Sashe 16
Feeryal Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali take shirin dan har cikin ranta bata jin zataje gurin dinner, dan tasan zata fuskanci kalubale a gun Mommy da Umma Karima da wasu daga cikin danginsu.
kiran Miemie ne ya shigo wayarta, Miemie ce ta
"Kiyi sauri ki fito Feeryal gamu mun fito."
ta ce "Tom."
ta sauke wayar, tayi ta lalawai, Miemie tayi ta kiranta a waya tayi ta ce mata gatanan fitowa, daga bisani ta ce mata itafa su Mommy take tsoron abun da zasuje su mata.
Miemie ta ce
"Ina ruwanki da su muna gefe suna gefe."
kai ta girgiza kana ta ce
"Gani fitowa."
sai sannan ta d'auko ashoben nasu tasaka pant da underwear batare da ta sa bra ba, tayi tayi ta tasaka doguwar rigar tasama takasa, dole sai ta kasa ta saka ta janyo sama ya wuce da kyar.
d'inkin ya kamata sam bataji dad'i ba, dan bata saba sa kayan daya matse ta ba.
ta d'au gyale ta saka akan ta,
ta zura takalmi mara tudu sosai.
ta d'an feshe jikin ta da turare ba masu karfi ba.
kana ta d'au handbag da wayan ta fita..
Tana fita ta hangoshi yana fito daga gefen sa,
tana kokarin wucewa yayi mata alama da hannu ta koma ciki.
tsayuwa tayi kamar zatayi kuka, takuma duban shi ya tsare ta da ido, fuskarsa bawasa.
kasa tayi da kanta tana jin hawaye na taruwa mata, sai dai ta kasa iya kuma kallon sa.
a hankali ta juya ta koma ciki ta fad'a saman bed.
Sai da yaga shigewar ta kafin ya fita.
motoci nata fita da mutane yawanci a daren zasu wuce, dan daga gurin dinner ango da amarya zasu wuce Jos da wasu daga cikin 'yan biki da yawa.
dan akwai wani gaggarumin shagalin da za'a gudanar a washegari a can Jos d'in.
tuni anyi bukin jiri na jiran su 11:30 zasu tashi, shi yasa 11 za'a tashi a gun dinner.
Daddy da ya fito daga side d'in Aunty ya tsaya suna sallama da wasu 'yan'uwan shi.
Abdulrahim ya karaso gurin san da motar ba'in ya tashi.
Daddy ya dube shi tare da amsa gaisuwar da yake masa,
ya ce
"Ina Feeryal ga 'yan'uwan ta nan duk kowa yafita za'a tafi."
shiru ya yi baiyi magana ba
Daddy yakuma duban sa tare da karantar sa kana ya ce
"Idan kai bazakaje ba, to ita kabarta taje, akan me yasa zaka hanata, wata kila tasa ranta tana son zuwa."
nan ma baiyi magana ba sai nad'e hannayensa da yayi a kirji.
A b'angeren Feeryal wayanta tajanyo tana share d'an guntun kwallan da suka zubo mata.
ta danna numman Aunty, tana d'agawa cikin muryar shagwab'a ta ce
"Ammie Sahab ya hanani zuwa."
da sauri Aunty ta ce
"Ban amince kiyi gardama ba ki zauna, ban sanki da kafiya ba kar naji kinyi masa gardama"
baki ta cuno ta sauke wayar.
itafa ba gun biki take son zuwa ba so take tasamu ta fita taje b'angaren Ammien nata..
da sauri ta kalli kofa jin an turo kofar.
daga bakin kofar ya tsaya ya ce
"Ki tashi ki sa hijab kije."
aiko bai rufa baki ba ta mike.
ya tab'e baki yajuya.
babban hijabin sallar ta ta zura tayi waje.
Yana tsaye daga sama yana hango cikin gidan.
motoci duk sun gama tafiya.
akan idon sa ta shige sashin Aunty.
