamakon shigar dake jikinsa irin na sauran likitotin.
ya taka gaban gadon da jariran suke, wanda tuni an kimsasu cikin kaya masu kyau da tsada wan da Aunty ta taho da shi.
ido ya kura musu suna ta shure kafafu da kokarin tura hannu a baki.
a sannu ya mika hannayen sa ya ruko hannayen su.
ya kura musu ido sosai yana d'an jijjiga hannun nasu, fuskarsa a yalwace da annuri yana ta sakin tsiririn murmushi wa yaran.
wasu nurse mata biyu suka karaso gurin cikin girmamawa suka ce
"Sir bari mu d'auke su iyayen patent d'in suna waje, tun d'azu suke cewa a fito musu da su, anyi musu albishir twins aka ciro."
baiyi magana ba bai kuma fasa wasan da yake da hannayen su ba.
yakai 10second kafin ya zame hannun sa daga nasu, yad'an matsa gefe.
suka d'auke su suka fito sa su.
Daddy da Aunty har suna rige-rigen karb'ar su.
Aunty ta rungume wanda aka mika mata tana fad'in
"Alhamdulillah!."
Daddy ma haka bakinsa ya kasa rufuwa.
bayan ya yi wa nurse's d'in tukuici da kud'i masu yawa.
Abdulrahim ya fito yana warware hannun rigarsa.
Aunty ta bishi da murmushi da farincikin daya gaza b'oyuwa a fuskarta, tana fad'in
"Sannun ku da aiki Abdulrahim."
Daddy kuwa bai kalli in da yake ba, idanunsa akan jikarsa, daya gaza janye ido a kansa.
kai ya jinjina ya wuce ya tafi can gefe yana d'aga kiran yada shigo wayarsa.
aka fito da Feeryal a ture a kan gado aka wuce da ita wani room.
su Daddy suka bi bayan su da sauri, yana tsaye yana kallon wucewar su.
Ajmaal da Shamsuddin da Faisal ne su shigo da sauri suka karoso in da yake cike da matukar farinciki suke fad'in
"Ya Abdulrahim ina baby's d'in mu, ina twins d'in mu suke!."
sukayi maganar cike da matukar farinciki sosai.
dan tuni Daddy ya kira ya fad'a musu tun kafin a fito da ita.
murmushin gefen baki yayi ganin yadda suke maganar kamar kananun yara suna wani tsalle ya ce
"Suna can."
ya nuna musu kofar room d'in da aka shige da Feeryal.
ai ko da sauri suka juya suna rige-rigen shiga.
shiko ya fice ya shiga motarsa ya bar asibitin.
su Ajmaal
suka karb'e yaran a hannun su Aunty kamar zasu had'iye su dan farinciki.
sai yabawa da zuzuta kyan su suke.
Daddy yayi murmushi yana kallon yadda suke yi kamar zasu had'iye yaran.
ya ce "Iye anyi 'ya'ya sai murna ake."
sukayi dariya Shamsuddin ya ce
"Wayyo kalle su fa kyawawa wlh duk kama da Ya Abdulram suke, suka d'auko farin Feeryal."
"Asalin kama ma kuwa."
cewar Ajmaal da Faisal.
Aunty tayi murmushi dan ko ba karya 'ya'yan asalin kama da uban su suke.
sai sannan suka masa bakin gado in da Feeryal ke kwance suka gaisheta suna yi mata ya jiki.
murmushi tayi musu tana lumshe idanunta tare da juya fuskarta ta jikin garo.
Daddy ya ce
"To mu fitan ku waje likita ya ce a barta ta huta, ku bawa Aunty'n ku yaran ta kwantar da su suma suna bukatar hutu."
suna shirin fita Hajiya da Goggo Bishira Ammah Miemie Kulu mai aikin Hajiya da Sumayya suka shigo.
Miemie kamar zatayi tsalle dan murna Sumayya ma haka, dan ita halinta da sauki dan wani lokaci bata d'aukar zugar Ameerah.
ko da suka fito zata biyo su Hajiya Ameerah ce mata tayi wai zataje kallon 'ya'yan aljanu ita ba inda zata.
ita Sumayya na son yaran tun bata gansu ba, tana ji a ranta ko ba komai dai 'ya'yan yayansu ne, dan bata daga cikin 'yan'uwan ta masu cewa ba cikin yayan nasu bane.
Miemie da Sumayya suka riga kowa d'aukar yaran.
da kyar goggo Bishira ta karb'i na hannun Sumayya dan Miemie kam ta rike na hannunta gam.
Hajiya ta leko fuskar su ta tana fad'in
"Eh to ga kamar abokin turawa a jikin su, ah to yanzu kam hankali zai kwanta."
Ammah ta girgiza kai.
Aunty ko Murmushi kawai tayi.
sai da likita ya shigo ya ce su bata guri ta huta kafin kowa ya fita aka bar Aunty da ita.
da zasu tafi Sumayya da Miemie suka ce su bazasu tafi ba,
suna tare da Aunty a asibitin.
Sumayya tana like da yaran da har cikin ranta take jin kaunarsu.
Aunty ta kira su Hajja Umma ta video call.
Abba da Hajja Umma sunyi matukar farinciki Aunty ta hasko musu yaran sunata yabawa da fatan Allah ya raya.
lokacin bacci ya d'auki Feeryal suka ce idan ta tashi zasu kira.
Aunty na kashewa ta kira Maryam, Maryam kamar zata fasa wayar da ihu
"Wai da gaske Aunty Faty Feeryal twin's ta haifa?."
cewar Maryam cike da zallar farinciki.
Aunty tayi dariya tana fad'in
"Gasu kuwa kina gani."
ta ce "Jibi ina hanya inasha'allah."
Aunty ta kashe tana mata dariya.