Sashe 29
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Su Abba suna zaune suna alhenin lamarin da tuni hukuma suka sunduma ciki.
suna ganin ta suka mike duk suka mike cike da mamaki.
Maryam ta tafi da gudu ta rungume ta na fad'in
"Feeryal ke ce ina kika shiga."
Hajja Umma ma ta rungumo ta.
Abba ko sai fad'in alhamdulillah ya ke.
ya ce "Dama hukuma sunce insha'allah zuwa dare za'a gano in da kike,
bari na kira wannan yaro Sadam dan yanzun nan yasake komawa, kasuwar dan yakuma bincikan lamarin, ku sake ta ta karaso zo zauna nan Feeryal hukuman suna waje ne shi ne basu shigo ba ai da sun shigo."
suka sake ta ta karo suka zazzauna Abba ya mike yana fad'in bari yaje ya sami jami'an tsaron da suka samo ta.
ta ce "Abba ba da kowa muka zo ba fa, Sahab ne ya kawo ni."
Abba ya zauna yana dubanta ya ce
"Sahab wane ne Sahab kuma?."
da sauri Maryam ta ce
"Wai Abdulrahim kike nufi?."
Abba ya mai da hankalin sa ga Maryam ya ce
"Wane ne shi d'in?."
"Abba Abdulrahim dai AA FIYA tsohon mijin ta."
Abba ya ce "Wane shi ne ya dawo da ke da ma shi ya d'au ke ki?."
da sauri Maryam ta ce
"Abba ni fa da take nuna min wai wasu suna kallon, ni fa babu wan da na gani, ko da take gudun ma babu me binta ita kad'ai take gudun ta."
baki ta cuno ta ce
"Allah na gansu kuma sun bini, ni dai ban san ya akayi na ganni tare da shi ba,
amma shi ya dawo da ni."
abun da ta sani ta basu labari.
a take suka fahimci ciwonta ya tashi kuma taga halittun da ita kad'ai ke iya ganin su.
Hajja Umma ta ce
"Ai mun godewa Allah ma da ya takaita iya haka, Allah ya dad'a rufa asiri."
a take Abba ya sanarwa hukumar cewa an same ta.
Tun daga ranar ba'a sake barin ta ta fita ko nan da can ba,
gudun abun da zai je ya dawo....
Lagos...
"Kuraiba ke ma lokacin barinki gidan nan ya yi."
Umma karima ta fad'a
tana wani shekewa da dariya tana kallon video da aka turo mata yanzu.
ta taka ta isa ta hakimce kan kujera tana kad'a kafa,
"Ni ce mamallakiyar komai na Alhaji Abubakar AA FIYA, kar ki ji dad'i ki baje kafa hatta uwar mazan gidan ita kanta sai ta bar min gidan, yanzu ta kan ki zan waiwayo Kuraiba."
ta danna wani lamba ta kai wayar kunne.
"Ai kin ka yana kyau Jaguu yanzu zakaji sakon ka, idan ka samo sauran zan turamaka tukuici mai tsoka."
ya ce "Angama Hajiya."
ta kashe wayar tana dad'a girgiza kafa...
Abuja....
Feeryal ce ta fito daga bayi da sauri tana fad'in
"Aunty Maryam ki kalli ni fa ashe da gaske ne kika ce narika cin abinci zan kara kiba, nakusa kai ki yau ma tuwa zanci da yawa na kara kiba."
Maryam dake zaune tana shayar da d'anta ta ce
"Kaji ta kamar wani abincin kirki ta ke ci, ke da shinkafarma bai fi kiyi cokali biyar ba kice kin koshi, sai dai in cake da yogurt ne ke hura ki."
"Allah Aunty Maryam yanzu ina ci fa, ai kin ga banjima da cin abinci bama, yanzu zansa kaya naje na sake ci dan na fara jin yunwa."
Maryam tayi dariya tana fad'in
"Yarinya tana so tayi kiba ta dawo cin abinci."
gaban mirror ta zauna tana murmushi tana shafa mai suna hira da Maryam, tana gamawa ta saka kaya ta tsaya gaban mirror tana kallon kanta.
