← Book details Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 61

Sashe 32

Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Boka wai har sai yaushe bakin aljanin nan zai isa inda take ne,
dan Allah boka kayi duk yadda zakayi ka katura akashe abun da ke cikin ta lokaci nata tafi, a lissafi na yanzu watannin cikinnan biyar ke nan, saura wata hud'u ya zo duniya, boka idan yazo kwai matsala fa a kashe shi tun kafin yazo, sannan a shirya auren Siyama da shi."
Boka Mali ya d'ago daga bugo kasan da yake ya ce
"Ai kin ki bazai karasa ciwuwa ba har sai kin karasa jefa cikon na uku cikin kaskon can, ki tashi kije ki nemo cikon aikin ki,
ki tabbatar da biyu ne cikin sa ba d'aya ba, dan a wannan karon idan kika kuma kuskure to aikin ki ya rushe duka,
bazai tab'a gyaruwa ba, kin kuma tabba babban kuskure zaki fuskanci kalubale, mai girma."
kirji ta dafe ta ce
"Boka yanzu a ina zan samu kasan irin kasadar da nayi a wancan lokacin kafin na samo,
na karshen dana zo da shi sai da na narka kud'i kafin na samo, cutana yayi ce min yayi biyu ne a ciki, amma Boka babu yadda za'ayi aljanu su samo min, ni ko mawa ne zan iya badawa in har zan sami biyan bukata."
Boka Mali ya kece da kazamin dariya yana cewa
"Babu halin yin haka in har kina son cimma burin ki to dole ke zaki samo da kanki."
shiru tayi sannan ta gyara zama ta ce
"Boka zan samo kota halin yaya."
"Tashi kije ki taho da shi aikin ki ya gamu daga ranar duniyar ki tana hannunki."
Umma karima ta mike da sauri zuciyar ta abushe ta dasawa ranta ko ta halin yaya zata samo.

Yau Farida sanmakon zuwa AA FIYA STREET tayi kamar yadda halinta yake bata zuwa sashin kowa daga na Daddy sai na uwar ta da kakarta.
daga sashin Daddy ta tafi side d'in Hajiya.
tana zaune suna hira da Hajiya, 'yarta data yaye ta da d'an jimawa nata tsalle-tsalle cikin parlour'n.
Hajiya tabi yarinyar da kallo tana fad'in
"Har yanzu uwarki ta kasa yin ciki ta kuma haihuwa kun zauna irin abun 'ya'yan zamani, wai baza'ayi ciki ba sai yaro ya shekara biyar."
Farida ta ce
"Wai Hajiya yanzu an karb'i cikin aljanar yarinyar nan a matsayin na Ya Abdulrahim ke nan?
taya ma hakan zata yuwu a ce mu had'a jini da kaskantacciyar da ba'a san daga ina ta fito ba, ba'a san su saye dan gin ta ba, ta yuwuma 'yar wani kaskantacce talaka ne, taya za'ayi mu had'a jini da ita, wlh idan ta haihu ma ba'a isa a danganta mu da d'an da ta haifa ba,
dan cikin nan na tabbata bana Ya Abdulrahim bane."
Hajiya ta ce
"Um ni ma dai haka nagani, Abubakar ya tattare maganar ya hana yin sa, ba muna nan ba zamuga yadda d'an zai fito idan baiyi kama da Abokin turawa ba, to bazai karb'e shi a d'a ba, suje can su nima masa uba."
"Hajiya maganar kama ma bata taso ba, kawai ciki ba nashi bane dan wlh baza a kawo mana shege cikin gida ba."
Farida ta had'eye ragowar maganar nata sakamakon shigowar da yayi parlour'n.

Wani kallo ya wurga mata ta shiga taitayin ta.
ta mike da sauri tana gaishe shi bai amsa ba ya zauna.
ita ko ta ja 'yarta da sauri sukayi waje.
Hajiya ta dube shi tana cewa
"Abokin tuwa an shigo, dama ina ni man ka, cikin nan fa ni ina ganin ba naka bane,
kawai so ake ayi ma rufa-rufa a baka cikin da ba naka ba."
"Ni zan fad'i hakan ba ku ba."
ya yi maganar yana murtuke fuska.
da sauri Hajiya ta ce
"Yauwa ba naka bane ai dama nasan za'a rina, su rike kayan su a can, bari ma na kira Abubakar ya kira su tun da wuri, bazamu karb'i cikin ba gara tun da wuri su sani, tun kafin ta haihu."

Fuska ya dad'a sukewa ya ce
"Cikina ne mana ba ku kukaje kukayi jinyarta a daren mu na farko ba."
"To fisararre zama da wancan shegiyar aljanar yarinyar ya saka zama mara kunya, sau nawa ake kamata da maza a cikin gidan nan Karima tasha zuwa ta fad'a min."
ya dago ya dube ta sannan ya ce
"Yanzu idan aka ta da ke kina da hujjar da zaki kawo akan ta tab'a zina."
Hajiya ta ce
"Zancen banza yarinyar da a cikin gidan nan ta kawo wani, ga shaida an ganta da ido."
"Ni ne shaidar da yakamata a ji daga baki na, ba kurika yanke hukunci kaitsaye ba, Beauty bata tab'a sanin wani namiji ba, ni na fara sanin ta mace,
kada wani ya sake sheganta min d'a idan kuma ba haka ba zan d'auki mataki a kan kowa!."
yana gama fad'in haka ya mike yanufi kofar fita.
Hajiya ta saki uban salati
"Laha'ilaha'illallah Abokin turawa, Eh ba shakka anyi ma turen aljanu, dole na sa a nemo mai rokiyya."
Goggo Bishira data fito daga d'aki ta sinkayo zancen a sama ta saki murmushi tana karasowa cikin parlour'n.
"Zo Bishira kirawo min Abubakar ina ga fa yaron nan ya sami matsala, Eh an masa turen aljanu."
Goggo Bishira ta zauna tana cigaba da murmushi ta ce
"Hajiya wani turen aljanu gaskiya ya fad'a, duk da shiru irin nasa sai da aka sa shi ya maganu, tabbas shine babban shaidar matarsa gaskiya ya fad'a, a budurwa ya sami matarsa dan haka babu wata hujjar da za'a ce ciki ba nashi bane, kuma dai na wannan maganar, yafi kowa sanin cikin nashi ne ko akasin haka."
"To ai shike nan mu namu ido idan aka haifi aljani muna daga gege."
"Allah ma ya tsare."
cewar Gogga Bishira.

