Sashe 45
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya ciro wayar ya buga shi da kasa, yana wani irin huci.
Mommy ta ce
"Abdulrahim ka nutsu dan Allah, kana yi musu irin wanan barazanar ai sai suki fad'in nawa suke bukata, suyi ta jan rai suki sakin ta,
a bisu a hankali yadda zasu fad'a da wuri a kai musu a karb'o ta."
ya juya a fusace yana taka kasa da karfi, ya shige mota.
Daddy ya biyo shi da sauri yana cewa
"Kar kaje kace zaka sanar wa hukuma, sai da sukayi min gargad'i a barsu a gani daga nan zuwa gobe."
ina kunnuwan sa sun toshe baya ma jin Daddy ya fige motar a guje kamar zai tashi sama.
a d'ari security suka bud'e mata get suka dare dan kad'an ya rage yayi ciki da su.
Ajmaal ya tatta wayar da tayi fisis.
Jikin kowa yayi sanyi Aunty kam sai hawaye, da ambaton sunan Allah.
wani kira ne ya shigo wayar Daddy, Ajmaal Zaraddin Shamsuddin Faisal suka dad'a matsowa kusa da shi duk zukatan su na d'ar-d'ar.
Daddy ya d'aga kiran yasa a handsfree daga cikin wayar aka ce.
"Ka gaya wa d'an ka gada yayi gigin sanarwa hukuma, ko ya ce zai ne mo mu, idan yayi d'aya cikin biyun nan zamu kasheta bayan mun gama abun da zamuyi da ita."
d'ip aka kashe kiran.
Mommy da Hajiya da Ammah sukayi salati.
Hajiya ta ce "Amma wad'an nan ba imani, Abubakar maza ka kirawo Abokin turawa ya dawo kada ya aikata abun da zai sa su kashe ta."
Abbieh da Dad suka d'aga waya suna rige-rigen kiran shi.
Ameerah Miemie Sumayya sai kuka.
Bilkisu Saddiqa Rahma Sahla ma sunyi jigum cike da jimami.
Abbieh da nashi wayar ya fara shiga ya yi ta ring bai d'aga ba.
ya kira yakai sau goma baya d'aga wa.
Ganin magriba ya karato Daddy ya ce kowa yaje ya yi sallah, a roki Allah.
Aunty tana sallah tana kuka, bayan tayi addu'a ta mike tsaye da kafafunta tana jiran shigowar Daddy.
Aunty ta kira Abba'n Abuja ta sanar masa,
hankalin su ya tashi matuka,
Abba ya ce
"Ko nawa suke bukata su fad'a za'a basu, zan bi jirgin karfe 6 na safe insha'allah zan shigo gobe."
jiki a sanyaye Aunty ta ce "To Allah ya kaimu."
har sai da akayi isha tana kan sallaya Daddy ya shigo.
tana ganin shi ta mike tana fad'in
"Daddy sun kuma kira sun fad'i nawa suke so? Abba ma ya ce zai zo gobe."
ya ce "Munyi waya da shi yanzu yace min zai gobe,
har yanzu basu kara kira ba amma Abdulrahim ya dawo yanzu, ya ce bai sanar wa hukuma ba,
dole yanzu mu jira su sake kira su fad'i in da za'a kai musu kud'in, da adadin kud'in da suke bukata."
Aunty ta zauna bakin gado jiki ba kwari tana fad'in
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un, ya Allah ka tsare ta kar ya barsu su cutar da ita."
hawaye ya zubo mata ta share.
Daddy ya fita yana amsa waya.
