Sashe 74
El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hajiya sai faman gyaran amarya take, uwani na faman washe baki, ashe hajiya na sonta take boye mata, lallai jiddah tayi mata baqin ciki domin bata mata wannan gyaran ba shiyasa akace kishiya abin tsoro da gudu ce, wai uwani ke cewa kishiya abin gudu ce🤔
Duk ranar da hajiya ta manta ba ta bata ta sha ba ita da kanta take tuna mata, hajiya bata mamakin rashin kunya irin na uwani tunda tasan ko wacece ita.
Ba suyi wani dogon biki ba kasancewar kowa yasan uwani baxawara ce🤪, duk bikin da ake jiddah ta halarta kuma sosai ta bada gudumuwar ta, banan ma taje da jiddah ta gayamata,
Ta bawa uwani gudumuwar hadaddiyar cooler mai kyau da tsada, amma uwani ta rena.
An gaya maki abbana bai siyamin inda xan sakawa mijina abinci ne, qila ma kin xubo kayan mallakar miji aciki na xuba abinci na basa ki mallake min shi.
Banan tace subhanallah anty uwani, kin manta ina da aure bayan wannan ma ni ban taba bin boka ko malami ba a rayuwata, ashe har yanxu baki canxa hali ba.
Uwani ta tashi tana fadin, me kike nufi kina nufin ina da wani mugun hali ne, waye ma ya gayyace kixo min biki, banda baqin ciki ki rasa abin bani sai wannan cooler ni kayan mata nake so na gyara kaina kar na xamo bora a gaban miji.
Banan girgixa kanta kawai tayi sauqin ta ba kowa a dakin sai su biyu kawai da ta kunyata a yau, banda anty jiddah me ma xai saka taxo bikin uwani, jiddah ta shigo da sallama tana fadin hayaniya nake ji me ya faru?
Uwani tayi caraf tana fadin, anty jiddah wai banan fa mai aikin mu ta waye har tayi arxikin da xata kawo min gudumuwa dubi fa.
Jiddah tace laifine dan ta kawo maki? Ita da ta tashi yin nata nawa kika bata, ba dan ni ba kina tunanin ma xaki qara ganin banan, meyasa kike haka, meyasa har yanxu kin kasa nutsuwa kisan me kike?
Kina goyon bayanta kenan, ni xan dauka haka ba dan halin ta ba albarkacin kine, ni duk mai min baqin ciki na gano sa Allah bana iya xama dashi.
Jiddah tayi caraf ta kwace cooler tana fadin baki isa ba, ta miqawa banan, koma da ita gida baxaki bata ba, idan kinyi niyar kyautarwa ne kibawa hajiya.
Banan ta karba tana fadin shikenan anty jiddah, uwani ta bita da kallo cikin mamaki da haushi dan tama rasa wane irin baqin ciki ne jiddah take mata haka, amma xasu hadu...
An daura auren yusuf da uwani, kuma a ranar xaa wuce da amarya.
Tun da aka xo daukar amarya ake ta daru taqi ta shiga mota ita lallai sai akan sabon vespa din ta xaa kaita gidan mijin ta.
Wai wace irin mata ce yusuf ya aura haka?cewar daya daga cikin mutanen da suka xo daukar amarya.
Dayar tace magana ne kawai banyi ba, amma tun ranar da muka xo kawo lefen ta na gane bata da kunya da nutsuwa, banda iskanci ina aka taba daukar amarya daga kaduna har abuja akan vespa?
Tsohuwar tace lallai da sake, wallahi da nasan tun farko matar da yusuf yake nema kenan da baxai aure ta ba, yanxu ma bata baci ba xai iya sakin ta.
Aa Inna dan Allah kiyi haquri, inaji yarinyar dama tun farko bata da nutsuwa anty ikram ta gayamana komai akanta shiyasa kika ga bata goyon bayan auren komai ma bata saka hannunta a ciki ba.
Inna tace amma meyasa tun farko baku sanar dani hakan ba, da ba abinda xai saka a daura wannan auren, ita ikram din ai bata taba gayamin ba.
Inna ai anty ikram xatayi maganin ta, tana tsoronta sosai, ki xuba idanu kawai kiyi kallo kada ki sakawa xuciyarki bacin rai.
Inna ta shige mota tana taunar goro cikin jin haushin uwani.
Lamarin uwani kuwa sai da aka kira abba kafin ta shiga mota amma sai da aka saka mata vespa a bayan motar tukunna, cewar baxataje ta barshi ba.
