Sashe 38
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bappa Salihu ya shiga gurin Daddy.
anan ya tadda su Dad da Abbieh.
sunyi mamakin ganin sa suka mike suna yi masa sannu da zuwa.
Daddy da har yanzu jikin sa da saura ya ce
"Bappa baka sanar mana zaka zo ba bamu tura mota domin taron ka ba a gafarce mu."
Bappa Salihu ya ce
"Zauna Abubakar."
ya dubi Dad da Abbieh yana cewa "Tukur Sulaiman ku kirawo hukuma azo a tafi da Halima."
Abbieh yayi saurin cewa
"Allah ya huci zuciyan ka Bappa da dai anyi maganar a cikin gida daya fi."
"Hakane kuwa kayi hakuri Bappa kuskure kam anyi sai dai fatan a gyara nan gaba."
cewar Dad.
Bappa Salihu ya ce
"Babu maganr gyara kuskure, baza'a rufe maganar a gida ba dan suma raine da su, hukun cin kisa kuma kisa ne, dole kuma a hukuntata,
Abubakar ka sake ta kafin a tafi da ita."
Daddy ya gyara zaman sa yana cewa
"Bappa na saki Halima amma na maida ita, abisa umurnin Hajiya,
da fari nima hukuncin dana so zartarwa ke nan, kiran hukuma azo a tafi da ita,
sai dai yin hakan bashi ne zai sa, yaran su dawo ba."
Bappa Salihu ya ce
"Ko da bazasu dawo ba hukunci ya rayata a kanta, kuma dole a zartar da hukunci."
Abbieh ya ce
"Bappa a bar maganar zuwa yarinyar ta sami sauki, a halin da ake ciki yanzu shima kansa Yaya Abubakar ba balafiyar ne da shi ba, kayi hakuri a aje maganr tukun."
Daddy da Dad duk suka sa baki akan bar kiran hukuma tukun.
Bappa Salihu badun ya so ba ya
hakura amma da tabbatar musu da cewa, zai zauna tare da su a nan har lokacin da za'a yanke wa Mommy hukunci.
ya fita yana tambayar Ajmaal ina Abdulrahim yake?.
ya ce tun jiya daya shige side d'in sa bai ga fitarsa ba har yau.
Bappa Salihu ya nufi sashin nasa Ajmaal na biye da shi.
mai gadin side d'in a ya shaida musu yana ciki.
suka karasa kofar parlour'n sa Ajmaal ya ya babbuga.
ya d'au tsawon ninuna 5 kafin yazo ya bud'e.
yana sanye da gajeren wanda da singilet.
fuskarsa babu annuri.
Bappa Salihu ya bubbaga kafad'ar sa yana cewa
"Sannu kaji najimin duniya, Allah ya huci zuciyar ka."
baiyi magana ba har Bappa Salihu ya juya daga bakin kofar suka fice daga side d'in yana tsaye.
kana a sannu ya taka ya koma ciki.
A b'angaren Bappa Salihu kuwa suna fita
Ajmaal ya d'auke sa, zuwa asibiti in da Feeryal take.
sosai Bappa Salihu ya bawa su Aunty hakuri ya koma ga Feeryal itama yakuma bata tabbacin za'a bi mata kadinta.
Aunty dai har yanzu hawaye bai bar zuba a idanunta ba, sai dai tace masa ba komai, dan Abba'n Abuja ya gargad'e ta da d'aukar mataki a hannunta, shima kuma baiyi magana ba har lokacin duk da sunji matukar zafin abun da ya faru..
A b'angaren Mommy kuwa jikinta ya sanyaya matuka zafi biyu ta ko ina, gana Daddy gana mahaifinta.
tana zaune tayi jigum a d'aki kiran Hajiya Luba ya shigo wayarta.
kamar bazata d'aga ba harya kusa yankewa kafin ta d'aga.
"Hajiya Halima ikon Allah ashe haka kika kware a iya kisan kai,
amma anji kunya atarihin mu mu kawaye babu wacce ta tab'a aikata irin abunda kika aikata yanzu, to ina laifin ki had'a da babban d'an naki duk ki kashe sakarai mara lissafi."
Hajiya Luba tana kaiwa nan ta kashe wayar.
Mommy tabi wayar da kallo jikinta na dad'a jin sanyi, wanda har ya kai da jin kamar abun kunya ta aikata,
dan tun da abun ya faru take amsa kira daga kawayen ta suna masu mamakin abun da ya faru.