Aunty ta bud'e baki cike da mamakin ganin ta ta ce
"Ke Feeryal bana ce kar ki fito ba."
"Ammie shi yace naje."
"Feeryal yaushe kika koyi karya?."
"Allah Ammie da gaske Sahab shi ya ce nasa hijab naje."
Aunty tayi shiru tana nazartar ta kana ta ce
"To me ya hanaki binsu Miemie ku tafi kika zo nan?."
zama tayi kan kujera tana cewa
"Nifa dama Ammie ba zuwa zanyi ba ni bazan je gurin dinner ba."
"Ai ko sai ki tashi ki koma d'akin ki, tun da ba tafiya zakiyi ba."
"Ayya Ammie kibari sai anjima, idan suka dawo sai na koma, nima nayi dinner na anan."
tayi maganar tana cire hijab d'in.
Aunty tayi murmushi tana girgiza kai....karfe goma nayi tace ta tashi ta tafi dare ya yi.
Feeryal ta shagwab'e fuska,
"Ammie kaina ciwo yake min kuma ina jin yunwa."
Aunty ta ce
"To tashi maza mijin ki likita, shi yasan maganin da ya dace ya baki,
fad'a min dai yanzu me kike son ci, sai na dafa na baiwa Baba Rabi ta kawo miki yanzu,
gobe idan Allah ya kaimu ma ki huta na d'auke miki girkin gobe duka, ni zan dafa nabayar a kawo miki, kinji ko 'yammatan Ammie."
takuma shagwab'ewa tana fad'in
"Faten dankali da kifi kuma zan jira kiyi."
dakyar talallab'ata tace yanzu zatayi tabada akawo mata.
suka fito ta yi mata rakiya har bakin side d'in su sai da taga shigarta kafin ta juyo.
Feeryal na shiga d'aki ta kwab'e hijab tashiga kokarin cire kayan jikinta, dan ba karamin damunta yake ba.
tayi-tayi ta cire ta gagara,
tarika kokawa da rigar kamar zatayi kuka.
da sauri ta shige bathroom jin fitsarin da take ji yana kokarin fitowa, tayi ta fito tacigaba da kokarin cire rigar ga zip d'in rigar can sama kuma yayi tauri sosai.
zama tayi bakin gado tana maida numfashi kamar wacce tayi wani aikin.
ta janyo waya ta dannan number Aunty tana d'agawa ta ce
"Ammie na kasa cire rigar, zanzo ki jamin zip d'in."
Aunty ta ce
"Me ya kaiku yin matsastsen d'in ki, karki fito ai ba ke kad'ai bace a side d'in mijinki na nan sai kije yaja miki, haka kawai kamatse kanka da kanka kahana kanka jan numfashi da kyau."
Aunty ta kashe wayar Feeryal ta kwab'e fuska kamar zatayi kuka.
taya za'ayi ma taje tace yaja mata zip ai gara ta kwanta haka.
ta gyara ta kwanta.
tana sa kafad'arta akan gado taji rigar yana cizon ta, gashi ko numfashi mai dad'i bata iya ja dan bata sama ba sa irin matsastsun kayan nan ba, uwa uba kuma bata iya bacci da kaya masu nauyi ba, in ba sleeping dress ba.
ta mike da sauri ta d'au hijap ta fito.
tana sa kafarta a farfajiyar gidan tajiyo kukan kule, ai da gudu ta koma ciki..
ta haye gado ta kwanta.
ta matse ido tana fatan bacci ya d'auke ta.
amma ina tamkar mistsinin ta ake tacikin kayan,
idan ya manne da jikinta har wani radad'i take ji.
zunbur ta mike tana sosa jikinta idonta sun cika da kwalla.
tana son tafita taje Ammien ta ta taimaka mata tacire rigar, amma tana tunanin mage a waje.
kwalla ta share in har ba kwana zaune take son yi ba to tana bukatar rigar nan yabar jikin ta.
ke nan bata da zab'in da ya wuce taje ya taimaka yazuge mara zip d'in.
kwalla ta share ta d'auki hijab ta saka kana ta fito a hankali tana waige-waige, dan a tsoro take sai gani take kamar zata gamu da magen..