Jiddah bata tsaya daukar amarya ba tana can tare da masu gyaran gidan na uwani suna jiran isowar su.
Kuyanga Qaumi ce ta shigo dauke da airah tana kuka sosai,
'Anty jiddah, airah ta tashi daga barci sai kuka take taqi ta karbi abincinta.
Jiddah ta karbe ta tana fadin, kada kije nesa yanxu xan kira ki karbeta da tasha, saboda sun kusa isowa, ina sauran abokan xaman naki,
Ranki ya dade muna tare da su a waje,
'Yauwa, kije xan neme ki, ta fita,
Banan tace wai anty jiddah ni bansan wadannan kuyangun ba hala an canxa maki su ne.
Eh tuni sarki ya canxa min wadancan basa son aiki, shine ya bani Maryam, Hajja, Saina da Mom sadeeq.
Banan tace cab kice duk yan kayan baqin ciki ne aka hada ki dasu.
Jiddah murmushi kawai tayi.
Bayan wani lokaci sai ga motocin amarya sun iso, ana fitowa da uwani a mota ta cire mayafi tana kallon gidan da aka kawo ta, ba wanda ya lura da halin da take ciki sai da suka ji tana fadin,
Shiyasa nake son yusuf kwata kwata a rayuwarsa bashi da baqin ciki, duk wannan gidan nawa ne.
Wasu suka dauki salallami, wasu kuwa suka tabe baki tunawa da suka je da ita yanxu ta gaida iyayen yusuf sai da tayi makamancin irin wannan.
Sai aka rasa waye amarya aciki tun da suka shigo, jiddah tamkar ta nutse gurin saboda kunya, ta jawo uwani ta gyarta hade da kai mata rankwashi mai xafi a tsakiyar kai tana fadin uban waye ya gaya maki amarya na fito da fuskarta.
To baxan kalli gidan bane, gidana ko naki, banda baqin ciki miye n.... Jiddah ta qara bige mata baki.
'Na qara jin muryarki anan wlhy abba xan kira na gayamasa kinsan yanda kukayi kafin axo dake,
Akaje da amarya bakin gado aka xaunar da ita, wasu suka fita suna fadin bari muje muga gidannan kamar ba wanda muka sani ba an gyara sosai gashi an qayata gidan da kaya masu tsada, iyayen ta sunyi matuqar qoqari gsky.
Uwani najin haka ta miqe kar abarta baya gwanda taje ganin gidan ta tsare abinta kada wata tayi mata sata ta wuce da kayan kitchen din ta taji yanxu haka ake yi.
Jiddah ta maida ta da qarfin gaske ta xauna,
Wai baki da hankali uwani, ina xakije, kawaicin ma baxakiyi ba har su tafi.
'Anty jiddah xanje na tsare kitchen dina ne kada amin sata, abba ya siya min kaya masu tsada, baki ga gas dina yafi wanda kika siyawa banan ba idan aka dauke fa.
Cikin takaici jiddah tace to sai me dan an dauke, wallahi kika bata min rai dukan ki xanyi a gidannan.
Uwani tayi shiru tana tunxuro baki, sai ga hawaye suna bin kuncinta, jiddah tayi mata banxa, yau gata ita ke tsaron uwani ita bata taba ganin ana tsaron amarya ba, ta dubi uwani tana fadin,
Wai ke baki da qawaye ne, duk ina suke ko daya ban gani ba.
Cikin takaici tace bani dasu menene.
Jiddah tace au hakane fa, sam na manta da uwani nake magana wadda ke rayuwarta ita kadai.
Uwani ta tabe baki tana fadin ban gayyaci kowa ba duk yan baqin ciki ne, ashe na manta har ta kusa dani ma tana min baqin ciki saboda an kawo ni gidan mijina, kada ayi min snatching ace xaa auri mijina dan na auri mijin wata.
Jiddah ta tabe baki tana fadin, ai rijiya ba gurin wasan yaro bane, mijin wata da kika ga kin aura ai yafi qarfin ki shiyasa har kika kasa xaman aure dashi, wanda kika aura a yanxu ma ai sai da aka bisa da roqo da rarrashi akan has rufa asiri banda haka ai da kin tsinci hoton ki a gidan masallaci ana cigiyar mai so a kyauta.
Takaici ya hana uwani magana ta tashi ta leqa ta window dakin tana kallon harabar gidan kafin tace,
'Yauwa har yanxu vespa dina yana nan kafin yan baqin ciki suyi gaba dashi, na lura yana tsonewa mutane ido sosai...
