Sashe 14
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A kusa da sashin Hajiya Ajmaal ya iso shi suka shige sashin nata tare.
in da su Faisal kuma suka nufi b'angare iyayen su.
Hajiya na zaune a parlour suka karaso sai da ya fara zama kafin Ajmaal ya zauna.
Hajiya ta bishi da kallo tana fad'in
"Wai kai kam abokin turawa ko yaushe zaka sauya oho, kullum ya kullum fuska turnuke ba'a gane farincinka;
ko da yake iyayen ka su suka ja maka, kai kuma gaka mai jin maganar iyaye, bazaka iya tuburewa kace ba haka ba,
sai an karka da ranka anga bayanka,
ko d'iyar sarkin aljanu aka aurama zaka aminta,
bazakayi musuba duk rashin adalcin da aka maka haka zaka d'auke shi ka aza a kanka,
ba garama uwar taka mutum ta zab'a maka ba, shiko uban ka d'iyar ifiritu ya aura maka,
ina zaka sami farin ciki,
ai saukin ka d'aya ka fito da matar da kake so ni muka nasa dole uban ka ya aura maka ita."
Ajmaal ya ce
"Ke Hajiya daga shigowar mutum ko gaisawa ba'ayi ba, kibi ki ishe shi da magana, ai ke ma haka su Daddy suke yi miki biyayya, ke nan shi so kike ya bijire yaki yi masa biyayya,
dan Allah kibar mutane su huta."
"To dun uban ka bazan bar mutanen su huta ba, rashin hutu na nawa kuma, yawuce wan da ubanku ya d'aura masa, ai nan gaba sarauniyar aljanu zai kuma aura masa, iya shegen banza a hanani magana ga abun maganar,
kai ma in baka maida hankali ba jinnun za'a had'a ka da ita, duk ku taru kuyita kumburi kuna cika kuna batsewa kamar kububuwa." Jamal
"Idan ba a suffar aljanun zasu zo ba me zai hana mu iya zama da su, biyayya ga iyaye kuma ai wajibine, haba ki barmu haka mu huta ko mu tafi mu fasa gaisuwar."
"Yo ku tafin mana mai mugun baki, ana fad'i tashi a kanku idan aka barku da aljanun zaku iya ne."
"Me zai hanamu iyawa da su, a barmu da su d'in kawai."
Hajiya ta harare shi tana kai loman nama bakin ta.
Ajmaal ya ce "Ke dai kici namar ki, bama Ya Abdulrahim ya ce ba kowani irin nama zaki rika ci ba, kuma ba kullum zaki rika ci ba, amma kullum duk sanda za'a ganki da kwanon nama a gaban ki."
"Yo in ban da abokin turawa ma ai nama kara lafiya yake."
cewar Hajiya tana kai loman nama bakin ta.
"In ji wa? shi likita ya gaya miki kice ba haka ba."
Ajmaal yayi maganar yana rike hab'a.
Hajiya tace
"Ko d'azu ma sai da nasa Kulu ta kamo min tashar da ake saka shirin, haka matar take cin nama kuma da bakin ta tace nama lafiya yake karawa,
itama likita ne yagaya mata."
"Hajiya in ban da abun ki shirin film gaskiya ne, ai ba komai ne ake fad'ar sa kuma ka samu da gaske ne hakan ba, shirin film ne kawai, gara dai ki kiyaye, kafin ki kasa iya tafiya."
da sauri ta ware ido ta dubi Abdulrahim ta ce
"Abokin turawa ba wani da yawa nake ci ba, sai nafi sati banci ba, ai bazai zamo illa ba ko."
Ajmaal ya yi dariya
"Hajiya anji batu kan lafiyar jiki, ba'a kaunar lafiya ta tab'o, to ai sai ki rika kiyaye wa."
mikewa Abdulrahim yayi cike da kosawa da surutun nasu, yanufi kofar fita.