"Aunty Maryam."
ta kira sunan tana tana kallon ta ta cikin mirror.
Maryam ta d'ago tana duban ta, ta ce
"Ba ki gani ba Allah har tunbi nayi, nayi kiba fa da gaske kuwa."
tayi maganar tana d'ame rigarta ta cikinta tana shafa shi.
Maryam ta girgiza kai tana mata dariya.
itama dariyar tayi.
ta zo ta d'auki Aiman tana fad'in
"Taho muje ka rakani muci tuwa, zan bawa Aunty Maryam mamaki idan naci na koshi nazamo katuwa kamar ta."
tayi waje Maryam ta biyo ta tana cewa
"Kamar da gaske wani cin abincin arziki zakiyi, muje naga yawan abincin."
Hajja Umma suka karasa dinning tana fad'in
"Ai zaki gani Hajja Umma zubo min tuwo cikin plt."
Hajja Umma ta yi mata hararar wasa tana fad'in
"Ni na isa na zuba duk masu aiki sun koshi karshe na zubar, kwatan malmala zan saka miki."
"Ah to wai ita gani take wani abincin kirki take ci, kullum sai ta ce min wai ta kara jiki, har da wani wai yau har tunbi tayi dan ta ci abinci d'azu."
Hajja Umma ta kalle ta tana zama kan kujeran dinning.
da sauri ta ce
"Ke Feeryal mike tsaye."
Hajja Umma tayi maganar tana dad'aatsowa kusa da ita.
ta mike tana cewa
"Allah Hajja Umma ke bakiga tunbin ba, ai kin san ina cin abiinci sosai."
"Bani d'an nan, ke Maryam karb'e shi."
Hajja Umma
ta karb'i d'an ta mikawa Maryam.
tana bin Feeryal da kallo daga sama har kasa.
da sauri ta ce
"Ke rabon da kiyi al'ada tun yaushe?."
shiru tayi tana son tuna tun yaushe ne rabon ta da yi.
Maryam ta ce
"Ai kuwa dai kamar tun da tazo fa banga tayi ba."
Hajja Umma ta ce
"Amma Maryam baki da hankali amma kuma shine baki fad'a ba, ni ina zan sani tun da dake kuke rayuwa cikin d'aki, sai dai in kun fito mu had'u,
kullum kuna tare da ita, amma ki kasa gane sauyi tare da ita, ni sam ban tab'a luraba in ba yau da aka kawo wanna zancen ba,
sabo da kullum babban riga abaya take fitowa da shi,
kina kallon ciki har yayi wayo a jikin yarinya ku kwana tare ku tashi tare ki kasa ganewa, duk da jikin ta d'anye ne dama ai ko gashi nan ya kara d'anyace wa in ba ka lura ba bazaka gane ba dan jikin nata d'anye ne dama,
d'auko mayafin ki maza muje nan asibitin bayan."
Feeryal tabi jikinta da kallo tana mamakin maganar Hajja Umma.
sai da Hajja Umma ta fad'a kafin
Maryam take ganin alamun ciki karara a jikin ta.
nan da nan Hajja Umma ta d'auketa sukayi asibiti, kwajin farko aka tabbatar mata tana da ciki, bayan anyi scanning aka tabbatar musu da wata uku da sati biyu ke nan cikin a jikinta...
ko da Abba ya sami labarin
Nan da nan ya kira Daddy ya sanar masa.
zo kaga farinciki gun Daddy d'iyanin ya kira Abdulrahim, ya ce yazo yana niman sa.
batare da b'ata lokaci ba ya amsa kiran.
ya nimi guri ya zauna a kasan carpet.
Daddy ya dube sa da kyau sannan ya ce
"Yanzun nan na sami labarin Feeryal tana da ciki, kimanin watanni uku da sati biyu, shi yasa na kiraka na sanar maka da wuri dan ka shaida."
shiru yayi kansa a kasa bai yi magana ba, Daddy ya ce
"Ka tashi ka je dama na shaida maka ne tun da wuri."
ya mike ya fice batare da ya ce kala ba.......!