Yana tsaye a can saman upstairs yana rike da mug, dare ya tsala gidan yayi shiru amma hasken wuta ta ko ina tamkar rana.
kallo d'aya zakayi masa ka fahimci tsagwaran b'acin rai mai garwaye da damuwa.
a hankali yakai mug d'in bakin sa ya kurb'i sudan tea d'in ciki, kana ya saki mug d'in ya fad'o kasa ya tarwatse.
mai gadin dide d'in sa ya zabura daga gyangyad'in da yake kan kujera, jin karar fashewar abu.
ya d'aga kai da sauri ya hango sa tsaye daga can sama.
ogansa bai kwanta bacci lallai wad'an da sukayi garkuwa da ita basa da imani.
abun da mai gadin yayi ta fad'a cikin ransa ke nan.
Washegari da asuba bayan an idar da sallah.
duk mazan gidan suna masallaci.
malamai da yawa cikin masallacin Daddy yasa anata karatun kur'ani.
karfe 6 da 'yan mintuna Abban'an Abuja ya iso aka yi masa jagora cikin masallaci.
ana cikin gaisawa wayan Abdulrahim yayi kara, duk aka juyo gare sa.
Daddy ya ce
"Sune ko?."
"Su ne." ya fad'a yana d'aga kiran ya kai wayar kunnensa ba tare da yayi magana ba.
daga cikin wayar muryar da jiya ya masa magana shi ya sinkoayo shi yana fad'in
"Kamar fa tsoron barazanar da ka mana naji, yara sun so more kayan alatun nan na hana su, nima kuma ban tab'a ba,
amma mun barta tasha sanyi dan a tantagaryar kasa ta kwana sanyi na bugata."
ido ya rumtse ya bud'e sanda yaci gaba da fad'in
"Kasa a handsfree dan nasan tsoffin attajiran nan suna gurin."
a hankali ya zaro wayar yayi kamar yadda suka bukata.
"Idan kun shirya karb'arta ga abun da muke bukata,
muna bukatar billion d'ari biyar, daga nan zuwa yammacin rana, idan ba'a kawo mana ba zamu kashe ta bayan ko wannen mu ya mata fyad'a."
da sauri Abbieh ya ce
"Haba ku d'an rage mana billion d'ari biyar ai yayi yawa, kuyi hakuri ku dai fad'i dai-dai kima."
"Lale marhabin da zuwa Alhaji Tahir Abbas, lallai kuna ji da yarinyar nan tun da takanas babban bako ya taso daga Abuja ya zo Legos akan b'atar ta,
baza mu rage ko sisiba,
acikin ku waye bashi da fin kud'un da muka ambata,
Alhaji Tahir Abbas Alhaji Abubakar AA FIYA, Dr AA FIYA idan kun shirya zamu gaya muku inda zaku kawo kud'in ku karb'e ta,
idan ya wuce yammacin yau to tabbas zamu aikata abun da muka fad'a."
"Ina za'a kai muku!."
ya fad'a zuciya na tafarfasa.
"Da kyau mana Dr AA FIYA ka dakace mu zamu fad'a ma in da zaka kai, ka shirya kud'in."
suna kaiwa nan suka kashe wayar.
ya yi wani irin mikewa zuciya na tafarfasa.
Abba'n Abuja ya ce
"Ka dakata kafin banki su fito sai muje a cire musu kud'in."
Daddy ya ce
"Aa Alhaji ni zan bada kud'in, bari na rubuta check sai yaje ya karb'arba a banki."
"No akwai kud'i a kasa."
ya fad'a yana fita daga masallacin da sauri, suka bi bayan sa da kallo.
Da misalin karfe 2 na rana yana zaune cikin mota kirar Jeep Wrangler mai bakar gilashi, waya a rike a hannunsa yana sauraran kiran su, dan sun tabbatar masa da karfe 2 zasu kirashi ya kawo musu.
biyu da minni 3 kiransu ya shigo wayar sa, suka kwatanta masa in da zai je sannan suka ce kada ya sake ya zo da hukuma, sun rantse idan ya sab'a musu sai sun kashe ta.
