Sashe 3
El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hakan ba qaramin sosa xuciyar jidda yayi ba, domin ba abinda take buqata a yau kamar mijinta, tafi kowa sanin elmustapha yana daya daga cikin irin maxan nan da basu cika neman mace akai akai ba, sai sufi sati a haka bai damu ba amma romance tana samu sosai domin yafi sonshi sosai akan wancan, yau kam tana tsananin buqatar shi.
Gadon ta hau, yanda suka kwanta suna fuskantar juna sai dai shi idanunsa a lumshe suke, qirjinsa take kallo kafin ta dora hannu akai tana shafawa a hankali, bude idanuwansa yayi yana kallonta cikin yanayi na barci,
jiddana yau ban sami Hutu ba ko kadan, nagaji sosai, ban gayamaki ba har xaria naje yau.
Tayi shiru batare da tayi magana ba, amma yanda idanunta sukayi jaa kawai xai tabbatar maka na bacin rai ne, ta juya masa baya cikin fushi, hannu yasa ya juyo da ita hade da matse ta ajikinsa, hannunsa na yawo a doron bayanta,
'wannan kadai ya isa ki gane, ke kadaice macen dana keso, kin isheni a rayuwata, baxan iya lalurar wata macen ba, baxan iya son wata 'ya mace bayan jidda ba, bana son kina juyamin baya ko kadan.
Still bata tanka ba, banda sauke numfashi ba abinda take,
Ko baya buqata jidda ta nuna masa tata buqatar yana qoqarin sauke wannan nauyin just to make her happy and satisfied, baiga abinda jidda xata nema a gunshi ya hanata ba, ballantana karan kansa kacokan, ya sabule hannun rigar baccinta bayan ya hada bakinsa da nata.
Asuba ta gari *Jiddatulmusty*
*EL_MUSTAPHA*
HASKE WRITER'S ASSOCIATION
(home of experts and perfect writers)
Fertymerh Xarah 💞
11
'Washe garin ranar ga baki daya yinin ranar uwani bata fito ko falo ba tana can qunshe acikin daki.
Ganin shirun yayi yawa ne yasanya jidda xuwa ta dubata,
Kallo daya tayi wa uwani sai da hankalinta ya tashi, jikinta ya dauki rawa ta qarasa kusa da ita fuskarta dauke da mamaki take kallonta.
'meke damun ki uwani, meya same ki haka, idanunki sukayi jawur suka kumbura,
Uwani tayi qoqarin boye hawayen ta amma ina kamar kada ta tambayeta sai hawayen suka fara xarya, kukan me takeyi idan ba kukan so ba, rungumar da elmustapha yayi wa jidda jiya ba qaramin tarwatsa xuciyarta yayi ba, amma taya xata iya gayawa jidda saboda mijinta ne?
Ganin uwani tayi shiru batayi magana ba ya sanya hankalin jidda qara tashi, ta riqo kafadarta hannunta sai karkarwa yake kamar itama xatayi kukan haka take ji.
Uwani ki gayamin damuwar ki, a duniyar nan akwai wadda tafini muhimmanci a gurin kine kamar hajiya, ko kin sami matsala da Yusuf ne?
Uwani ta girgixa kanta cike da quncin jin ta ambaci wani Yusuf,
'ko matsala kika samu a makaranta? Nan ma ta girgixa kanta,
'to menene uwani, kiyi magana, ke ba arham bace da xan xauna rarrashin ki tun daxu jin matsalar ki, atleast ko menene ya kamata ki fara sanar dani kafin kixo kina kuka anan, kinga yanda idanunki sukayi kuwa?
'ba komai anty jidda, xaxxabi ke damuna kuma bayan wannan sai na tsinci kaina bana jin dadin rayuwata, I just feel like to cry.
'shine kuma baxaki gayamin ba, idan wani abu ya same ki am to hold responsible, dan Allah kidaina min haka bana so, idan abu na damunki let me know da wuri, kinsha magani ne?