Babu editing sai a karanta da hakuri
suna ganin ta suka mike duk suka mike cike da mamaki.
Maryam ta tafi da gudu ta rungume ta na fad'in
"Feeryal ke ce ina kika shiga."
Hajja Umma ma ta rungumo ta.
Abba ko sai fad'in alhamdulillah ya ke.
ya ce "Dama hukuma sunce insha'allah zuwa dare za'a gano in da kike,
bari na kira wannan yaro Sadam dan yanzun nan yasake komawa, kasuwar dan yakuma bincikan lamarin, ku sake ta ta karaso zo zauna nan Feeryal hukuman suna waje ne shi ne basu shigo ba ai da sun shigo."
suka sake ta ta karo suka zazzauna Abba ya mike yana fad'in bari yaje ya sami jami'an tsaron da suka samo ta.
ta ce "Abba ba da kowa muka zo ba fa, Sahab ne ya kawo ni."
Abba ya zauna yana dubanta ya ce
"Sahab wane ne Sahab kuma?."
da sauri Maryam ta ce
"Wai Abdulrahim kike nufi?."
Abba ya mai da hankalin sa ga Maryam ya ce
"Wane ne shi d'in?."
"Abba Abdulrahim dai AA FIYA tsohon mijin ta."
Abba ya ce "Wane shi ne ya dawo da ke da ma shi ya d'au ke ki?."
da sauri Maryam ta ce
"Abba ni fa da take nuna min wai wasu suna kallon, ni fa babu wan da na gani, ko da take gudun ma babu me binta ita kad'ai take gudun ta."
baki ta cuno ta ce
"Allah na gansu kuma sun bini, ni dai ban san ya akayi na ganni tare da shi ba,
amma shi ya dawo da ni."
abun da ta sani ta basu labari.
a take suka fahimci ciwonta ya tashi kuma taga halittun da ita kad'ai ke iya ganin su.
Hajja Umma ta ce
"Ai mun godewa Allah ma da ya takaita iya haka, Allah ya dad'a rufa asiri."
a take Abba ya sanarwa hukumar cewa an same ta.
Tun daga ranar ba'a sake barin ta ta fita ko nan da can ba,
gudun abun da zai je ya dawo....
Lagos...
"Kuraiba ke ma lokacin barinki gidan nan ya yi."
Umma karima ta fad'a
tana wani shekewa da dariya tana kallon video da aka turo mata yanzu.
ta taka ta isa ta hakimce kan kujera tana kad'a kafa,
"Ni ce mamallakiyar komai na Alhaji Abubakar AA FIYA, kar ki ji dad'i ki baje kafa hatta uwar mazan gidan ita kanta sai ta bar min gidan, yanzu ta kan ki zan waiwayo Kuraiba."
ta danna wani lamba ta kai wayar kunne.
"Ai kin ka yana kyau Jaguu yanzu zakaji sakon ka, idan ka samo sauran zan turamaka tukuici mai tsoka."
ya ce "Angama Hajiya."
ta kashe wayar tana dad'a girgiza kafa...
Abuja....
Feeryal ce ta fito daga bayi da sauri tana fad'in
"Aunty Maryam ki kalli ni fa ashe da gaske ne kika ce narika cin abinci zan kara kiba, nakusa kai ki yau ma tuwa zanci da yawa na kara kiba."
Maryam dake zaune tana shayar da d'anta ta ce
"Kaji ta kamar wani abincin kirki ta ke ci, ke da shinkafarma bai fi kiyi cokali biyar ba kice kin koshi, sai dai in cake da yogurt ne ke hura ki."
"Allah Aunty Maryam yanzu ina ci fa, ai kin ga banjima da cin abinci bama, yanzu zansa kaya naje na sake ci dan na fara jin yunwa."
Maryam tayi dariya tana fad'in
"Yarinya tana so tayi kiba ta dawo cin abinci."
gaban mirror ta zauna tana murmushi tana shafa mai suna hira da Maryam, tana gamawa ta saka kaya ta tsaya gaban mirror tana kallon kanta.