Gidan yayi tsit yan kawo amarya duk sun watse ya rage jiddah kawai a gidan, ta xauna sosai tayi wa uwani nasiha game da aure, ta qara nuna mata wannan auren daban yake da irin wanda tayi a baya.
Cikin ikon Allah kuwa uwani ta saurareta cikin nutsuwa har take ganin jiddah mai son ta ce bata mata baqin ciki a rayuwarta.
Ganin dare nayi sosai ga el'mustapha sai faman kiranta yake ya sakata shirin tafiya, ga mamakin ta sai ji tayi uwani na fadin.
Yanxu anty jiddah shima yusuf xamuyi irin wannan abin da mukayi da yaya el'mustapha kenan,
Cikin rashin fahimta jiddah tace menene uwani.
Tace ai kinsan da mukaje Lagos har jamcy ta bani pills na saka masa a juice, ai sau daya mukayi bamu qara ba, amma yusuf shima sai na saka masa pills dinne?
Subhanallah uwani, wannan abin sirri ne da baa so kowa yaji, tsakanin ki ne da mijin ki, ki riqe sirrin auren ki karki qara fadawa kowa, maganar ki saka masa pills kada na qara jin wannan, kin manta kece mace, shi xai neme ki ai.
Uwani ta washe baki tana fadin, ai anty jiddah hajiya ta bani wani abu nasha, shikenan inajin jikina ba dadi, ya xanyi yanxu.
Jiddah xata yi magana kiran el'mustapha ya shigo, tana dauka ya soma fada,
Ina hanya mijin jiddah, yanxu xan qaraso, baiyi magana ba ya tsinke wayar, sam bata bi ta kan uwani ba ta fice da sauri, a ranta tana tsoro kada su yi wani abu da yusuf uwani taje tana fadawa mutane.
Bayan fitar jiddah uwani taje tana qara duba gidan, taji dadin gidan sosai, taji ta qara son yusuf tunda bai hada ta xama da surayya ba, lallai el'mustapha bai son ta yana mata baqin ciki tunda ya hada ta xama da jiddah.
Tana xaune a falo ta tura masa test,
_cwt ni bana son wannan kaza da ake siyowa amarya, kifi nake so babba mai nama, ko daxu naci naman kaxa a gida bana so, ina ta jiranka tun daxu kayi sauri._
Duk ranar da hajiya ta manta ba ta bata ta sha ba ita da kanta take tuna mata, hajiya bata mamakin rashin kunya irin na uwani tunda tasan ko wacece ita.
Ba suyi wani dogon biki ba kasancewar kowa yasan uwani baxawara ce🤪, duk bikin da ake jiddah ta halarta kuma sosai ta bada gudumuwar ta, banan ma taje da jiddah ta gayamata,
Ta bawa uwani gudumuwar hadaddiyar cooler mai kyau da tsada, amma uwani ta rena.
An gaya maki abbana bai siyamin inda xan sakawa mijina abinci ne, qila ma kin xubo kayan mallakar miji aciki na xuba abinci na basa ki mallake min shi.
Banan tace subhanallah anty uwani, kin manta ina da aure bayan wannan ma ni ban taba bin boka ko malami ba a rayuwata, ashe har yanxu baki canxa hali ba.
Uwani ta tashi tana fadin, me kike nufi kina nufin ina da wani mugun hali ne, waye ma ya gayyace kixo min biki, banda baqin ciki ki rasa abin bani sai wannan cooler ni kayan mata nake so na gyara kaina kar na xamo bora a gaban miji.
Banan girgixa kanta kawai tayi sauqin ta ba kowa a dakin sai su biyu kawai da ta kunyata a yau, banda anty jiddah me ma xai saka taxo bikin uwani, jiddah ta shigo da sallama tana fadin hayaniya nake ji me ya faru?
Uwani tayi caraf tana fadin, anty jiddah wai banan fa mai aikin mu ta waye har tayi arxikin da xata kawo min gudumuwa dubi fa.
Jiddah tace laifine dan ta kawo maki? Ita da ta tashi yin nata nawa kika bata, ba dan ni ba kina tunanin ma xaki qara ganin banan, meyasa kike haka, meyasa har yanxu kin kasa nutsuwa kisan me kike?
Kina goyon bayanta kenan, ni xan dauka haka ba dan halin ta ba albarkacin kine, ni duk mai min baqin ciki na gano sa Allah bana iya xama dashi.