'yanxu na sha,
'Abinci fa?
'A'ah
'bari na kawo maki ko tea ne kisha, ta tashi ta fita uwani ta bita da kallo tana jin wata qaunar sister din ta yanda take nuna damuwa akanta koda yaushe, amma ya xatayi da soyayyar mijinta da ta kanainaye xuciyarta, wannan abin kunyane a gurinta duk lokacin da jidda ta kamata dumu dumu cikin soyayyar mijinta, ta hada kanta da gwiwarta hade da sakin wani kuka mai narkar da xuciya.
Asalin labarin.......
Hajiya Zubaida itace mahaifiyar jidda, macece mai haquri da tawakkali, tana da riqon amana da rashin son abin duniya, Jiddah kadai ce ta mallaka tun bayan rasuwar mijinta,
Hajiya zubaida aminiya ce ga hajiya maimuna, xama suke na amana irin wanda yayi qaranci a wannan xamanin namu, xama suke batare da hassadar juna ba.
Suna rayuwa a gida daya ne, kasancewar mijin hajiya maimuna ba wani mai qarfi bane sosai yana xaune a gidan haya, wulaqanci iri iri yake gani sanadiyar hakan hajiya zubaida ta umurci da su dawo a gidan ta su xauna tunda bata da miji kuma gidan yana da girma sosai.
Yan uwan hajiya xubaida irin mutanen ne masu son cin dukiya hassada da kyashi ba abinda suke so daga gare ta kamar abin hannunta.
Sanda ta kwanta wani ciwo mai tsanani ta soma ganin take taken su tun tana da rai suke kissafa dukiyarta saboda sun dora mata mutuwa, tana tuna mahaifin Jiddah sanda yana raye shima haka sukayi saboda auren xumunci ne dama a tsakaninsu.
Dalilin haka hajiya zubaida ta tara su duka, ta basu wani abu cikin dukiyarta kada bayan mutuwarta su tayar da wata fitina, sauran kuwa ta damqawa hajiya maimuna tare da amanar jidda lokacin tana shekara goma a duniya, Uwani tana shekara biyar itace yar'hajiya maimuna.
Baa dauki wani dogon lokaci ba Allah ya yiwa hajiya xubaida cikawa, tashin hankalinsu a ranar bai misaltuwa, musamman jidda kusan sau biyu tana suma.
Jidda ta taso cikin maraici ba uwa ba uba, amma ta sami kulawa sosai a gurin hajiya maimuna tamkar yar'ta Uwani babu banbanci ko hantara tsakanin su, ta dauki jidda hannu biyu tana bata tarbiya gwargwadon iyawarta.
Ta hada kan ya'yanta, abu mai kyau da marar kyau duk tana nuna masu kuma tare da illar sa, duka family suna son junansu musamman jidda da bata da hayaniya, tana da sanyin hali da kauda ido akan komai, gata da girmama iyayenta sabanin uwani da ita a rayuwarta tana son ta ganta da manyan qawaye masu kudi, komai dai ayi qarya, kun dai gane😀
Sannu sannu har jidda ta kammala secondary School din ta, a lokacin ta hadu da elmustapha hajiya ta aike ta banki.
Daga yanayin tafiyarta xaka gane nutsuwarta da kamalarta, kai tsaye ta shiga bankin hannuwanta duka Acikin Jakarta da alama abu take nema tana tafe tana dubawa,
dai dai lokacin ya fito daga cikin bank din, sanye da baqaqen suit, hannuwansa wayar sa yana tafe shima yana latsa ta cikin sauri da alama wani yake son kira...
Kicibis sukayi karo da juna, wayar dake hannunsa ta subulce ta fadi qasa, ya daqo a fusacce ya dora idanuwansa akanta dai dai lokacin da ta sunkuya domin dauko masa waya.
Tun da taga wayar ta tarwatse hankalinta ya tashi, jikinta ya dauki rawa ta kasa daqowa illah hada kai da tayi da gwiwarta ta soma kuka cikin tashin hankali, abinda bata tabayi ba, yau tayi wa wani hasarar abu mai muhimmanci a garesa.