Kwanan Feeryal biyu ita ma aka sallame ta.
tun da suka dawo gida Aunty a zubda kwalla take, ta kasa iya daure zuciyarta.
a yammacin ranar da suka dawo Aunty na zaune a gefen Feeryal tana had'a mata ruwan zafi da milo, jifa-jifa tana share hawaye.
ganin hawayen nata yake sa Feeryal d'in yin hawaye.
a hankali Feeryal ta kwantar da kanta jikin kafad'ar Aunty,
takai bayan hannunta ta goge hawayen da suka zubo mata.
cikin muryarta mai sanyi ta ce
"Ammie to wai mu meye damuwar mu ma, ba kin ce idan na haihu za'a basu d'ansu ba,
to ai 'ya'yan su suka kashe mu babu ruwan mu, Ammie ki daina kuka ni ma kina sani kuka, daga yau kar mu sake damuwa tun da dama nasu ne."
Aunty ta matse ido da karfi tana son had'iye kukan da ya taso mata.
da sauri ta mika mata cup d'in ta mike ta fice ta shige d'akin ta, dan bata son yin kukan agaban ta.
bin bayan Aunty tayi da kallo har ta fice.
a hankali ta kai cup d'in bakin ta ta kurb'i yea d'in.
Aunty tayi kuka sosai kafin ta fito bayan ta wanke fuskarta ta share kamar batayi ba.
tana fitowa Abdulramin ya shigo d'auke da sallama mara sauti a bakin sa.
Aunty ta amsa ya karaso ciki ya gaisheta batare da ya had'a ido da ita ba.
Aunty ta amsa gaisuwar tasa gami da d'an yin murmushi ta ce
"Tana ciki."
ta juya ta koma d'akin ta.
a sannu ya tako ya tura kofar, da sauri ta d'ago zaton ta Aunty ce.
ganin shine ta sauke idanunta kasa.
ido ya kura mata tare da soma takowa cikin d'akin, ya iso bakin gadon.
tana jin yadda idanunsa yake kafe a kanta.
sinkayo muryarsa tayi
"Ina mai baki hakuri na rasa 'ya'yan ki da kikayi."
ta jiyo maganar sa daga in da yake tsaye a kanta.
da sauri ta d'ago ta kalle sa sai kuma ta cuno lips tare da sauke idanunta kasa ta ce
"Ya'yan ku dai ai dama naku ne, ba haka kuka zab'ar musu ba, ni babu ruwana."
tayi maganar tana dad'a cuno baki cikin yanayin ta mai sanyi da fita da yanayin shagwab'a.
cike da jin haushin yadda Mommy'n sa tasa Ammie'n ta tashiga damuwa take ta kuka akan yaran.
ta juya kai ta d'aya gefen tana mai dad'a cuno baki gaba.
bataji takun tafiyarsa ba sai karar bud'e kofa taji, ta juyo ta hangi bayan sa yana fita daga d'akin.
kai ta kuma juyawa tana mai dad'a b'ata fuska da gaske wai haushi take ji dan ansa Ammie'n ta kuka..
"Feeryal."
taji an fad'a ta juyo da sauri jin muryar Chuchu da Chulu.
yunkurin mikewa tayi da sauri, suka rike gefe da gefen kafad'un ta suna cewa
"Yi a hankali Feeryal."
ta zauna suka zauna a gefen ta suna fad'in
"Ki gafarce mu san da abunnan ya faru bama kusa, munyi bakincikin da muka gaza taimakon 'ya'yan ki har suka salwanta, muna niman afuwarki ki gafarce mu."
hannaye bibbiyu suke rokonta.
ganin yadda suma suka nuna damuwa sosai ta ce "Ni fa yanzu na daina damuwa tun da dama nasu ne, ko ma me sukayi da su oho ni ban damu ba."
Chuchu da Chulu sun dad'e a gurun ta kafin suka tafi...
Zaune yake a office d'insa, idanunsa a lumshe ya jingina bayan sa jikin kujera yana d'an jujjuyawa.
Dr Imran ne ya shigo ya karaso yana yi masa kallon tausayawa,
tabbas uwansa ta kasance mai son kai,
ko bai fad'i damuwar sa ba bayau ya saba zama da shi ba,
duk da halayen sa masu wuyar gane wa ne, amma tabbas ya lura da shiga kunci tare da shi tun ranar da uwassa tayi sananiyyar mutuwar 'ya'yan sa.
table d'in gaban sa ya bubbuga, a hankali ya bud'e lumsassun idanuwan sa.
Dr Imran ya ce
"AA akwai C'S da kasa time 1 30 an shirya ko mai saura 20 seconds yanzu."
mikewa yayi tare da d'aukar makullin motar ya nufi kofa yana cewa
"Kayiwa Dr John magana bazan yi C'S ba."
Dr Imran yabi bayan sa da kallo har ya fice.
ire-iren wad'an nan halayen nasa duk wan da yake tare da shi yakan sha wuya wajen gano inda lamuran sa suka dosa, baka b'a gane albiblarsa.
anan ya tadda su Dad da Abbieh.
sunyi mamakin ganin sa suka mike suna yi masa sannu da zuwa.