"Ina mai tabbatar maka zamu kasheta bayan mun mata fyad'e kaca-kaca mun more wannan kyakkyawan surar, sai mun kasheta! idan kace zakayi mana wata dabarar."
ya d'auke ta da mari Feeryal ta fasa kara.
da karfi ya rumtse idanunsa karar marin da ihun ta yaki gushewa cikin kwakwalwa da kunnuwan sa.
ya bud'e rinannun idanuwan sa san da aka ci gaba da fad'in
"Fuska mai laushi kamar auduga wannan jiki a kwai dad'in tab'awa, idan ka b'ata lokaci komai zai iya faruwa dan ba karya wannan halitta na fisgata,
wata kila idan ka jinkirta ka samu na kwakule ta, idan ka dad'a b'ata lokaci yara su kwakule suma."
"Kaiii! ga kud'i na shirya maka cikin mota narantse idan kuka tab'a ta dukkanin ku bazan kyale ku ba, sai kun d'and'ani mutuwa!."
"Hahaha da kyau mana nafahimci tafasar zuciyar ka a kanta,
idan ka canza shirin abun da zai faru ke nan."
d'ip aka kashe wayar.
wani irin figar motar ya yi tamkar zai lula sararin samani ya.
Cikin kankanin lokaci ya kawo shi in da suka kwatan ta masa.
yana tsayuwa kira ya shigo wayarsa.
suka kuma fad'a masa ta in da zai bi, yakuma jan motar zuwa gurin.
sau uku suna fad'a masa ta in da zai bi, bayan ya iso in da suke bukata suka ce ya dakata a gurin.
"Ka fita a motar ta koma mashigar ka ta biyu ka jira a gurin za'a kawo maka ita,
dan har da motar muke bukata."
d'an jim yayi yana latsa computer motar, ya d'au wayoyin sa ya fita kamar yadda suka bukata, ya taka har mashigar da ya shigo na biyu ya tsaya a gurin.
suka ce ya baiwa in da yake kalla baya, ba musu ya juya bayan sa.
yana juyawa wayar hannunsa tayi dirrr yad'an matse wayar, yana daidaita tsayuwar sa.
Biyu daga cikin su suka fito daga mab'oyar su, d'aya na rike da bindiga,
suka zo gurin motar suna waige waige, mai bindigar ya bud'e motar yana saita bindigar cikin motar.
d'ayan da ba bingida a hannunsa ya shiga motar yana bud'e kwalayen da ya shirya kud'ad'en ciki, ya cika motar da su.
duk ya bubbud'e su yana zuba su har kasa.
kud'ad'e ne har kasa suka jinjinawa junan su, sannan suka koma mab'uyar su suka fito su da sauran 'yan uwan nasu da ita.
daga can mab'uyar su suka turo ta, suka ce ta mike nan.
kanta ba d'an kwali kafa ba takalmi tasa gudu tana waigen ganin ko zasu biyo ta.
gudu sosai ta ke tana haki, har ta b'ullo in da yake tsaye.
baya tayi da sauri tare da dafe kirji ta fasa kara tana toshe bakin ta, zaton ta su ne dan bayan sa ta gani.
da sauri ya juyo yana binta da kallo tare da mata alama da hannu tazo.
ta taho da gudu ta rungune shi, tare da fashewa da kuka.
hannun sa ya saka ya zagaye ta da shi yana dad'a matseta a jikinsa.
a hankali yayi sama da d'aya hannunsa,
yana shafa gashin kanta da yake baje a bayan ta.
yayin da idanunsa ke dad'a canza kala b'acin rai karar a kan fuskarsa, yana dad'a mannata da kijinsa, ya yin da zuciyar sa ke harbawa.
Da sauri da gudu-gudu suka karasa gurin motar,
in da direban taxi ya fito da taxi a inda suka b'oye sa, mutum hud'u suka shiga taxi mutum biyu kuma suka shiga mator da yazo da shi.
suna shirin barin gurin suka jiyo karar helicopter daga sama yana yin kasa-kasa aka fara bud'e musu wuta.
karar harbin ya sata birkicewa a kid'ime ta kankame shi, tana b'oye fuskarta a jikinsa.
ya dad'a rungume ta sosai.