Kofar da ke sakanin gefen ta da nashi, wanda take ganin duk san da zai shigo tanan yake shigowa.
a hankali ta isa jikin kofar ta bud'e jiki a sanyaye.
ido ta zubawa corridor daya bayyana a gana ta, bata tab'a kawo kanta nan ba.
a hankali tabi cikinsa ta taka har zuwa wata kofar da ta gani a can gaba, nan ma ta bud'e a hankali sai da ta d'anyi jim kafin tazura kafafunta ta shige ciki.
wani sassanyan kamshi ne gami da sanyi ya bugeta, har sai da ta d'an kame jikinta ta nad'e hannunta cikin hijab, dan ba kad'an ba sanyin ya rasa fatarta ya zarce har cikin jikinta.
gani tayi ta bayyana cikin wata duniya.
katon parlour mai d'auke da kayan alatu na musamman.
ido ta shiga bazawa cikin katafaren parlour'n.
can ta hango sa zaune saman kujera idanunsa akan system d'in da ke gabansa.
takai 10snd tsaye
kana a hankali tashi d'aga kafarta tana takowa cikin parlour'n.
yayin da take dad'a jin sanyin na kuma shi garta.
tun shigan ta idanunsa a kan abun da yake bai d'ago ba.
a d'an nesa da shi ta tsaya d'an kallon shi tayi kana ta sunkiyar da kanta tana wasa da bakin hijabin ta.
a hankali cikin muryarta mai sanyi ta ce
"Um dan Allah Sahab dama..dama..dama umm."
sai kuma tayi shiru.
a sannu ya d'ago idanunsa ya sauka cikin nata, da sauri ta janye nata idanun takuma yin kasa da kanta.
mai da idanunsa yayi kan laptop d'in.
hannu ta yarfe kana ta ce
"Dama.um dan Allah dama so nake kad'an taimaka kajamin zip..zip d'in riga ta, nakasa cirewa ne, kuma bazan iya bacci da shi ba."
tsai da abun da yake yayi kana ya d'ago, kasa takuma yi da kanta.
5 second idanunsa a kanta, sai kuma ya gyara zamansa ya yi mata alama da hannu ta zo......!
A hankali tashiga d'aga kafarta, ta maso in da yake.
sai kuma taja ta tsaya
kanta a kasa tana wasa da 'yan yatsun ta ta cikin hijab.
"You are waisting my time."
ya fad'a yana gimtse fuska.
a hankali ta juya bayan ta a sannu tad'an ja hijab d'in tayi sama da shi.
ratan da ke sakanin su yakai taku uku, sai noke-noke take takasa jan hijab d'in duka.
gajeren tsaki yaja, yana daga zaune ya mika hannu ya fisgota, razana tayi har sai da wayar ta yafad'i kasa.
ido ta waro jin ta a kan cinyarsa.
gaba d'aya ta firgita tarasa ina zatasa kanta.
shiko ko a jikin ta,
ya tura hannunsa tacikin hijab d'in ta, yana lalub'o ta inda zip d'in yake.
d'aya hannunsa kuma yaja hijab d'in ya haura da shi sama har zuwa kafad'ar ta.
kana ya zuge mata zip d'in.
da sauri ta mike tasaki hijab d'in ya rufe ta, kana ta taka da sauri tabi ta kofar da ta shigo ta fice daga parlour'n nasa.
baki ya tab'e ganin yadda ta wani birkice, ya gyara zamansa ya cigaba da abun da yake.