"Aunty Maryam."
ta kira sunan tana tana kallon ta ta cikin mirror.
Maryam ta d'ago tana duban ta, ta ce
"Ba ki gani ba Allah har tunbi nayi, nayi kiba fa da gaske kuwa."
tayi maganar tana d'ame rigarta ta cikinta tana shafa shi.
Maryam ta girgiza kai tana mata dariya.
itama dariyar tayi.
ta zo ta d'auki Aiman tana fad'in
"Taho muje ka rakani muci tuwa, zan bawa Aunty Maryam mamaki idan naci na koshi nazamo katuwa kamar ta."
tayi waje Maryam ta biyo ta tana cewa
"Kamar da gaske wani cin abincin arziki zakiyi, muje naga yawan abincin."
Hajja Umma suka karasa dinning tana fad'in
"Ai zaki gani Hajja Umma zubo min tuwo cikin plt."
Hajja Umma ta yi mata hararar wasa tana fad'in
"Ni na isa na zuba duk masu aiki sun koshi karshe na zubar, kwatan malmala zan saka miki."
"Ah to wai ita gani take wani abincin kirki take ci, kullum sai ta ce min wai ta kara jiki, har da wani wai yau har tunbi tayi dan ta ci abinci d'azu."
Hajja Umma ta kalle ta tana zama kan kujeran dinning.
da sauri ta ce
"Ke Feeryal mike tsaye."
Hajja Umma tayi maganar tana dad'aatsowa kusa da ita.
ta mike tana cewa
"Allah Hajja Umma ke bakiga tunbin ba, ai kin san ina cin abiinci sosai."
"Bani d'an nan, ke Maryam karb'e shi."
Hajja Umma
ta karb'i d'an ta mikawa Maryam.
tana bin Feeryal da kallo daga sama har kasa.
da sauri ta ce
"Ke rabon da kiyi al'ada tun yaushe?."
shiru tayi tana son tuna tun yaushe ne rabon ta da yi.
Maryam ta ce
"Ai kuwa dai kamar tun da tazo fa banga tayi ba."
Hajja Umma ta ce
"Amma Maryam baki da hankali amma kuma shine baki fad'a ba, ni ina zan sani tun da dake kuke rayuwa cikin d'aki, sai dai in kun fito mu had'u,
kullum kuna tare da ita, amma ki kasa gane sauyi tare da ita, ni sam ban tab'a luraba in ba yau da aka kawo wanna zancen ba,
sabo da kullum babban riga abaya take fitowa da shi,
kina kallon ciki har yayi wayo a jikin yarinya ku kwana tare ku tashi tare ki kasa ganewa, duk da jikin ta d'anye ne dama ai ko gashi nan ya kara d'anyace wa in ba ka lura ba bazaka gane ba dan jikin nata d'anye ne dama,
d'auko mayafin ki maza muje nan asibitin bayan."
Feeryal tabi jikinta da kallo tana mamakin maganar Hajja Umma.
sai da Hajja Umma ta fad'a kafin
Maryam take ganin alamun ciki karara a jikin ta.
nan da nan Hajja Umma ta d'auketa sukayi asibiti, kwajin farko aka tabbatar mata tana da ciki, bayan anyi scanning aka tabbatar musu da wata uku da sati biyu ke nan cikin a jikinta...
ko da Abba ya sami labarin
Nan da nan ya kira Daddy ya sanar masa.
zo kaga farinciki gun Daddy d'iyanin ya kira Abdulrahim, ya ce yazo yana niman sa.
batare da b'ata lokaci ba ya amsa kiran.
ya nimi guri ya zauna a kasan carpet.
Daddy ya dube sa da kyau sannan ya ce
"Yanzun nan na sami labarin Feeryal tana da ciki, kimanin watanni uku da sati biyu, shi yasa na kiraka na sanar maka da wuri dan ka shaida."
shiru yayi kansa a kasa bai yi magana ba, Daddy ya ce
"Ka tashi ka je dama na shaida maka ne tun da wuri."
ya mike ya fice batare da ya ce kala ba.......!
Babu editing sai a karanta da hakuri