Hajiya ta bud'e murya tana fad'in
"Kai abokin turawa tafiya ma zakayi, ina tambayar ka bazaka bani amsa ba."
bai ko juyo ba yayi gaba abinsa.
ta kalli Ajmaal tana fad'in
"Kaga wannan d'an'uwan naka ban tab'a ganin mara alkibla irin sa ba, bazaka tab'a gane me ya dosa ba,
dan Allah kaje ka tambaya min shi ka gano min bazan kasa iya tafiya nan gaba bako."
Ajmaal ya mike yana dariya gaba d'aya Hajiya ta rud'e, in dai lafiya ce ba'a kaunar ya tab'o..
Bayan sallan la'asar Feeryal ta foto zata shiga kitchen.
Kuraiba ta shigo tana yi mata kallon sama da kasa.
Feeryal taja ta tsaya a kofar kitchen.
Kuraiba tashiga karewa parlour'n kallo tana takowa gami da wasa mata harara.
tana kuma fad'in
"Sati guda dama na d'iba naga wani irin shiri kika shigo da shi, sai kuma naga akasin haka ashe ma fanko ne."
ta sheke da dariya ta tafa hannu kana ta ci gaba da fad'in
"Sai gashi har kwanin ki goma yau da tare wa, ban tab'a ganin yakai minti 10 da ke ba,
kash ayya ashe dai duk buge ne sorry fa."
d'akunan cikin parlour'n tashiga bud'e wa tana lekawa sai da ta leka duka d'akunan hud'u, ko ina har kitchen da store kana ta fito tana tafa hannu da fad'in
"Da kyau mana ko ni da akasan waye ubana kayan d'aki na bai kai wannan ba, sai ke da ba'a san asalinki ba, wai wannan shine duka kayanki,
saboda karya, ko da shike aiki da asiri meye baza'a iya ba."
Feeryal na tsaye tana kallon ta bata tanka mata ba.
ta tako gabanta ta dafa kafad'arta, tayi mata wani kallo tare da yamutsa fuska sannan ta saki dariyar makirci ta ce
"Laa karki damu da wannan fa ai ke kanwata ta ce tun da muna auren miji d'aya ai munza 'yan uwa, duk mun zamo abu guda, naga cucumber a cikin d'in nan naki bari na d'auka amma fa babba zan d'auka,
kin san laulayin ciki tun da yayi min cikin nan bani da abincin ci sai cucumber."
ta shiga kitchen d'in ta zab'o babba ta fito ta d'aga mata hannu ta ce
"Bye."
Feeryal na tsaye har sai da taga ficewar ta kafin ta shige kitchen.
Dad ne ya shigo side d'in sa yana kwalawa Mom kira.
da sauri ta fito jin kiran da
yake kwad'a mata.
ya dube ta yana fad'in
"Kin gani yaron nan Zaraddin
bai kwana a gida ba, yana so ya jamin abun magana, gashi Yaya Abubakar ya tare ni yana
tambaya ta ina yaje bai kwana a gida ba?."
Mom ta yamutsa fuska ta ce
"Sai kace an mai da Zaraddin d'in d'an tayi da beyi kwana
d'aya a gida ba, a taru ayi ta magana, ansan matasa da wannan
yanzu haka suna tare da
abokansa ne, zaka samu gidan
wani abokin sa yaje ya kwana,
wannan ai ba sabon abu bane a gun matasa, aje gidan aboki a
kwana, haba dan Allah duk kabi ka tada hankalin ka kawai daga
ya yi magana."
Dad ya zauna yana fad'in
"Wannan yaro duk abun da zan
fad'a masa bazai ji ba,
ya natsu yajira lokacin da
komai zai dawo karkashin ikon
mu in yaso duk abunda zaiyi ya yi amma ya tsaya dole sai ya b'ata min shiri, zamu gamu da shi bazai dawo ba duk in da
yaje ai zai dawo ai,
wai yaron nan shaye-shayen
nasa yakai har da giya yake
shigowa gidan nan."