Tana shiga bedroom d'in ta tasauke numfashi.
sai kuma ta turo baki gaba, ta cire hijab ta shige bathroom.
tana shiga ta cire rigarar tayi wurgi da shi, dan yabata haushi, ta cire underwear da pant ta tara ruwan d'umi cikin bathtub ta shige ciki tasoma wanka.
kiran Miemie ne ya shigo wayarta, Miemie ce ta
"Kiyi sauri ki fito Feeryal gamu mun fito."
ta ce "Tom."
ta sauke wayar, tayi ta lalawai, Miemie tayi ta kiranta a waya tayi ta ce mata gatanan fitowa, daga bisani ta ce mata itafa su Mommy take tsoron abun da zasuje su mata.
Miemie ta ce
"Ina ruwanki da su muna gefe suna gefe."
kai ta girgiza kana ta ce
"Gani fitowa."
sai sannan ta d'auko ashoben nasu tasaka pant da underwear batare da ta sa bra ba, tayi tayi ta tasaka doguwar rigar tasama takasa, dole sai ta kasa ta saka ta janyo sama ya wuce da kyar.
d'inkin ya kamata sam bataji dad'i ba, dan bata saba sa kayan daya matse ta ba.
ta d'au gyale ta saka akan ta,
ta zura takalmi mara tudu sosai.
ta d'an feshe jikin ta da turare ba masu karfi ba.
kana ta d'au handbag da wayan ta fita..
Tana fita ta hangoshi yana fito daga gefen sa,
tana kokarin wucewa yayi mata alama da hannu ta koma ciki.
tsayuwa tayi kamar zatayi kuka, takuma duban shi ya tsare ta da ido, fuskarsa bawasa.
kasa tayi da kanta tana jin hawaye na taruwa mata, sai dai ta kasa iya kuma kallon sa.
a hankali ta juya ta koma ciki ta fad'a saman bed.
Sai da yaga shigewar ta kafin ya fita.
motoci nata fita da mutane yawanci a daren zasu wuce, dan daga gurin dinner ango da amarya zasu wuce Jos da wasu daga cikin 'yan biki da yawa.
dan akwai wani gaggarumin shagalin da za'a gudanar a washegari a can Jos d'in.
tuni anyi bukin jiri na jiran su 11:30 zasu tashi, shi yasa 11 za'a tashi a gun dinner.
Daddy da ya fito daga side d'in Aunty ya tsaya suna sallama da wasu 'yan'uwan shi.
Abdulrahim ya karaso gurin san da motar ba'in ya tashi.
Daddy ya dube shi tare da amsa gaisuwar da yake masa,
ya ce
"Ina Feeryal ga 'yan'uwan ta nan duk kowa yafita za'a tafi."
shiru ya yi baiyi magana ba
Daddy yakuma duban sa tare da karantar sa kana ya ce
"Idan kai bazakaje ba, to ita kabarta taje, akan me yasa zaka hanata, wata kila tasa ranta tana son zuwa."
nan ma baiyi magana ba sai nad'e hannayensa da yayi a kirji.
A b'angeren Feeryal wayanta tajanyo tana share d'an guntun kwallan da suka zubo mata.
ta danna numman Aunty, tana d'agawa cikin muryar shagwab'a ta ce
"Ammie Sahab ya hanani zuwa."
da sauri Aunty ta ce
"Ban amince kiyi gardama ba ki zauna, ban sanki da kafiya ba kar naji kinyi masa gardama"
baki ta cuno ta sauke wayar.
itafa ba gun biki take son zuwa ba so take tasamu ta fita taje b'angaren Ammien nata..
da sauri ta kalli kofa jin an turo kofar.
daga bakin kofar ya tsaya ya ce
"Ki tashi ki sa hijab kije."
aiko bai rufa baki ba ta mike.
ya tab'e baki yajuya.
babban hijabin sallar ta ta zura tayi waje.
Yana tsaye daga sama yana hango cikin gidan.
motoci duk sun gama tafiya.
akan idon sa ta shige sashin Aunty.
Aunty ta bud'e baki cike da mamakin ganin ta ta ce
"Ke Feeryal bana ce kar ki fito ba."