Daddy da har yanzu jikin sa da saura ya ce
"Bappa baka sanar mana zaka zo ba bamu tura mota domin taron ka ba a gafarce mu."
Bappa Salihu ya ce
"Zauna Abubakar."
ya dubi Dad da Abbieh yana cewa "Tukur Sulaiman ku kirawo hukuma azo a tafi da Halima."
Abbieh yayi saurin cewa
"Allah ya huci zuciyan ka Bappa da dai anyi maganar a cikin gida daya fi."
"Hakane kuwa kayi hakuri Bappa kuskure kam anyi sai dai fatan a gyara nan gaba."
cewar Dad.
Bappa Salihu ya ce
"Babu maganr gyara kuskure, baza'a rufe maganar a gida ba dan suma raine da su, hukun cin kisa kuma kisa ne, dole kuma a hukuntata,
Abubakar ka sake ta kafin a tafi da ita."
Daddy ya gyara zaman sa yana cewa
"Bappa na saki Halima amma na maida ita, abisa umurnin Hajiya,
da fari nima hukuncin dana so zartarwa ke nan, kiran hukuma azo a tafi da ita,
sai dai yin hakan bashi ne zai sa, yaran su dawo ba."
Bappa Salihu ya ce
"Ko da bazasu dawo ba hukunci ya rayata a kanta, kuma dole a zartar da hukunci."
Abbieh ya ce
"Bappa a bar maganar zuwa yarinyar ta sami sauki, a halin da ake ciki yanzu shima kansa Yaya Abubakar ba balafiyar ne da shi ba, kayi hakuri a aje maganr tukun."
Daddy da Dad duk suka sa baki akan bar kiran hukuma tukun.
Bappa Salihu badun ya so ba ya
hakura amma da tabbatar musu da cewa, zai zauna tare da su a nan har lokacin da za'a yanke wa Mommy hukunci.
ya fita yana tambayar Ajmaal ina Abdulrahim yake?.
ya ce tun jiya daya shige side d'in sa bai ga fitarsa ba har yau.
Bappa Salihu ya nufi sashin nasa Ajmaal na biye da shi.
mai gadin side d'in a ya shaida musu yana ciki.
suka karasa kofar parlour'n sa Ajmaal ya ya babbuga.
ya d'au tsawon ninuna 5 kafin yazo ya bud'e.
yana sanye da gajeren wanda da singilet.
fuskarsa babu annuri.
Bappa Salihu ya bubbaga kafad'ar sa yana cewa
"Sannu kaji najimin duniya, Allah ya huci zuciyar ka."
baiyi magana ba har Bappa Salihu ya juya daga bakin kofar suka fice daga side d'in yana tsaye.
kana a sannu ya taka ya koma ciki.
A b'angaren Bappa Salihu kuwa suna fita
Ajmaal ya d'auke sa, zuwa asibiti in da Feeryal take.
sosai Bappa Salihu ya bawa su Aunty hakuri ya koma ga Feeryal itama yakuma bata tabbacin za'a bi mata kadinta.
Aunty dai har yanzu hawaye bai bar zuba a idanunta ba, sai dai tace masa ba komai, dan Abba'n Abuja ya gargad'e ta da d'aukar mataki a hannunta, shima kuma baiyi magana ba har lokacin duk da sunji matukar zafin abun da ya faru..
A b'angaren Mommy kuwa jikinta ya sanyaya matuka zafi biyu ta ko ina, gana Daddy gana mahaifinta.
tana zaune tayi jigum a d'aki kiran Hajiya Luba ya shigo wayarta.
kamar bazata d'aga ba harya kusa yankewa kafin ta d'aga.
"Hajiya Halima ikon Allah ashe haka kika kware a iya kisan kai,
amma anji kunya atarihin mu mu kawaye babu wacce ta tab'a aikata irin abunda kika aikata yanzu, to ina laifin ki had'a da babban d'an naki duk ki kashe sakarai mara lissafi."
Hajiya Luba tana kaiwa nan ta kashe wayar.
Mommy tabi wayar da kallo jikinta na dad'a jin sanyi, wanda har ya kai da jin kamar abun kunya ta aikata,
dan tun da abun ya faru take amsa kira daga kawayen ta suna masu mamakin abun da ya faru.
