← Book details El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 80

Sashe 46

El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tsayuwar me kike yi anan,

Ta rikice aa dama xan shigo ne ince maki nagama sharar na kwashe Ma, cewar uwani tana sosa kanta cikin washe baki😁

Kece kika bata min kaya, yaushe Ma kika shigo dakin?

Ni😯, yaushe bani bace, kinsan bana shigowa ai, haba hajiya sai na shigo dakinki bada ixini ba, cab ai ni bana xuwa dakin mutum saboda gujewa ganin mugun abu, ni banxo ba dan Ma karna ga kayan baqin ciki.

Tayi shiru tana kallonta kafin tace wannan scissor din na hannunki na menene, ni xaki Ma qarya.

Uwani ta xare idanu, ta hadiye yawu da kyar kafin ta sami abin fada,

Hajiya tsaya kiji dauko shi nayi yanxu inxo in tambayeki xan iyawa flowers dincan na waje aski, naga leaves ya masu yawa.

Aski kuma? Me kike nufi kina son raina min wayo ko, wlhy sai kinyi dana sani bata min wannan rigar, kinsan daga inda na siye ta kuwa?

Uwani ta girgixa kai tana kallonta,

Saboda ina sauri ana jirana ne, amma kisa a ranki yau baxakiyi barcin kirki a gidannan ba xan ta axabtar dake ne sai na fanshi kudin ta a jikinki, ta juya a fusacce ta ciro wata rigar,

Uwani na tsaye a gun kamar statue har ta shirya ta dauki key da wayarta ta fice tana amsa waya.

A hankali ta sauke numfashi, koma me xaki min baxai hana gobe na rama ba har sai kin gaji kin sallameni, yar iska kawai mai yin lalata.

Ta matsa tana kallon abinda taga ta shafa tsakiyar cinyoyinta,

Qilama iskanci xataje yi, gobe baxaki qara ba, yaji xan xuba masa, in kin dawo kin hanamin barci kika shafa kema na hanamiki barci, do me I do you man no go vex, if you touch me I touch you man no go vex, if you beat me you go suffer man no go vex, ta fita ta dauko yajin taxo ta xuba aciki ta gauraye ta fita tana dariya.

*

Sai safa da marwa yake a corridor a asibitin, hannunsa goye a bayansa,

A hankali lips dinsa ke motsawa wanda idan baka qura masa ido ba baxaka taba ganin motsin su ba,

Banda addua babu abinda yake, gabansa sai tsananta bugawa yake,

Anti yusrah na kishingide barci ya dauke ta ita da hajiya, tun jiya da dare basu runtsa ba,

Jaririyar kuwa kuka take banan na rarrashinta amma kacokan idanunta na kan el'mustapha, duk wani feelings akansa ya dawo mata batasan dalili ba,

Kukan jaririyar ya saka el'mustapha juyowa, carab suka hada ido, ya bata fuska bayan ya dauke kansa da sauri,

Ya qaraso ya karbi jaririyar, a qirjinsa ya rungumeta sosai yana jijjiga ta amma sai kuka take ba kakkautawa,

Yunwa take ji ya sani, lips dinshi ya tura mata a baki ta fara tsotsa da sauri.

Ya qura mata ido yana kallonta, son yarinyar na shiga cikin jikinsa har yafi wanda yayi wa twins a baya, duk kukan nan da take ba ko digon hawaye a fuskarta, bai san sanda dariya na subulce masa ba, aikuwa ta saki wani kukan da sauri ya maida lips din yana tafiya a hankali gurin wasu nurse's ko akwai wani taimako da xasu masa na madarar da xai siya mata.

Bai jima da tafiya ba ya dawo lokacin har tayi barci tana kafadarsa,

Ganin hajiya ta tashi ya miqa mata ita, ya juya yana kallon banan cikin lalabar aljihunsa,

Kudi ya ciro ya bata tare da wata takarda,

Dai dai lokacin Dr Aiman Merah ya fito tare da wasu nurses a bayansa fuskar nan tasa a daure kamar kullum.

Bai gayawa banan kome xata siyo ba ya juya da sauri gabansa na faduwa ya tunkare sa, su hajiya ma duk suka taso bayan ta goya yarinyar.

Hannu dr merah ya daga masa wanda ya saka el'mustapha tsayawa cak cike da mamaki,

Yana kallo fadawa ke cire masa rigar aikin da ya shiga da ita kafin su saka masa doguwar alkyabba, suka nada masa rawanin sa cikin sauri, nan take ya fito yarima merah.

El'mustapha na tsaye cikin haushi wanda ke ta lafiyar matarsa ina ruwansa da wata sarauta, Merah ya soma tafiya a hankali fadawa suka take masa baya tare da wasu nurse's,

Alama suka Ma el'mustapha da ya biyo bayan su,

Ba yanda xaa yi Dr Merah ya fito tiyata ko duba patient ya tsaya yima bayani batare da ka same shi office na shi ba koda kuwa mutuwa ce, bai damu ba, a ganinsa mulkinsa da sarautar sa duk sun xube.

Suna shiga office din duk suka fice ya rage el'mustapha da Dr merah.

Tsaki yaja a xuciyarsa kusan minti goma da xamansa a office din amma yaqi ya masa mgn, yana son sanin condition din jiddah is d work successful or not amma mutumin yaqi magana saboda mulki.

El'mustapha ya xuba mashi idanu hade da sakin uban tagumi yana kallon ikon Allah,

Abinda el'mustapha bai gane ba idan xasu shekara a gurin batare da ya fara tambayar dr merah lafiyar jiddah ba baxai taba gayamasa ba, halin sa ne, a jinin sa yake, ka fara tambayarsa kafin ya bama bayanin komai.

