Sashe 40
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Bayan wani lokaci a ranar da mamarka zata haifi Ameerah, tare da ita akaje asibiti bayan tayi min tayin kud'i mai tsoka ta waya, ganin yawan kud'in yasani amincewa suna kawo ta asibitin ita da baban ku da kakarku, nayi rubutu na ce C'S za'a mata, kamar yadda Hajiya Karima ta bukata, bayan da kanta ma zata iya haihuwa na ce dole sai an mata C'S,
kamar yadda Hajiya Karima ta shirya.
babu b'ata lokaci mahaifin ka ya sa hannu aka shiga da ita.
bayan na ciro Ameerah sannan na cire mahaifar na damkawa Hajiya Karima, ta biyani kud'in da tayi min tayinsa.
ganin yawan kud'in yasa naji dad'i, har na kara ginin asibiti na da kud'in,
a cikin 'yan shekarun nan ma ta kuma nima na tana niman mahaifa yazo a sa'an zanyi wa wata C'S na cire na kai mata ta biyani.
shi ne da aka kai matarka haihuwa ta ce na cire mahaifar da yaran a ciki gaba d'aya,
kuma ai kazo kafin na cire ka sani dai ba ni na kashe maka yara ba mamarka ce ta kashesu,
kar ka kashe ni kayi hakuri dan Allah kar ka kashe ni."
d'ip TV ya d'auke ya dawo tashar da kowa ke kallo..
Mommy da ta mike tsaye jikinta na tsuma, tun san da Sumayya ta kunna mata TV har yanzu da TV ya d'auke.
wani irin suya gami da girgiza zuciyarta yake, lallai mutum a bin tsoro ne, wacce ta yarda da ita tabata dukkan yarda, ashe ita ce makashin ta.
lallai hausawa sunyi gaskiya makashin ka na tare da kai.
nannauyar numfashi Mommy ta sauke a fili ta furta
"Lallai Hajiya Karima kin jima kina zurma ni a rami, ban ankara ba har sai da kika ruftamin kasa a ka."
Wani irin zufa ne yake sassafowa Umma Karima, ta cire d'ankwalin kanta tana fifita.
"Bazan kyale ka ba Abdulrahim tun da ka tono asirin da ya dad'e a bisne."
Bilkisu Rahma Nabila duk suka juyo ga mahaifiyar tasu, ya yin da jikinsu ya yi matukar sanyi, gami da matukar jin mamakin abun da mamar tasu ta aikata.
Siyama ko hannu ta nad'e duk da tasan Aunty'n nata ma'abociyar ta'ammali da bokaye ne, amma batayi zaton abun nata yakai nan ba.
Bilkisu ta ce
"Umma me yasa zakiyi haka."
duk sauran 'yan'uwan nata ma kalar tambayar da sukayiwa uwar tasu ke nan.
Saddiqa data shigo da sauri ta ce
"Umma kowa a gidan nan ya kalli abun da ya faru, Umma ya zakiyi haka."
Nabila ta d'aura hannu a kai tana fad'in
"Mun shiga uku mu da gidan uban mu za'a rika mana gori da hantara, wanna tsintacciya Feeryal d'in shike nan ta sami abun mana gori itama,
shike nan muda gidan mu zata rika yimana kallon banza."
Rahama ta ce
"Wacce irin magana ce wannan Nabila ai abun da Umma ta aikata, shine abu mafi muni ba kallon da Feeryal ko mutane zasuyi mana ba,
idan Feeryal tayi mana kallon banza batayi laifi ba, dan mun aikata mata fiye da yadda zata mana."
Nabila ta yamutsa fuska tana fad'in
"Ko ma me Umma tayi wlh ni da gidan ubana bata isa tayi min kallon banza banci ubanta ba."
Bilkisu ta ce "Ki rufa mana baki Nabila, abun da Umma ta aikata abun kunya ne agare mu,
Umma baki kyauta ba."