Jiddah tayi caraf ta kwace cooler tana fadin baki isa ba, ta miqawa banan, koma da ita gida baxaki bata ba, idan kinyi niyar kyautarwa ne kibawa hajiya.
Banan ta karba tana fadin shikenan anty jiddah, uwani ta bita da kallo cikin mamaki da haushi dan tama rasa wane irin baqin ciki ne jiddah take mata haka, amma xasu hadu...
An daura auren yusuf da uwani, kuma a ranar xaa wuce da amarya.
Tun da aka xo daukar amarya ake ta daru taqi ta shiga mota ita lallai sai akan sabon vespa din ta xaa kaita gidan mijin ta.
Wai wace irin mata ce yusuf ya aura haka?cewar daya daga cikin mutanen da suka xo daukar amarya.
Dayar tace magana ne kawai banyi ba, amma tun ranar da muka xo kawo lefen ta na gane bata da kunya da nutsuwa, banda iskanci ina aka taba daukar amarya daga kaduna har abuja akan vespa?
Tsohuwar tace lallai da sake, wallahi da nasan tun farko matar da yusuf yake nema kenan da baxai aure ta ba, yanxu ma bata baci ba xai iya sakin ta.
Aa Inna dan Allah kiyi haquri, inaji yarinyar dama tun farko bata da nutsuwa anty ikram ta gayamana komai akanta shiyasa kika ga bata goyon bayan auren komai ma bata saka hannunta a ciki ba.
Inna tace amma meyasa tun farko baku sanar dani hakan ba, da ba abinda xai saka a daura wannan auren, ita ikram din ai bata taba gayamin ba.
Inna ai anty ikram xatayi maganin ta, tana tsoronta sosai, ki xuba idanu kawai kiyi kallo kada ki sakawa xuciyarki bacin rai.
Inna ta shige mota tana taunar goro cikin jin haushin uwani.
Lamarin uwani kuwa sai da aka kira abba kafin ta shiga mota amma sai da aka saka mata vespa a bayan motar tukunna, cewar baxataje ta barshi ba.
Jiddah bata tsaya daukar amarya ba tana can tare da masu gyaran gidan na uwani suna jiran isowar su.
Kuyanga Qaumi ce ta shigo dauke da airah tana kuka sosai,
'Anty jiddah, airah ta tashi daga barci sai kuka take taqi ta karbi abincinta.
Jiddah ta karbe ta tana fadin, kada kije nesa yanxu xan kira ki karbeta da tasha, saboda sun kusa isowa, ina sauran abokan xaman naki,
Ranki ya dade muna tare da su a waje,
'Yauwa, kije xan neme ki, ta fita,
Banan tace wai anty jiddah ni bansan wadannan kuyangun ba hala an canxa maki su ne.
Eh tuni sarki ya canxa min wadancan basa son aiki, shine ya bani Maryam, Hajja, Saina da Mom sadeeq.
Banan tace cab kice duk yan kayan baqin ciki ne aka hada ki dasu.
Jiddah murmushi kawai tayi.
Bayan wani lokaci sai ga motocin amarya sun iso, ana fitowa da uwani a mota ta cire mayafi tana kallon gidan da aka kawo ta, ba wanda ya lura da halin da take ciki sai da suka ji tana fadin,
Shiyasa nake son yusuf kwata kwata a rayuwarsa bashi da baqin ciki, duk wannan gidan nawa ne.
Wasu suka dauki salallami, wasu kuwa suka tabe baki tunawa da suka je da ita yanxu ta gaida iyayen yusuf sai da tayi makamancin irin wannan.
Sai aka rasa waye amarya aciki tun da suka shigo, jiddah tamkar ta nutse gurin saboda kunya, ta jawo uwani ta gyarta hade da kai mata rankwashi mai xafi a tsakiyar kai tana fadin uban waye ya gaya maki amarya na fito da fuskarta.
To baxan kalli gidan bane, gidana ko naki, banda baqin ciki miye n.... Jiddah ta qara bige mata baki.
'Na qara jin muryarki anan wlhy abba xan kira na gayamasa kinsan yanda kukayi kafin axo dake,
Akaje da amarya bakin gado aka xaunar da ita, wasu suka fita suna fadin bari muje muga gidannan kamar ba wanda muka sani ba an gyara sosai gashi an qayata gidan da kaya masu tsada, iyayen ta sunyi matuqar qoqari gsky.