Turus yaja ya tsaya yana kallonta har lokacin baiga fuskarta ba, sai dai fuskarsa da xuciyarsa cike suke da tsananin mamakin yarinyar dake tsugunne a gabansa......
Vote me on wattpad phertymerh1
*EL_MUSTAPHA*
HASKE WRITER'S ASSOCIATION
(home of experts and perfect writers)
Fertymerh Xarah 💞
12
Hannu yasa ya xame wayarsa daga hannunta, kallo daya yayi wa wayar, hankalinsa ya qara tashi,
Daga yanayinsa xaka gane bai ji dadin hakan ba, ya juya da sauri ya bar gurin, yana gab da shiga motar sa yaji muryarta.
'Dan Allah kayi haquri ka yafemin kada ka tafi da fushina a xuciyarka.....
Juyowar da xaiyi ya ganta tsaye a bayansa ta harde hannuwanta duka biyu alamar tana roqansa, idanuwanta har sunyi ja, hakan da tayi yaji tausayinta matuqa.
'yace ba komai, kidaina kukan domin bai da amfani a yanxu.
'tace nagode, ta juya batare da taji amsar sa ba ta fice, kallonta yake yana observing akan ta har lokacin da ta shiga cikin bankin, ya jingina da motar sa yana kallon wayar,
Bude wayar yayi ya ciro sim din sa, kana ya bude motar ya dauko qaramar wayarsa ya bude da sauri ya sanya sim din.
Qoqarin kunna babbar wayar yake yagani ko xata tashi, cikin sa'a kuwa ta tashi, tunani yayi to kodai screen guard dinne ya tarwatse, da kuwa yayi murna sosai ya cilla wayar cikin mota.
Yana qoqarin shiga ya ganta ta fito, wannan karon waya take amsawa
Kallo ya bita dashi har sanda tayo gab dashi dai dai lokacin tana qoqarin mai da wayar a jaka, ko kadan batayi tunanin sake kallon sa ba saboda cike take da tsoronsa gani take kamar xai iya dukanta, meyiwuwa tsayuwar sa anan Ma ita yake jira,
Kamar ance ta dago, suna hada ido yayi mata alama da hannu taxo, sai da hantar cikinta ta motsa, ta juya tana kallon wani security tunani take ko xata hada shi da shine kada yayi mata wani abin, bata qara tsorata ba sai sanda ta gansa yana xuwa da kansa, ta riqe jakarta dam jikinta ya dauki rawa kamar ta xura da gudu take ji,
'amma ai nace kayi haquri ko, cikin rashin sani ne dan Allah kada ka cutar dani.... ta rumtse idanunta,
Idanu ya xura mata kallonta yake sama da qasa har xuwa lokacin da ta bude idanuwanta, irin kallon da yake mata ya qara ruda ta,
'your name? Shine abinda taji ya fada,
Tace ni.. ni... Hauwau Ahmed suna na am.. am.. Sai kuma ta kasa qarasawa,
'ki nutsu, ni ba mugu bane da xan cutar dake, ya nuna mata card dinsa, am a police, ko wani naga xai cuta maki xan kare ki.
Sai ta fara sauke numfashi ahankali ba dan ta nutsu dashi, ita kawai ya barta ta tafi xata fi samun nutsuwa fiye da tsayuwa dashi, ya nemi address nata ba gardama ta bashi, da sauri ta bar gurin yana ganin lokacin da ta shiga napep ta bar gurin.
Tana xuwa gida ta bawa hajiya labari, sosai sukayi dariyar ta bama kamar uwani,
'Anti Jiddah kin fiye tsoro ne meyasa xaki tsaya masa kuka,
Jidda ta tashi ta nufi dakin ta tana fadin ai kuma tunda ba ke bace ni sai ki barni.