Bilkisu bata rufa baki ba
Umma Karima ta juya ta shige d'aki tana fad'in
"Dole naje gurin boka yanzu yarufa min bakin kowa."
ta shiga tana kokarin d'aukar mayafinta
taji wani irin karar durowar abu da saida ilahirin side d'in ya girgiza, tamkar sama zai rusho ya afko kasa.
girgiza mai matukara ban tsoro da firgitarwa.
kafin ta dawo hayyacin ta daga sananin firgitan data shiga taji anyi sama da ita an buga da kasa.
wasu halittu masu ban tsoro suka bayyana wa ganin ta,
ya yin da
muryoyin su masu matukar bantsoro da firgitarwa suka karad'e jinta tamkar dodon kunnen ta zasu zazzago kasa.
idan kaji ana kuka ko ihu samin dama ce ga tashin hankalin da ka shiga,
idan tashin hankali yakai tashin hankali ihu ko kuka basa tab'a maraftarka.
yanayin ne ya kasance da Umma Karima wanda take fatan dama tayi ihun ko wani zai jita ya kawo mata d'auki,
dan tasan kiyamar ta ce ta tsaya.
saukar bulalu ta soma ji ta ko ina a jikinta, tamkar aska mai tsananin kaifi a ke tsastsaga jikinta da shi.
aka shiga tabaibayeta da sarkokin sarfe.
ya yin da muryoyin suka soma amsa kuwa cikin kunnuwanta.
"Yau sa'ar ki ta kare zaki karb'i hukunci mai tsanani daga fadar sarkin Aljanu,
ire-iren ki azzalumai sarkin aljanu ne yake yanke muku hukunci da kansa, a duk sanda kuka had'a kai da azzaluman jinnu kuna zaluntar bil'adama, ko jinnun da basu ci muku ba basu taka muku ba,
jeki ki bayyana kanki wa duk wanda kikayi wa zalunci,
kafin karb'ar hukuncin ki!!."
idanun Umma Karima suka firfito kamar zasu zazzago kasa.
ta yunkura da gudu tayi waje a gigice tana fad'uwa tana tashi cikin mawuyacin hali.
'ya'yan ta da suke tsaye cirko-cirko wan da firgicin girgizan da sukaji side d'in ya yi, kowa ya shiga niman hanyar guduwa waje.
ganin uwar tasu ta fito kamar an d'agota an jefo ta cikin parlour'n ta bugu da kasa.
ta kuma mikewa
ya yin da take jin saukar bulalun ta ko ina a jikinta.
'ya'ya nata sukayi kururuwa ganin halin da uwar tasu take ciki,
wan da basa iya ganin halittun,
sai dai azabar da take sha kad'ai ke bayyana a jikinta.
ta na tabaibaye da sarka
a haka ta nufi waje
idan ta fad'i sai tayi birgima a kasa ta gogo fuskarta da kasa jini ya fito kafin ta mike ta kuma fad'i a haka ta isa farfajiyar gidan.
inda 'ya'yan ta suka biyo ta a baya suna ihu.
Firgicin afkuwar lamarin ya sanya kowa na gidan fitowa farfajiyar gidan, har da Feeryal, da ta soma samin lafiya.
aka jefo Umma Karima tsakiyar mutanen gidan ta fad'i timm a kasa,
ta goga fuskarta da kasa ta d'ago baki na fita da jini, ta ke fad'in
"Ni karima ni na sa aka cire min mahaifar Hajiya Halima da Hajiya Fatima na kaiwa boka yayi min asiri da shi, dan na mallaki Alhaji,
da dukiyarsa baki d'aya, bayan na mallake shi nasa a kashe shi,
mahaifa uku boka ya ce na kawo, domin a kashe Alhaji,
mahaifa uku ya ce na saka cikin kaskon tsafi, na farko mahaifa mai d'auke da yara 'yan biyu da basu wuce wata uku cikin mahaifar ba,
na biyu mahaifar da babu komai cikin sa, na uku mahaifa masu d'auke da 'ya'yan da suka kai watanni tara,
a ranar farko dana saka mahaifar farko cikin kaskon tsafi,
a ranar ce Alhaji ya soma gamuwa da mugayen mafarkan da yasa masa ciwon zuciya,
bakaken aljanu suka soma bibiyarsa a mafarki domin hallakashi dan na mallaki dukiyarsa.