Uwani najin haka ta miqe kar abarta baya gwanda taje ganin gidan ta tsare abinta kada wata tayi mata sata ta wuce da kayan kitchen din ta taji yanxu haka ake yi.
Jiddah ta maida ta da qarfin gaske ta xauna,
Wai baki da hankali uwani, ina xakije, kawaicin ma baxakiyi ba har su tafi.
'Anty jiddah xanje na tsare kitchen dina ne kada amin sata, abba ya siya min kaya masu tsada, baki ga gas dina yafi wanda kika siyawa banan ba idan aka dauke fa.
Cikin takaici jiddah tace to sai me dan an dauke, wallahi kika bata min rai dukan ki xanyi a gidannan.
Uwani tayi shiru tana tunxuro baki, sai ga hawaye suna bin kuncinta, jiddah tayi mata banxa, yau gata ita ke tsaron uwani ita bata taba ganin ana tsaron amarya ba, ta dubi uwani tana fadin,
Wai ke baki da qawaye ne, duk ina suke ko daya ban gani ba.
Cikin takaici tace bani dasu menene.
Jiddah tace au hakane fa, sam na manta da uwani nake magana wadda ke rayuwarta ita kadai.
Uwani ta tabe baki tana fadin ban gayyaci kowa ba duk yan baqin ciki ne, ashe na manta har ta kusa dani ma tana min baqin ciki saboda an kawo ni gidan mijina, kada ayi min snatching ace xaa auri mijina dan na auri mijin wata.
Jiddah ta tabe baki tana fadin, ai rijiya ba gurin wasan yaro bane, mijin wata da kika ga kin aura ai yafi qarfin ki shiyasa har kika kasa xaman aure dashi, wanda kika aura a yanxu ma ai sai da aka bisa da roqo da rarrashi akan has rufa asiri banda haka ai da kin tsinci hoton ki a gidan masallaci ana cigiyar mai so a kyauta.
Takaici ya hana uwani magana ta tashi ta leqa ta window dakin tana kallon harabar gidan kafin tace,
'Yauwa har yanxu vespa dina yana nan kafin yan baqin ciki suyi gaba dashi, na lura yana tsonewa mutane ido sosai...
Gidan yayi tsit yan kawo amarya duk sun watse ya rage jiddah kawai a gidan, ta xauna sosai tayi wa uwani nasiha game da aure, ta qara nuna mata wannan auren daban yake da irin wanda tayi a baya.
Cikin ikon Allah kuwa uwani ta saurareta cikin nutsuwa har take ganin jiddah mai son ta ce bata mata baqin ciki a rayuwarta.
Ganin dare nayi sosai ga el'mustapha sai faman kiranta yake ya sakata shirin tafiya, ga mamakin ta sai ji tayi uwani na fadin.
Yanxu anty jiddah shima yusuf xamuyi irin wannan abin da mukayi da yaya el'mustapha kenan,
Cikin rashin fahimta jiddah tace menene uwani.
Tace ai kinsan da mukaje Lagos har jamcy ta bani pills na saka masa a juice, ai sau daya mukayi bamu qara ba, amma yusuf shima sai na saka masa pills dinne?
Subhanallah uwani, wannan abin sirri ne da baa so kowa yaji, tsakanin ki ne da mijin ki, ki riqe sirrin auren ki karki qara fadawa kowa, maganar ki saka masa pills kada na qara jin wannan, kin manta kece mace, shi xai neme ki ai.
Uwani ta washe baki tana fadin, ai anty jiddah hajiya ta bani wani abu nasha, shikenan inajin jikina ba dadi, ya xanyi yanxu.
Jiddah xata yi magana kiran el'mustapha ya shigo, tana dauka ya soma fada,
Ina hanya mijin jiddah, yanxu xan qaraso, baiyi magana ba ya tsinke wayar, sam bata bi ta kan uwani ba ta fice da sauri, a ranta tana tsoro kada su yi wani abu da yusuf uwani taje tana fadawa mutane.
Bayan fitar jiddah uwani taje tana qara duba gidan, taji dadin gidan sosai, taji ta qara son yusuf tunda bai hada ta xama da surayya ba, lallai el'mustapha bai son ta yana mata baqin ciki tunda ya hada ta xama da jiddah.
Tana xaune a falo ta tura masa test,
_cwt ni bana son wannan kaza da ake siyowa amarya, kifi nake so babba mai nama, ko daxu naci naman kaxa a gida bana so, ina ta jiranka tun daxu kayi sauri._