Mom ta ce
"Narasa me Zaraddin ya tsare
wa mutane ayi ta maganar shi
kamar shine kad'ai mai abun
fad'a, ni dai kar a tambad'a
min yaro da mugun baki."
Mom tayi ta surutai da
zage-zage.
Feeryal ne tsaye cikin
parlour'n ta tana gyara shi.
da sauri ta waigo jin an turo
kofa.
Kuraiba ce ta shigo tana wani taku ta iso cikin parlour'n.
ta zube kan kujera tare da fad'i
"Wash Allah wlh na gaji."
sai kuma ta kalli Feeryal ta ce
"Barka dai amarya ana ta gyara ne haka, wlh duk a gajiye nake daren jiya ko rumtswa Mijin
Kuraiba bai barni nayi ba, oh
sorry Abdulrahim mai gidan namu, tun d'azu naso shigowa
mud'an yi hira baccin gajiya
ya kamani dole na kwanta,
to ykk."
tageren murmushi tayi sannan
ta ce
"Lafiya lau."
Kuraiba ta mike tana cewa
"Um bari na barki kiyi aikin
ki zan shigo muyi hira sanda
bakya komai."
a bakin kofa sukayi kiliya da
Miemie zata shigo.
kallon banza Miemie tayi mata
kamar yadda itama Kuraiba tayi
mata.
Miemie ta karaso ciki da sauri, ta harari Feeryal ta
ce
"Me wannan tazo yi a nan?."
Feeryal ta ce "Nima ban sani
ba yanzu shigowar ta kuma ta
fita, amma dai ce min tayi hira taso muyi bacci ya kamata
bata zo ba sai yanzu, amma gobe zata zo."
a hatsale Miemie ta ce
"Wannan ba karamar munafuka
bace, ni haka kawai bana son
ta, idan kika sake mata sai
tayi shanya a kanki."
Feeryal ta ce "Ni ina ruwana ma da ita, Ammie na ta ce kar
na sake nashiga sabgarta,
zauna Miemie dan Allah kar ki tafi yanzu."
"Ke ni yanzu zan tafi dama nazo nuna miki ashoben Yaya Yusuf ne,
Daddy ya
bada kud'i a yi mana odan kayan, dukan mu har da ke."
baki Feeryal ta washe tana kallon kayan a wayar Miemie ta ce
"Ai kuwa sunyi kyau."
"Idan ya iso zan kai mana
gurin d'inki, yanzu zanje wa Ammah aika ne direban ta na
jirana."
tayi waje da sauri..
Yusuf d'an yayan Mommy ne da suke ciki d'aya, wanda suke kira da Kawu Sani.
Kawu Sani shine babban d'an Bappa Salihu, yana zaune da iyalansa a Yelwa.
Yusuf shine babban d'an Kawu Sani, shi yana da zama a cikin garin Jos in da gidan sa da gun aikin sa yake can cikin garin Jos.
Daddy ne zai karb'a masa aure a nan Lagos za'ayi bikin.
matar anan cikin Lagos take,
bayan an gama biki zasu koma Jos.
biki na saura sati jama'an Yelwan Shendam suka taho.
in da shima tuni ango Yusuf yana nan.
Ana saura kwana uku bikin Miemie ta karb'o musu d'inkin su. a parlour suka baje kayan Feeryal tana ta yaba kyan d'inkin.
bayan fitar Miemie Feeryal ta mike zata koma d'aki, ya shigo
rike da waya a kunnen sa, sai da ya wuce dinning kafin ta shige d'aki. wayan sa data gani ranar a d'akinta ta d'auko ta fito,
dai-dai lokacin da yazo zai wuce rike da karamar flask mai d'auke da Sudan tea a ciki.
ta moko masa wayar
a hankali cikin muryarta mai sanyi ta ce "Ga wayar ka......!
in da su Faisal kuma suka nufi b'angare iyayen su.