a ranar dana saka mahaifa na uku ana daf da kashe Alhaji na kirawo boka na a matsayin mai magani,
domin yazo ya karasa aikinsa, da ya shiga d'akin Alhaji, da ranar Alhaji bazai kwana a duniya ba,
Feeryal ta tare shi harta fasa kwaryar tsafin,
sanadin da aiki ya dawo baya,
boka ya ce sai na sake kawo wani mahaifar mai d'auke da yara biyu a cikin sa, kafin a karasa min aikin,
shine sanadin da nasa a ciro min 'ya'yan cikin Feeryal a cikin mahaifarsu, da likita ya tabbatar min da ya duba yaga biyu ne a cikin ta.
da ban yi sa'a ba nazuga Hajiya Halima ta je ta kashesu.
sanadin da yasa na aikata haka, ina bakin cikin da ni ban sami 'ya'ya maza ba, naso bayan na kashe Alhaji zan hallaka yaya mazan Hajiya Halima, sannan na mallake dukiyar Alhaji, tun da nasan idan ya mutu bani da gadon sa da yawa,
tun da a baya nayi ta kokarin ganin na sami d'a na miji ban
samu ba, har na ja direba na
muka soma had'a shinfid'a ko dan zan sami d'a na miji tare da shi, ina bashi kud'i domin
ya biya min bukata ko zan sami
cikin d'a na miji tare da shi,
amma akayi rashin sa'a na sami
cikin sai dai ba na mijin na haifa ba,
Nabila wannan ba 'yar Alhaji bane cikin da Sule direba ya yi min ne, a wani lokacin da Alhaji baya ma kasarnan,
nasan yadda nayi babu wanda ya gane bare a zarge ni,
har na haifi Nabila a matsayin 'yar Alhaji,
ban hakura ba bayan haihuwarta nayi ta kokarin ganin ko zan sami d'a na miji,
ina d'aukarsa muna fita hotel nayi ciki uku a bayan ta, ina zuwa asibiti a gwada idan akaga mace ce sai na sa a zubar,
daga baya na hakura na soma shirin d'aukar matakin na kashe Alhaji na kawar da 'ya'yan Hajiya Halima maza, dan na mallaki dukiyar Alhaji,
sai dai tun da Feeryal tazo gidan nan take bani matsala dan duk shirin da nayi dan cimma burina ita take rushewa,
ta b'ata min shiri, badun wanzuwan ta a gidan nan ba da yanzu ba wannan batun ake ba."
kamar yadda Hajiya Karima ta shirya.
babu b'ata lokaci mahaifin ka ya sa hannu aka shiga da ita.
bayan na ciro Ameerah sannan na cire mahaifar na damkawa Hajiya Karima, ta biyani kud'in da tayi min tayinsa.
ganin yawan kud'in yasa naji dad'i, har na kara ginin asibiti na da kud'in,
a cikin 'yan shekarun nan ma ta kuma nima na tana niman mahaifa yazo a sa'an zanyi wa wata C'S na cire na kai mata ta biyani.
shi ne da aka kai matarka haihuwa ta ce na cire mahaifar da yaran a ciki gaba d'aya,
kuma ai kazo kafin na cire ka sani dai ba ni na kashe maka yara ba mamarka ce ta kashesu,
kar ka kashe ni kayi hakuri dan Allah kar ka kashe ni."
d'ip TV ya d'auke ya dawo tashar da kowa ke kallo..
Mommy da ta mike tsaye jikinta na tsuma, tun san da Sumayya ta kunna mata TV har yanzu da TV ya d'auke.
wani irin suya gami da girgiza zuciyarta yake, lallai mutum a bin tsoro ne, wacce ta yarda da ita tabata dukkan yarda, ashe ita ce makashin ta.
lallai hausawa sunyi gaskiya makashin ka na tare da kai.
nannauyar numfashi Mommy ta sauke a fili ta furta
"Lallai Hajiya Karima kin jima kina zurma ni a rami, ban ankara ba har sai da kika ruftamin kasa a ka."
Wani irin zufa ne yake sassafowa Umma Karima, ta cire d'ankwalin kanta tana fifita.
"Bazan kyale ka ba Abdulrahim tun da ka tono asirin da ya dad'e a bisne."