Mommy ta ce
"Abdulrahim ka nutsu dan Allah, kana yi musu irin wanan barazanar ai sai suki fad'in nawa suke bukata, suyi ta jan rai suki sakin ta,
a bisu a hankali yadda zasu fad'a da wuri a kai musu a karb'o ta."
ya juya a fusace yana taka kasa da karfi, ya shige mota.
Daddy ya biyo shi da sauri yana cewa
"Kar kaje kace zaka sanar wa hukuma, sai da sukayi min gargad'i a barsu a gani daga nan zuwa gobe."
ina kunnuwan sa sun toshe baya ma jin Daddy ya fige motar a guje kamar zai tashi sama.
a d'ari security suka bud'e mata get suka dare dan kad'an ya rage yayi ciki da su.
Ajmaal ya tatta wayar da tayi fisis.
Jikin kowa yayi sanyi Aunty kam sai hawaye, da ambaton sunan Allah.
wani kira ne ya shigo wayar Daddy, Ajmaal Zaraddin Shamsuddin Faisal suka dad'a matsowa kusa da shi duk zukatan su na d'ar-d'ar.
Daddy ya d'aga kiran yasa a handsfree daga cikin wayar aka ce.
"Ka gaya wa d'an ka gada yayi gigin sanarwa hukuma, ko ya ce zai ne mo mu, idan yayi d'aya cikin biyun nan zamu kasheta bayan mun gama abun da zamuyi da ita."
d'ip aka kashe kiran.
Mommy da Hajiya da Ammah sukayi salati.
Hajiya ta ce "Amma wad'an nan ba imani, Abubakar maza ka kirawo Abokin turawa ya dawo kada ya aikata abun da zai sa su kashe ta."
Abbieh da Dad suka d'aga waya suna rige-rigen kiran shi.
Ameerah Miemie Sumayya sai kuka.
Bilkisu Saddiqa Rahma Sahla ma sunyi jigum cike da jimami.
Abbieh da nashi wayar ya fara shiga ya yi ta ring bai d'aga ba.
ya kira yakai sau goma baya d'aga wa.
Ganin magriba ya karato Daddy ya ce kowa yaje ya yi sallah, a roki Allah.
Aunty tana sallah tana kuka, bayan tayi addu'a ta mike tsaye da kafafunta tana jiran shigowar Daddy.
Aunty ta kira Abba'n Abuja ta sanar masa,
hankalin su ya tashi matuka,
Abba ya ce
"Ko nawa suke bukata su fad'a za'a basu, zan bi jirgin karfe 6 na safe insha'allah zan shigo gobe."
jiki a sanyaye Aunty ta ce "To Allah ya kaimu."
har sai da akayi isha tana kan sallaya Daddy ya shigo.
tana ganin shi ta mike tana fad'in
"Daddy sun kuma kira sun fad'i nawa suke so? Abba ma ya ce zai zo gobe."
ya ce "Munyi waya da shi yanzu yace min zai gobe,
har yanzu basu kara kira ba amma Abdulrahim ya dawo yanzu, ya ce bai sanar wa hukuma ba,
dole yanzu mu jira su sake kira su fad'i in da za'a kai musu kud'in, da adadin kud'in da suke bukata."
Aunty ta zauna bakin gado jiki ba kwari tana fad'in
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un, ya Allah ka tsare ta kar ya barsu su cutar da ita."
hawaye ya zubo mata ta share.
Daddy ya fita yana amsa waya.
Yana tsaye a can saman upstairs yana rike da mug, dare ya tsala gidan yayi shiru amma hasken wuta ta ko ina tamkar rana.
kallo d'aya zakayi masa ka fahimci tsagwaran b'acin rai mai garwaye da damuwa.
a hankali yakai mug d'in bakin sa ya kurb'i sudan tea d'in ciki, kana ya saki mug d'in ya fad'o kasa ya tarwatse.
mai gadin dide d'in sa ya zabura daga gyangyad'in da yake kan kujera, jin karar fashewar abu.
ya d'aga kai da sauri ya hango sa tsaye daga can sama.
ogansa bai kwanta bacci lallai wad'an da sukayi garkuwa da ita basa da imani.
abun da mai gadin yayi ta fad'a cikin ransa ke nan.