Rashin sani ya saka el'mustapha xuba mashi idanu yana kallonsa yaga qarshen girman kan nasa.

Fiye da minti goma xaune a wurin ba wanda yayi magana a cikin su.

Tashi el'mustapha yayi ya fice daga office din a fusacce, Dr Merah yabi bayansa da kallo yana tabe baki.

Yana fitowa hajiya da anty yusrah suka tare sa,

Ya akayi ne el'mustapha? An nasara ko?

Ya bata fuska yana Jan tsaki mai cike da takaici,

Taya xan sani wannan likitan mai baqar sarautar tsiya yaqi yamin mgn ballantana naji halin da jiddah take ciki.

Hajiya tace oh Allah munga sun fito da ita a lullube, hankalina ya kasa kwanciya el'mustapha, kayi haquri kaje ka qara tambayarsa meke faruwa da yar'mu.

El'mustapha ya shafi sumar sa, baxai je ya qara tambayarsa ba ai komai mulki da sarautar likita baxaiyi akan patient din sa ba, sai ya koma fada yayi wannan mulkin amma baa asibiti ba, ya furxar da iska a bakinsa yana kallon hajiya.

Ina suka je da jiddah,

Wani daki suka ajiye ta cewar hajiya tana tafiya suna biye da ita a baya.

Ta window suke kallonta, baxasu iya gane komai a tare da ita ba kasancewar tana nesa dasu sosai.

Indai tana raye alhamdulillah, ba dole sai ta rayu da qafar ba, xan iya xama da ita a hakan, ya juya ya soma tafiya a hankali, anty yusrah tabi bayansa.

Hannunsa ta riqo bayan ta kira sunansa,

Juyowa yayi yana kallonta ga mamakinta idanunsa cike suke da kwallah,

Tace meyasa el'mustapha, jiddah xata tashi insha Allah kuma da qafafunta, ganinta haka kwance ba shi xai saka mu cire tsammanin daga gare ta ba, be a man pls, idan kai da kake namiji kayi kuka mu kuma muyi me?

Yace kin lura da jiddah bata motsi anty yusrah, baki ga yanda suka ajiye ta ba kamar gawa, meyasa suka ajiye ta anan, just tell me anty yusrah me suke nufi da jiddah, baxan yarda ba idan suka kashe min mata.

Gabanta ya tsananta faduwa, taja hannunsa da suka suka fito cikin asibitin ganin yanda mutane suke kallonsu, juyo dashi tayi hade da saka tafin hannuwanta ta riqo fuskarsa tana kallon sa.

Me yake damun ka el'mustapha? Yaushe ka canxa ka dawo haka mai xafin rai, da nasan jiddah da xafin rai da nace daga ita ne amma jiddah kowa ya san ta da sanyin rai, idan mutuwa jiddah tayi meyasa xakayi qarar su, meyasa baxakayi tawakkali a xuciyar ka ba, meyasa kake tunanin baxaka iya rayuwa sai da jiddah ba, ka manta wanda yayi ta yayi mu ya fimu son ta, baka tunanin lahirar ta fiye mata wannan duniyar da duk abinda ke cikinta, ko kana nufin baxaka yi imani da abinda Allah ya yanke akan ka ba, mama ta mutu ka haqura ballantana jiddah, wace irin shaquwa ce tsakanin ka da ita wacce bakayi da mama ba?

A hankali ya sauke ajiyar xuciya bayan ya janye fuskarsa daga riqon da tayi masa, kallon ta yayi,

But why wannan likit..... Tayi saurin katse sa,

Is ok ni xanje na tambayesa, wait for me, ta juya tana tafiya, binta yayi da idanu jikinsa a sanyaye kafin ya nemi guri ya xauna, mutane yake kallo dake shige da fice.

Assalamu Alaikum, tayi sallama cikin muryarta mai sanyi,

Batare da ya dago ba ya amsa sallama cikin isa da taqama,

Bata jira ixini ba ta shiga ta xauna tana kallonsa, duk abin nan da take ko sau daya bai kalle ta ba, ya maida hankali sosai akan laptop dinsa,

Ta tabe baki bayan taja numfashi,

Tace sannu da aiki, naxo ne kan maganar patient din da muka kawo Hauwa Ahmed, ko a wane hali take ciki.

Kallo daya yayi mata ya maida hankalinsa kan abinda yake yi batare da yayi magana ba kuma bashi da niyar yin haka.

Ta tsare sa da idanu cikin takaici, meyasa maxa masu kyau da mulki suka fiye wulaqanci da taqama, kamar ba wanda take magana da shi ba, tana da xafin xuciya ba kamar el'mustapha ba, ta bata fuska sosai tana fuskantar sa,

Allah yasa wanda nake magana dashi is not dump, ba kallonsa naxo yi ba ko son xama dashi halin da yar uwata take ciki nake son sanin.

Murmushi yayi amma bai dago ya kalle ta ba, su dai mata halin su daban ne, wannan da xata gane da ta daina daga masa murya kada ta fasa masa dodon kunne, dole xai kulata cos yana respecting mace ko ya take kuma a duk inda take.

Kallon ta yayi yana ajiye laptop din,

Yace Hauwa is ok, xata sami sauqi insha Allah, addua kawai ake buqata da aikin da akayi mata domin ni baxan iya tada ta tayi tafiya ba sai da ikon Allah, but am sure the work is successful.

Yusrah ta saki murmushi tana sauke ajiyar xuciya,

Yace matsalar har yanxu bata farfado ba amma wannan ba babbar matsala bace, nayi tunanin kamar alluran da akayi mata ne basu sake ta ba, amma mgnr gaskiya idan tayi awa biyar a hakan bata motsa ba sai dai ayi haquri,

Gabanta ya tsananta bugawa, hankalinta ya tashi,
Chapter 46 · 0% Book details