Bilkisu Rahma Nabila duk suka juyo ga mahaifiyar tasu, ya yin da jikinsu ya yi matukar sanyi, gami da matukar jin mamakin abun da mamar tasu ta aikata.
Siyama ko hannu ta nad'e duk da tasan Aunty'n nata ma'abociyar ta'ammali da bokaye ne, amma batayi zaton abun nata yakai nan ba.
Bilkisu ta ce
"Umma me yasa zakiyi haka."
duk sauran 'yan'uwan nata ma kalar tambayar da sukayiwa uwar tasu ke nan.
Saddiqa data shigo da sauri ta ce
"Umma kowa a gidan nan ya kalli abun da ya faru, Umma ya zakiyi haka."
Nabila ta d'aura hannu a kai tana fad'in
"Mun shiga uku mu da gidan uban mu za'a rika mana gori da hantara, wanna tsintacciya Feeryal d'in shike nan ta sami abun mana gori itama,
shike nan muda gidan mu zata rika yimana kallon banza."
Rahama ta ce
"Wacce irin magana ce wannan Nabila ai abun da Umma ta aikata, shine abu mafi muni ba kallon da Feeryal ko mutane zasuyi mana ba,
idan Feeryal tayi mana kallon banza batayi laifi ba, dan mun aikata mata fiye da yadda zata mana."
Nabila ta yamutsa fuska tana fad'in
"Ko ma me Umma tayi wlh ni da gidan ubana bata isa tayi min kallon banza banci ubanta ba."
Bilkisu ta ce "Ki rufa mana baki Nabila, abun da Umma ta aikata abun kunya ne agare mu,
Umma baki kyauta ba."
Bilkisu bata rufa baki ba
Umma Karima ta juya ta shige d'aki tana fad'in
"Dole naje gurin boka yanzu yarufa min bakin kowa."
ta shiga tana kokarin d'aukar mayafinta
taji wani irin karar durowar abu da saida ilahirin side d'in ya girgiza, tamkar sama zai rusho ya afko kasa.
girgiza mai matukara ban tsoro da firgitarwa.
kafin ta dawo hayyacin ta daga sananin firgitan data shiga taji anyi sama da ita an buga da kasa.
wasu halittu masu ban tsoro suka bayyana wa ganin ta,
ya yin da
muryoyin su masu matukar bantsoro da firgitarwa suka karad'e jinta tamkar dodon kunnen ta zasu zazzago kasa.
idan kaji ana kuka ko ihu samin dama ce ga tashin hankalin da ka shiga,
idan tashin hankali yakai tashin hankali ihu ko kuka basa tab'a maraftarka.
yanayin ne ya kasance da Umma Karima wanda take fatan dama tayi ihun ko wani zai jita ya kawo mata d'auki,
dan tasan kiyamar ta ce ta tsaya.
saukar bulalu ta soma ji ta ko ina a jikinta, tamkar aska mai tsananin kaifi a ke tsastsaga jikinta da shi.
aka shiga tabaibayeta da sarkokin sarfe.
ya yin da muryoyin suka soma amsa kuwa cikin kunnuwanta.
"Yau sa'ar ki ta kare zaki karb'i hukunci mai tsanani daga fadar sarkin Aljanu,
ire-iren ki azzalumai sarkin aljanu ne yake yanke muku hukunci da kansa, a duk sanda kuka had'a kai da azzaluman jinnu kuna zaluntar bil'adama, ko jinnun da basu ci muku ba basu taka muku ba,
jeki ki bayyana kanki wa duk wanda kikayi wa zalunci,
kafin karb'ar hukuncin ki!!."
idanun Umma Karima suka firfito kamar zasu zazzago kasa.
ta yunkura da gudu tayi waje a gigice tana fad'uwa tana tashi cikin mawuyacin hali.
'ya'yan ta da suke tsaye cirko-cirko wan da firgicin girgizan da sukaji side d'in ya yi, kowa ya shiga niman hanyar guduwa waje.
ganin uwar tasu ta fito kamar an d'agota an jefo ta cikin parlour'n ta bugu da kasa.
ta kuma mikewa
ya yin da take jin saukar bulalun ta ko ina a jikinta.