Washegari da asuba bayan an idar da sallah.
duk mazan gidan suna masallaci.
malamai da yawa cikin masallacin Daddy yasa anata karatun kur'ani.
karfe 6 da 'yan mintuna Abban'an Abuja ya iso aka yi masa jagora cikin masallaci.
ana cikin gaisawa wayan Abdulrahim yayi kara, duk aka juyo gare sa.
Daddy ya ce
"Sune ko?."
"Su ne." ya fad'a yana d'aga kiran ya kai wayar kunnensa ba tare da yayi magana ba.
daga cikin wayar muryar da jiya ya masa magana shi ya sinkoayo shi yana fad'in
"Kamar fa tsoron barazanar da ka mana naji, yara sun so more kayan alatun nan na hana su, nima kuma ban tab'a ba,
amma mun barta tasha sanyi dan a tantagaryar kasa ta kwana sanyi na bugata."
ido ya rumtse ya bud'e sanda yaci gaba da fad'in
"Kasa a handsfree dan nasan tsoffin attajiran nan suna gurin."
a hankali ya zaro wayar yayi kamar yadda suka bukata.
"Idan kun shirya karb'arta ga abun da muke bukata,
muna bukatar billion d'ari biyar, daga nan zuwa yammacin rana, idan ba'a kawo mana ba zamu kashe ta bayan ko wannen mu ya mata fyad'a."
da sauri Abbieh ya ce
"Haba ku d'an rage mana billion d'ari biyar ai yayi yawa, kuyi hakuri ku dai fad'i dai-dai kima."
"Lale marhabin da zuwa Alhaji Tahir Abbas, lallai kuna ji da yarinyar nan tun da takanas babban bako ya taso daga Abuja ya zo Legos akan b'atar ta,
baza mu rage ko sisiba,
acikin ku waye bashi da fin kud'un da muka ambata,
Alhaji Tahir Abbas Alhaji Abubakar AA FIYA, Dr AA FIYA idan kun shirya zamu gaya muku inda zaku kawo kud'in ku karb'e ta,
idan ya wuce yammacin yau to tabbas zamu aikata abun da muka fad'a."
"Ina za'a kai muku!."
ya fad'a zuciya na tafarfasa.
"Da kyau mana Dr AA FIYA ka dakace mu zamu fad'a ma in da zaka kai, ka shirya kud'in."
suna kaiwa nan suka kashe wayar.
ya yi wani irin mikewa zuciya na tafarfasa.
Abba'n Abuja ya ce
"Ka dakata kafin banki su fito sai muje a cire musu kud'in."
Daddy ya ce
"Aa Alhaji ni zan bada kud'in, bari na rubuta check sai yaje ya karb'arba a banki."
"No akwai kud'i a kasa."
ya fad'a yana fita daga masallacin da sauri, suka bi bayan sa da kallo.
Da misalin karfe 2 na rana yana zaune cikin mota kirar Jeep Wrangler mai bakar gilashi, waya a rike a hannunsa yana sauraran kiran su, dan sun tabbatar masa da karfe 2 zasu kirashi ya kawo musu.
biyu da minni 3 kiransu ya shigo wayar sa, suka kwatanta masa in da zai je sannan suka ce kada ya sake ya zo da hukuma, sun rantse idan ya sab'a musu sai sun kashe ta.