"Ammie shi yace naje."
"Feeryal yaushe kika koyi karya?."
"Allah Ammie da gaske Sahab shi ya ce nasa hijab naje."
Aunty tayi shiru tana nazartar ta kana ta ce
"To me ya hanaki binsu Miemie ku tafi kika zo nan?."
zama tayi kan kujera tana cewa
"Nifa dama Ammie ba zuwa zanyi ba ni bazan je gurin dinner ba."
"Ai ko sai ki tashi ki koma d'akin ki, tun da ba tafiya zakiyi ba."
"Ayya Ammie kibari sai anjima, idan suka dawo sai na koma, nima nayi dinner na anan."
tayi maganar tana cire hijab d'in.
Aunty tayi murmushi tana girgiza kai....karfe goma nayi tace ta tashi ta tafi dare ya yi.
Feeryal ta shagwab'e fuska,
"Ammie kaina ciwo yake min kuma ina jin yunwa."
Aunty ta ce
"To tashi maza mijin ki likita, shi yasan maganin da ya dace ya baki,
fad'a min dai yanzu me kike son ci, sai na dafa na baiwa Baba Rabi ta kawo miki yanzu,
gobe idan Allah ya kaimu ma ki huta na d'auke miki girkin gobe duka, ni zan dafa nabayar a kawo miki, kinji ko 'yammatan Ammie."
takuma shagwab'ewa tana fad'in
"Faten dankali da kifi kuma zan jira kiyi."
dakyar talallab'ata tace yanzu zatayi tabada akawo mata.
suka fito ta yi mata rakiya har bakin side d'in su sai da taga shigarta kafin ta juyo.
Feeryal na shiga d'aki ta kwab'e hijab tashiga kokarin cire kayan jikinta, dan ba karamin damunta yake ba.
tayi-tayi ta cire ta gagara,
tarika kokawa da rigar kamar zatayi kuka.
da sauri ta shige bathroom jin fitsarin da take ji yana kokarin fitowa, tayi ta fito tacigaba da kokarin cire rigar ga zip d'in rigar can sama kuma yayi tauri sosai.
zama tayi bakin gado tana maida numfashi kamar wacce tayi wani aikin.
ta janyo waya ta dannan number Aunty tana d'agawa ta ce
"Ammie na kasa cire rigar, zanzo ki jamin zip d'in."
Aunty ta ce
"Me ya kaiku yin matsastsen d'in ki, karki fito ai ba ke kad'ai bace a side d'in mijinki na nan sai kije yaja miki, haka kawai kamatse kanka da kanka kahana kanka jan numfashi da kyau."
Aunty ta kashe wayar Feeryal ta kwab'e fuska kamar zatayi kuka.
taya za'ayi ma taje tace yaja mata zip ai gara ta kwanta haka.
ta gyara ta kwanta.
tana sa kafad'arta akan gado taji rigar yana cizon ta, gashi ko numfashi mai dad'i bata iya ja dan bata sama ba sa irin matsastsun kayan nan ba, uwa uba kuma bata iya bacci da kaya masu nauyi ba, in ba sleeping dress ba.
ta mike da sauri ta d'au hijap ta fito.
tana sa kafarta a farfajiyar gidan tajiyo kukan kule, ai da gudu ta koma ciki..
ta haye gado ta kwanta.
ta matse ido tana fatan bacci ya d'auke ta.
amma ina tamkar mistsinin ta ake tacikin kayan,
idan ya manne da jikinta har wani radad'i take ji.
zunbur ta mike tana sosa jikinta idonta sun cika da kwalla.
tana son tafita taje Ammien ta ta taimaka mata tacire rigar, amma tana tunanin mage a waje.
kwalla ta share in har ba kwana zaune take son yi ba to tana bukatar rigar nan yabar jikin ta.
ke nan bata da zab'in da ya wuce taje ya taimaka yazuge mara zip d'in.
kwalla ta share ta d'auki hijab ta saka kana ta fito a hankali tana waige-waige, dan a tsoro take sai gani take kamar zata gamu da magen..