'ya'ya nata sukayi kururuwa ganin halin da uwar tasu take ciki,
wan da basa iya ganin halittun,
sai dai azabar da take sha kad'ai ke bayyana a jikinta.
ta na tabaibaye da sarka
a haka ta nufi waje
idan ta fad'i sai tayi birgima a kasa ta gogo fuskarta da kasa jini ya fito kafin ta mike ta kuma fad'i a haka ta isa farfajiyar gidan.
inda 'ya'yan ta suka biyo ta a baya suna ihu.
Firgicin afkuwar lamarin ya sanya kowa na gidan fitowa farfajiyar gidan, har da Feeryal, da ta soma samin lafiya.
aka jefo Umma Karima tsakiyar mutanen gidan ta fad'i timm a kasa,
ta goga fuskarta da kasa ta d'ago baki na fita da jini, ta ke fad'in
"Ni karima ni na sa aka cire min mahaifar Hajiya Halima da Hajiya Fatima na kaiwa boka yayi min asiri da shi, dan na mallaki Alhaji,
da dukiyarsa baki d'aya, bayan na mallake shi nasa a kashe shi,
mahaifa uku boka ya ce na kawo, domin a kashe Alhaji,
mahaifa uku ya ce na saka cikin kaskon tsafi, na farko mahaifa mai d'auke da yara 'yan biyu da basu wuce wata uku cikin mahaifar ba,
na biyu mahaifar da babu komai cikin sa, na uku mahaifa masu d'auke da 'ya'yan da suka kai watanni tara,
a ranar farko dana saka mahaifar farko cikin kaskon tsafi,
a ranar ce Alhaji ya soma gamuwa da mugayen mafarkan da yasa masa ciwon zuciya,
bakaken aljanu suka soma bibiyarsa a mafarki domin hallakashi dan na mallaki dukiyarsa.
a ranar dana saka mahaifa na uku ana daf da kashe Alhaji na kirawo boka na a matsayin mai magani,
domin yazo ya karasa aikinsa, da ya shiga d'akin Alhaji, da ranar Alhaji bazai kwana a duniya ba,
Feeryal ta tare shi harta fasa kwaryar tsafin,
sanadin da aiki ya dawo baya,
boka ya ce sai na sake kawo wani mahaifar mai d'auke da yara biyu a cikin sa, kafin a karasa min aikin,
shine sanadin da nasa a ciro min 'ya'yan cikin Feeryal a cikin mahaifarsu, da likita ya tabbatar min da ya duba yaga biyu ne a cikin ta.
da ban yi sa'a ba nazuga Hajiya Halima ta je ta kashesu.
sanadin da yasa na aikata haka, ina bakin cikin da ni ban sami 'ya'ya maza ba, naso bayan na kashe Alhaji zan hallaka yaya mazan Hajiya Halima, sannan na mallake dukiyar Alhaji, tun da nasan idan ya mutu bani da gadon sa da yawa,
tun da a baya nayi ta kokarin ganin na sami d'a na miji ban
samu ba, har na ja direba na
muka soma had'a shinfid'a ko dan zan sami d'a na miji tare da shi, ina bashi kud'i domin
ya biya min bukata ko zan sami
cikin d'a na miji tare da shi,
amma akayi rashin sa'a na sami
cikin sai dai ba na mijin na haifa ba,
Nabila wannan ba 'yar Alhaji bane cikin da Sule direba ya yi min ne, a wani lokacin da Alhaji baya ma kasarnan,
nasan yadda nayi babu wanda ya gane bare a zarge ni,
har na haifi Nabila a matsayin 'yar Alhaji,
ban hakura ba bayan haihuwarta nayi ta kokarin ganin ko zan sami d'a na miji,
ina d'aukarsa muna fita hotel nayi ciki uku a bayan ta, ina zuwa asibiti a gwada idan akaga mace ce sai na sa a zubar,
daga baya na hakura na soma shirin d'aukar matakin na kashe Alhaji na kawar da 'ya'yan Hajiya Halima maza, dan na mallaki dukiyar Alhaji,
sai dai tun da Feeryal tazo gidan nan take bani matsala dan duk shirin da nayi dan cimma burina ita take rushewa,
ta b'ata min shiri, badun wanzuwan ta a gidan nan ba da yanzu ba wannan batun ake ba."