Hajiya na zaune a parlour suka karaso sai da ya fara zama kafin Ajmaal ya zauna.
Hajiya ta bishi da kallo tana fad'in
"Wai kai kam abokin turawa ko yaushe zaka sauya oho, kullum ya kullum fuska turnuke ba'a gane farincinka;
ko da yake iyayen ka su suka ja maka, kai kuma gaka mai jin maganar iyaye, bazaka iya tuburewa kace ba haka ba,
sai an karka da ranka anga bayanka,
ko d'iyar sarkin aljanu aka aurama zaka aminta,
bazakayi musuba duk rashin adalcin da aka maka haka zaka d'auke shi ka aza a kanka,
ba garama uwar taka mutum ta zab'a maka ba, shiko uban ka d'iyar ifiritu ya aura maka,
ina zaka sami farin ciki,
ai saukin ka d'aya ka fito da matar da kake so ni muka nasa dole uban ka ya aura maka ita."
Ajmaal ya ce
"Ke Hajiya daga shigowar mutum ko gaisawa ba'ayi ba, kibi ki ishe shi da magana, ai ke ma haka su Daddy suke yi miki biyayya, ke nan shi so kike ya bijire yaki yi masa biyayya,
dan Allah kibar mutane su huta."
"To dun uban ka bazan bar mutanen su huta ba, rashin hutu na nawa kuma, yawuce wan da ubanku ya d'aura masa, ai nan gaba sarauniyar aljanu zai kuma aura masa, iya shegen banza a hanani magana ga abun maganar,
kai ma in baka maida hankali ba jinnun za'a had'a ka da ita, duk ku taru kuyita kumburi kuna cika kuna batsewa kamar kububuwa." Jamal
"Idan ba a suffar aljanun zasu zo ba me zai hana mu iya zama da su, biyayya ga iyaye kuma ai wajibine, haba ki barmu haka mu huta ko mu tafi mu fasa gaisuwar."
"Yo ku tafin mana mai mugun baki, ana fad'i tashi a kanku idan aka barku da aljanun zaku iya ne."
"Me zai hanamu iyawa da su, a barmu da su d'in kawai."
Hajiya ta harare shi tana kai loman nama bakin ta.
Ajmaal ya ce "Ke dai kici namar ki, bama Ya Abdulrahim ya ce ba kowani irin nama zaki rika ci ba, kuma ba kullum zaki rika ci ba, amma kullum duk sanda za'a ganki da kwanon nama a gaban ki."
"Yo in ban da abokin turawa ma ai nama kara lafiya yake."
cewar Hajiya tana kai loman nama bakin ta.
"In ji wa? shi likita ya gaya miki kice ba haka ba."
Ajmaal yayi maganar yana rike hab'a.
Hajiya tace
"Ko d'azu ma sai da nasa Kulu ta kamo min tashar da ake saka shirin, haka matar take cin nama kuma da bakin ta tace nama lafiya yake karawa,
itama likita ne yagaya mata."
"Hajiya in ban da abun ki shirin film gaskiya ne, ai ba komai ne ake fad'ar sa kuma ka samu da gaske ne hakan ba, shirin film ne kawai, gara dai ki kiyaye, kafin ki kasa iya tafiya."
da sauri ta ware ido ta dubi Abdulrahim ta ce
"Abokin turawa ba wani da yawa nake ci ba, sai nafi sati banci ba, ai bazai zamo illa ba ko."
Ajmaal ya yi dariya
"Hajiya anji batu kan lafiyar jiki, ba'a kaunar lafiya ta tab'o, to ai sai ki rika kiyaye wa."
mikewa Abdulrahim yayi cike da kosawa da surutun nasu, yanufi kofar fita.