Umma karima ce da Mommy zauna anata kuskus, Umma karima ta kawo musu magani su sakawa Daddy a abinci wanda bokan ta ya bata.
sun rasa hanyar da zasu bi su saka masa dan ba cin abincin su yake ba.
Umma karima ta gyara zama cikin yin kasa da murya ta ce
"Yanzu ya zamuyi gashi malam ya ce, mu tabbata yaci maganin nan, yana ci duk asirin da Hajiya Fatima ta masa zai karye, sannan ya sake ta tabar gidan nan, kin ga babu labarin zuwan d'an shege cikin gidan nan, tun da ita uwar gayyar tabar gidan,
amma Hajiya Halima wani hanzari ba gudu ba, ga wani shawari mana, wata kila idan muka bi ta hanyar zamu sami kofar b'ullewa."
Mommy ta ce
"Yauwa fad'i muji Allah yasa ta b'ulle, ayita ta kare."
Umma karima ta ce
"Na ce me zai hana a had'a Siyama aure da Abdulrahim, bayan aure da kwana biyu ta dafo abinci ta zuba maganin ciki ta kawo mishi, irin dai ace girkin amarya, amarya tayi girki ta kawo wa uban miji,
amma yanzu mu idan muka ce zamuyi kinsan halin Alhaji ba lallai ne ma yaci ba, sai ya iya zargin wani abun ma,
amma idan ita tayi masa kuma yasan amarya ce zai iya ganin hakan a tsigar kyautatawa irin ta suruka, bazai kawo komai a ransa ba zai ci, amma me kika gani in kina gani da wata dabarar sai a sauya, ni dai ina ga ita ce kad'ai hanya mai sauki, amma ya kika ce?."
Mommy ta d'anyi jimm sanna ta ce
"Eh to wannan hanyar da aka biyu tayi, amma kina ganin su yaran zasu amince, kinsan fa taurin kan Abdulrahim."
da sauri Umma karima ta ce
"Haba haba Hajiya Halima kina uwar tasa bazaki iya juyasa yadda kike so ba, ai Abdulrahim yana jin maganar ki, kina bashi umurni zaiji,
nima zanje na tirsasa Siyama dolen ta ta amince dan bukatar mu yabiya,
idan ba haka ba fa wlh zamu zamo 'yan kallo, muna ji muna gani mu da gidan 'ya'yan mu zaifi karfin zaman mu,
karshe ita da bata saka ko d'aya ba ita zata mallake gidan."
Mommy ta ce
"To shike nan inaga hakan kawai za'ayi."
Umma karima ta ce
"Yauwa shine magana Hajia Fatima tana son ganin bayan mu, idan bamuyi da gaske ba kuwa sai ta kora mu da kafafunmu, dan malam ya tabbatar min da kalan asirin da take wa Alhaji, ya ce gurin manya manyan bokaye yake zuwa, tana yawo da sunan Alhaji da namu dan a farrakamu a kan 'ya'yan mu, gara mu tashi mu tsaya tun kafin dare ya yi mana."
Mommy ta jinjina kai tana fad'in
"Ai kuwa ta sha karya."

Umma karima na fita Mommy ta kira shi, ta ce idan ya dawo tana niman sa.
har dare bai shigo ba takuma kiransa,
ko da yazo ta ce ya zauna tana da magana da shi.
bayan ya zauna Mommy ta ce
"Abdulrahim yakamata kayi aure fa zaman ka haka ba mata, bai kyautu ba,
ga Siyama kanwar Hajiya Karima na yaba da hankalin yarinyar, me zai hana ka aureta tun da 'yar gida ce ansan halinta, Kuraiba dai tsautsayi ce yasa na ce ka aure ta, amma ita wannan ai an san komai nata."
da sauri ya d'ago ya dube ta sannan ya ce
"Shi ke nan ni rayuwata a haka zata kare, ko wace kare da doki ita za'a bani na aura,
ai ni nagama aure Mommy ko da ina da burin na sake aure bazan auri wama kika ce Siyama take ko wa? bazan aure ta ba,
idan zamata a gida ne bakwa so zantafi na baku guri."
yana kaiwa nan ya mike tsaya ya fice......!

Kuyi hakuri wlh nafi kowa son nagama littafin nan na huta wanna littafi ya katse min abubuwa da dama amma insha'allah mun kusa mu karkare

Mommy ta bud'e baki tana kallon sa har ya fice.
a fili ta ke fad'in
"Ai dole na lallab'a ka a wannan karon dan burin mu ya cika, idan na ce zan d'aga jijiyar wuya hakar mu bazata cimma ruwa ba."
Chapter 32 · 0% Book details