Kofar da ke sakanin gefen ta da nashi, wanda take ganin duk san da zai shigo tanan yake shigowa.
a hankali ta isa jikin kofar ta bud'e jiki a sanyaye.
ido ta zubawa corridor daya bayyana a gana ta, bata tab'a kawo kanta nan ba.
a hankali tabi cikinsa ta taka har zuwa wata kofar da ta gani a can gaba, nan ma ta bud'e a hankali sai da ta d'anyi jim kafin tazura kafafunta ta shige ciki.
wani sassanyan kamshi ne gami da sanyi ya bugeta, har sai da ta d'an kame jikinta ta nad'e hannunta cikin hijab, dan ba kad'an ba sanyin ya rasa fatarta ya zarce har cikin jikinta.
gani tayi ta bayyana cikin wata duniya.
katon parlour mai d'auke da kayan alatu na musamman.
ido ta shiga bazawa cikin katafaren parlour'n.
can ta hango sa zaune saman kujera idanunsa akan system d'in da ke gabansa.
takai 10snd tsaye
kana a hankali tashi d'aga kafarta tana takowa cikin parlour'n.
yayin da take dad'a jin sanyin na kuma shi garta.
tun shigan ta idanunsa a kan abun da yake bai d'ago ba.
a d'an nesa da shi ta tsaya d'an kallon shi tayi kana ta sunkiyar da kanta tana wasa da bakin hijabin ta.
a hankali cikin muryarta mai sanyi ta ce
"Um dan Allah Sahab dama..dama..dama umm."
sai kuma tayi shiru.
a sannu ya d'ago idanunsa ya sauka cikin nata, da sauri ta janye nata idanun takuma yin kasa da kanta.
mai da idanunsa yayi kan laptop d'in.
hannu ta yarfe kana ta ce
"Dama.um dan Allah dama so nake kad'an taimaka kajamin zip..zip d'in riga ta, nakasa cirewa ne, kuma bazan iya bacci da shi ba."
tsai da abun da yake yayi kana ya d'ago, kasa takuma yi da kanta.
5 second idanunsa a kanta, sai kuma ya gyara zamansa ya yi mata alama da hannu ta zo......!
A hankali tashiga d'aga kafarta, ta maso in da yake.
sai kuma taja ta tsaya
kanta a kasa tana wasa da 'yan yatsun ta ta cikin hijab.
"You are waisting my time."
ya fad'a yana gimtse fuska.
a hankali ta juya bayan ta a sannu tad'an ja hijab d'in tayi sama da shi.
ratan da ke sakanin su yakai taku uku, sai noke-noke take takasa jan hijab d'in duka.
gajeren tsaki yaja, yana daga zaune ya mika hannu ya fisgota, razana tayi har sai da wayar ta yafad'i kasa.
ido ta waro jin ta a kan cinyarsa.
gaba d'aya ta firgita tarasa ina zatasa kanta.
shiko ko a jikin ta,
ya tura hannunsa tacikin hijab d'in ta, yana lalub'o ta inda zip d'in yake.
d'aya hannunsa kuma yaja hijab d'in ya haura da shi sama har zuwa kafad'ar ta.
kana ya zuge mata zip d'in.
da sauri ta mike tasaki hijab d'in ya rufe ta, kana ta taka da sauri tabi ta kofar da ta shigo ta fice daga parlour'n nasa.
baki ya tab'e ganin yadda ta wani birkice, ya gyara zamansa ya cigaba da abun da yake.
Tana shiga bedroom d'in ta tasauke numfashi.
sai kuma ta turo baki gaba, ta cire hijab ta shige bathroom.
tana shiga ta cire rigarar tayi wurgi da shi, dan yabata haushi, ta cire underwear da pant ta tara ruwan d'umi cikin bathtub ta shige ciki tasoma wanka.