Hajiya ta bud'e murya tana fad'in
"Kai abokin turawa tafiya ma zakayi, ina tambayar ka bazaka bani amsa ba."
bai ko juyo ba yayi gaba abinsa.
ta kalli Ajmaal tana fad'in
"Kaga wannan d'an'uwan naka ban tab'a ganin mara alkibla irin sa ba, bazaka tab'a gane me ya dosa ba,
dan Allah kaje ka tambaya min shi ka gano min bazan kasa iya tafiya nan gaba bako."
Ajmaal ya mike yana dariya gaba d'aya Hajiya ta rud'e, in dai lafiya ce ba'a kaunar ya tab'o..
Bayan sallan la'asar Feeryal ta foto zata shiga kitchen.
Kuraiba ta shigo tana yi mata kallon sama da kasa.
Feeryal taja ta tsaya a kofar kitchen.
Kuraiba tashiga karewa parlour'n kallo tana takowa gami da wasa mata harara.
tana kuma fad'in
"Sati guda dama na d'iba naga wani irin shiri kika shigo da shi, sai kuma naga akasin haka ashe ma fanko ne."
ta sheke da dariya ta tafa hannu kana ta ci gaba da fad'in
"Sai gashi har kwanin ki goma yau da tare wa, ban tab'a ganin yakai minti 10 da ke ba,
kash ayya ashe dai duk buge ne sorry fa."
d'akunan cikin parlour'n tashiga bud'e wa tana lekawa sai da ta leka duka d'akunan hud'u, ko ina har kitchen da store kana ta fito tana tafa hannu da fad'in
"Da kyau mana ko ni da akasan waye ubana kayan d'aki na bai kai wannan ba, sai ke da ba'a san asalinki ba, wai wannan shine duka kayanki,
saboda karya, ko da shike aiki da asiri meye baza'a iya ba."
Feeryal na tsaye tana kallon ta bata tanka mata ba.
ta tako gabanta ta dafa kafad'arta, tayi mata wani kallo tare da yamutsa fuska sannan ta saki dariyar makirci ta ce
"Laa karki damu da wannan fa ai ke kanwata ta ce tun da muna auren miji d'aya ai munza 'yan uwa, duk mun zamo abu guda, naga cucumber a cikin d'in nan naki bari na d'auka amma fa babba zan d'auka,
kin san laulayin ciki tun da yayi min cikin nan bani da abincin ci sai cucumber."
ta shiga kitchen d'in ta zab'o babba ta fito ta d'aga mata hannu ta ce
"Bye."
Feeryal na tsaye har sai da taga ficewar ta kafin ta shige kitchen.
Dad ne ya shigo side d'in sa yana kwalawa Mom kira.
da sauri ta fito jin kiran da
yake kwad'a mata.
ya dube ta yana fad'in
"Kin gani yaron nan Zaraddin
bai kwana a gida ba, yana so ya jamin abun magana, gashi Yaya Abubakar ya tare ni yana
tambaya ta ina yaje bai kwana a gida ba?."
Mom ta yamutsa fuska ta ce
"Sai kace an mai da Zaraddin d'in d'an tayi da beyi kwana
d'aya a gida ba, a taru ayi ta magana, ansan matasa da wannan
yanzu haka suna tare da
abokansa ne, zaka samu gidan
wani abokin sa yaje ya kwana,
wannan ai ba sabon abu bane a gun matasa, aje gidan aboki a
kwana, haba dan Allah duk kabi ka tada hankalin ka kawai daga
ya yi magana."
Dad ya zauna yana fad'in
"Wannan yaro duk abun da zan
fad'a masa bazai ji ba,
ya natsu yajira lokacin da
komai zai dawo karkashin ikon
mu in yaso duk abunda zaiyi ya yi amma ya tsaya dole sai ya b'ata min shiri, zamu gamu da shi bazai dawo ba duk in da
yaje ai zai dawo ai,
wai yaron nan shaye-shayen
nasa yakai har da giya yake
shigowa gidan nan."