Kwanan Feeryal biyu ita ma aka sallame ta.
tun da suka dawo gida Aunty a zubda kwalla take, ta kasa iya daure zuciyarta.
a yammacin ranar da suka dawo Aunty na zaune a gefen Feeryal tana had'a mata ruwan zafi da milo, jifa-jifa tana share hawaye.
ganin hawayen nata yake sa Feeryal d'in yin hawaye.
a hankali Feeryal ta kwantar da kanta jikin kafad'ar Aunty,
takai bayan hannunta ta goge hawayen da suka zubo mata.
cikin muryarta mai sanyi ta ce
"Ammie to wai mu meye damuwar mu ma, ba kin ce idan na haihu za'a basu d'ansu ba,
to ai 'ya'yan su suka kashe mu babu ruwan mu, Ammie ki daina kuka ni ma kina sani kuka, daga yau kar mu sake damuwa tun da dama nasu ne."
Aunty ta matse ido da karfi tana son had'iye kukan da ya taso mata.
da sauri ta mika mata cup d'in ta mike ta fice ta shige d'akin ta, dan bata son yin kukan agaban ta.
bin bayan Aunty tayi da kallo har ta fice.
a hankali ta kai cup d'in bakin ta ta kurb'i yea d'in.
Aunty tayi kuka sosai kafin ta fito bayan ta wanke fuskarta ta share kamar batayi ba.
tana fitowa Abdulramin ya shigo d'auke da sallama mara sauti a bakin sa.
Aunty ta amsa ya karaso ciki ya gaisheta batare da ya had'a ido da ita ba.
Aunty ta amsa gaisuwar tasa gami da d'an yin murmushi ta ce
"Tana ciki."
ta juya ta koma d'akin ta.
a sannu ya tako ya tura kofar, da sauri ta d'ago zaton ta Aunty ce.
ganin shine ta sauke idanunta kasa.
ido ya kura mata tare da soma takowa cikin d'akin, ya iso bakin gadon.
tana jin yadda idanunsa yake kafe a kanta.
sinkayo muryarsa tayi
"Ina mai baki hakuri na rasa 'ya'yan ki da kikayi."
ta jiyo maganar sa daga in da yake tsaye a kanta.
da sauri ta d'ago ta kalle sa sai kuma ta cuno lips tare da sauke idanunta kasa ta ce
"Ya'yan ku dai ai dama naku ne, ba haka kuka zab'ar musu ba, ni babu ruwana."
tayi maganar tana dad'a cuno baki cikin yanayin ta mai sanyi da fita da yanayin shagwab'a.
cike da jin haushin yadda Mommy'n sa tasa Ammie'n ta tashiga damuwa take ta kuka akan yaran.
ta juya kai ta d'aya gefen tana mai dad'a cuno baki gaba.
bataji takun tafiyarsa ba sai karar bud'e kofa taji, ta juyo ta hangi bayan sa yana fita daga d'akin.
kai ta kuma juyawa tana mai dad'a b'ata fuska da gaske wai haushi take ji dan ansa Ammie'n ta kuka..
"Feeryal."
taji an fad'a ta juyo da sauri jin muryar Chuchu da Chulu.
yunkurin mikewa tayi da sauri, suka rike gefe da gefen kafad'un ta suna cewa
"Yi a hankali Feeryal."
ta zauna suka zauna a gefen ta suna fad'in
"Ki gafarce mu san da abunnan ya faru bama kusa, munyi bakincikin da muka gaza taimakon 'ya'yan ki har suka salwanta, muna niman afuwarki ki gafarce mu."
hannaye bibbiyu suke rokonta.
ganin yadda suma suka nuna damuwa sosai ta ce "Ni fa yanzu na daina damuwa tun da dama nasu ne, ko ma me sukayi da su oho ni ban damu ba."
Chuchu da Chulu sun dad'e a gurun ta kafin suka tafi...
Zaune yake a office d'insa, idanunsa a lumshe ya jingina bayan sa jikin kujera yana d'an jujjuyawa.
Dr Imran ne ya shigo ya karaso yana yi masa kallon tausayawa,
tabbas uwansa ta kasance mai son kai,
ko bai fad'i damuwar sa ba bayau ya saba zama da shi ba,
duk da halayen sa masu wuyar gane wa ne, amma tabbas ya lura da shiga kunci tare da shi tun ranar da uwassa tayi sananiyyar mutuwar 'ya'yan sa.
table d'in gaban sa ya bubbuga, a hankali ya bud'e lumsassun idanuwan sa.
Dr Imran ya ce
"AA akwai C'S da kasa time 1 30 an shirya ko mai saura 20 seconds yanzu."
mikewa yayi tare da d'aukar makullin motar ya nufi kofa yana cewa
"Kayiwa Dr John magana bazan yi C'S ba."
Dr Imran yabi bayan sa da kallo har ya fice.
ire-iren wad'an nan halayen nasa duk wan da yake tare da shi yakan sha wuya wajen gano inda lamuran sa suka dosa, baka b'a gane albiblarsa.