"Ina mai tabbatar maka zamu kasheta bayan mun mata fyad'e kaca-kaca mun more wannan kyakkyawan surar, sai mun kasheta! idan kace zakayi mana wata dabarar."
ya d'auke ta da mari Feeryal ta fasa kara.
da karfi ya rumtse idanunsa karar marin da ihun ta yaki gushewa cikin kwakwalwa da kunnuwan sa.
ya bud'e rinannun idanuwan sa san da aka ci gaba da fad'in
"Fuska mai laushi kamar auduga wannan jiki a kwai dad'in tab'awa, idan ka b'ata lokaci komai zai iya faruwa dan ba karya wannan halitta na fisgata,
wata kila idan ka jinkirta ka samu na kwakule ta, idan ka dad'a b'ata lokaci yara su kwakule suma."
"Kaiii! ga kud'i na shirya maka cikin mota narantse idan kuka tab'a ta dukkanin ku bazan kyale ku ba, sai kun d'and'ani mutuwa!."
"Hahaha da kyau mana nafahimci tafasar zuciyar ka a kanta,
idan ka canza shirin abun da zai faru ke nan."
d'ip aka kashe wayar.
wani irin figar motar ya yi tamkar zai lula sararin samani ya.
Cikin kankanin lokaci ya kawo shi in da suka kwatan ta masa.
yana tsayuwa kira ya shigo wayarsa.
suka kuma fad'a masa ta in da zai bi, yakuma jan motar zuwa gurin.
sau uku suna fad'a masa ta in da zai bi, bayan ya iso in da suke bukata suka ce ya dakata a gurin.
"Ka fita a motar ta koma mashigar ka ta biyu ka jira a gurin za'a kawo maka ita,
dan har da motar muke bukata."
d'an jim yayi yana latsa computer motar, ya d'au wayoyin sa ya fita kamar yadda suka bukata, ya taka har mashigar da ya shigo na biyu ya tsaya a gurin.
suka ce ya baiwa in da yake kalla baya, ba musu ya juya bayan sa.
yana juyawa wayar hannunsa tayi dirrr yad'an matse wayar, yana daidaita tsayuwar sa.
Biyu daga cikin su suka fito daga mab'oyar su, d'aya na rike da bindiga,
suka zo gurin motar suna waige waige, mai bindigar ya bud'e motar yana saita bindigar cikin motar.
d'ayan da ba bingida a hannunsa ya shiga motar yana bud'e kwalayen da ya shirya kud'ad'en ciki, ya cika motar da su.
duk ya bubbud'e su yana zuba su har kasa.
kud'ad'e ne har kasa suka jinjinawa junan su, sannan suka koma mab'uyar su suka fito su da sauran 'yan uwan nasu da ita.
daga can mab'uyar su suka turo ta, suka ce ta mike nan.
kanta ba d'an kwali kafa ba takalmi tasa gudu tana waigen ganin ko zasu biyo ta.
gudu sosai ta ke tana haki, har ta b'ullo in da yake tsaye.
baya tayi da sauri tare da dafe kirji ta fasa kara tana toshe bakin ta, zaton ta su ne dan bayan sa ta gani.
da sauri ya juyo yana binta da kallo tare da mata alama da hannu tazo.
ta taho da gudu ta rungune shi, tare da fashewa da kuka.
hannun sa ya saka ya zagaye ta da shi yana dad'a matseta a jikinsa.
a hankali yayi sama da d'aya hannunsa,
yana shafa gashin kanta da yake baje a bayan ta.
yayin da idanunsa ke dad'a canza kala b'acin rai karar a kan fuskarsa, yana dad'a mannata da kijinsa, ya yin da zuciyar sa ke harbawa.
Da sauri da gudu-gudu suka karasa gurin motar,
in da direban taxi ya fito da taxi a inda suka b'oye sa, mutum hud'u suka shiga taxi mutum biyu kuma suka shiga mator da yazo da shi.
suna shirin barin gurin suka jiyo karar helicopter daga sama yana yin kasa-kasa aka fara bud'e musu wuta.
karar harbin ya sata birkicewa a kid'ime ta kankame shi, tana b'oye fuskarta a jikinsa.
ya dad'a rungume ta sosai.