Mom ta ce
"Narasa me Zaraddin ya tsare
wa mutane ayi ta maganar shi
kamar shine kad'ai mai abun
fad'a, ni dai kar a tambad'a
min yaro da mugun baki."
Mom tayi ta surutai da
zage-zage.
Feeryal ne tsaye cikin
parlour'n ta tana gyara shi.
da sauri ta waigo jin an turo
kofa.
Kuraiba ce ta shigo tana wani taku ta iso cikin parlour'n.
ta zube kan kujera tare da fad'i
"Wash Allah wlh na gaji."
sai kuma ta kalli Feeryal ta ce
"Barka dai amarya ana ta gyara ne haka, wlh duk a gajiye nake daren jiya ko rumtswa Mijin
Kuraiba bai barni nayi ba, oh
sorry Abdulrahim mai gidan namu, tun d'azu naso shigowa
mud'an yi hira baccin gajiya
ya kamani dole na kwanta,
to ykk."
tageren murmushi tayi sannan
ta ce
"Lafiya lau."
Kuraiba ta mike tana cewa
"Um bari na barki kiyi aikin
ki zan shigo muyi hira sanda
bakya komai."
a bakin kofa sukayi kiliya da
Miemie zata shigo.
kallon banza Miemie tayi mata
kamar yadda itama Kuraiba tayi
mata.
Miemie ta karaso ciki da sauri, ta harari Feeryal ta
ce
"Me wannan tazo yi a nan?."
Feeryal ta ce "Nima ban sani
ba yanzu shigowar ta kuma ta
fita, amma dai ce min tayi hira taso muyi bacci ya kamata
bata zo ba sai yanzu, amma gobe zata zo."
a hatsale Miemie ta ce
"Wannan ba karamar munafuka
bace, ni haka kawai bana son
ta, idan kika sake mata sai
tayi shanya a kanki."
Feeryal ta ce "Ni ina ruwana ma da ita, Ammie na ta ce kar
na sake nashiga sabgarta,
zauna Miemie dan Allah kar ki tafi yanzu."
"Ke ni yanzu zan tafi dama nazo nuna miki ashoben Yaya Yusuf ne,
Daddy ya
bada kud'i a yi mana odan kayan, dukan mu har da ke."
baki Feeryal ta washe tana kallon kayan a wayar Miemie ta ce
"Ai kuwa sunyi kyau."
"Idan ya iso zan kai mana
gurin d'inki, yanzu zanje wa Ammah aika ne direban ta na
jirana."
tayi waje da sauri..
Yusuf d'an yayan Mommy ne da suke ciki d'aya, wanda suke kira da Kawu Sani.
Kawu Sani shine babban d'an Bappa Salihu, yana zaune da iyalansa a Yelwa.
Yusuf shine babban d'an Kawu Sani, shi yana da zama a cikin garin Jos in da gidan sa da gun aikin sa yake can cikin garin Jos.
Daddy ne zai karb'a masa aure a nan Lagos za'ayi bikin.
matar anan cikin Lagos take,
bayan an gama biki zasu koma Jos.
biki na saura sati jama'an Yelwan Shendam suka taho.
in da shima tuni ango Yusuf yana nan.
Ana saura kwana uku bikin Miemie ta karb'o musu d'inkin su. a parlour suka baje kayan Feeryal tana ta yaba kyan d'inkin.
bayan fitar Miemie Feeryal ta mike zata koma d'aki, ya shigo
rike da waya a kunnen sa, sai da ya wuce dinning kafin ta shige d'aki. wayan sa data gani ranar a d'akinta ta d'auko ta fito,
dai-dai lokacin da yazo zai wuce rike da karamar flask mai d'auke da Sudan tea a ciki.
ta moko masa wayar
a hankali cikin muryarta mai sanyi ta ce "Ga wayar ka......!