*
El'Mustapha Maneer (CP) yana dawowa gida ba abinda ya fara sai maganar ya sami matar aure,
Gadon ta hau, yanda suka kwanta suna fuskantar juna sai dai shi idanunsa a lumshe suke, qirjinsa take kallo kafin ta dora hannu akai tana shafawa a hankali, bude idanuwansa yayi yana kallonta cikin yanayi na barci,
jiddana yau ban sami Hutu ba ko kadan, nagaji sosai, ban gayamaki ba har xaria naje yau.
Tayi shiru batare da tayi magana ba, amma yanda idanunta sukayi jaa kawai xai tabbatar maka na bacin rai ne, ta juya masa baya cikin fushi, hannu yasa ya juyo da ita hade da matse ta ajikinsa, hannunsa na yawo a doron bayanta,
'wannan kadai ya isa ki gane, ke kadaice macen dana keso, kin isheni a rayuwata, baxan iya lalurar wata macen ba, baxan iya son wata 'ya mace bayan jidda ba, bana son kina juyamin baya ko kadan.
Still bata tanka ba, banda sauke numfashi ba abinda take,
Ko baya buqata jidda ta nuna masa tata buqatar yana qoqarin sauke wannan nauyin just to make her happy and satisfied, baiga abinda jidda xata nema a gunshi ya hanata ba, ballantana karan kansa kacokan, ya sabule hannun rigar baccinta bayan ya hada bakinsa da nata.
Asuba ta gari *Jiddatulmusty*
*EL_MUSTAPHA*
HASKE WRITER'S ASSOCIATION
(home of experts and perfect writers)
Fertymerh Xarah 💞
11
'Washe garin ranar ga baki daya yinin ranar uwani bata fito ko falo ba tana can qunshe acikin daki.
Ganin shirun yayi yawa ne yasanya jidda xuwa ta dubata,
Kallo daya tayi wa uwani sai da hankalinta ya tashi, jikinta ya dauki rawa ta qarasa kusa da ita fuskarta dauke da mamaki take kallonta.
'meke damun ki uwani, meya same ki haka, idanunki sukayi jawur suka kumbura,
Uwani tayi qoqarin boye hawayen ta amma ina kamar kada ta tambayeta sai hawayen suka fara xarya, kukan me takeyi idan ba kukan so ba, rungumar da elmustapha yayi wa jidda jiya ba qaramin tarwatsa xuciyarta yayi ba, amma taya xata iya gayawa jidda saboda mijinta ne?
Ganin uwani tayi shiru batayi magana ba ya sanya hankalin jidda qara tashi, ta riqo kafadarta hannunta sai karkarwa yake kamar itama xatayi kukan haka take ji.
Uwani ki gayamin damuwar ki, a duniyar nan akwai wadda tafini muhimmanci a gurin kine kamar hajiya, ko kin sami matsala da Yusuf ne?
Uwani ta girgixa kanta cike da quncin jin ta ambaci wani Yusuf,
'ko matsala kika samu a makaranta? Nan ma ta girgixa kanta,
'to menene uwani, kiyi magana, ke ba arham bace da xan xauna rarrashin ki tun daxu jin matsalar ki, atleast ko menene ya kamata ki fara sanar dani kafin kixo kina kuka anan, kinga yanda idanunki sukayi kuwa?
'ba komai anty jidda, xaxxabi ke damuna kuma bayan wannan sai na tsinci kaina bana jin dadin rayuwata, I just feel like to cry.
'shine kuma baxaki gayamin ba, idan wani abu ya same ki am to hold responsible, dan Allah kidaina min haka bana so, idan abu na damunki let me know da wuri, kinsha magani ne?
'yanxu na sha,
'Abinci fa?
'A'ah
'bari na kawo maki ko tea ne kisha, ta tashi ta fita uwani ta bita da kallo tana jin wata qaunar sister din ta yanda take nuna damuwa akanta koda yaushe, amma ya xatayi da soyayyar mijinta da ta kanainaye xuciyarta, wannan abin kunyane a gurinta duk lokacin da jidda ta kamata dumu dumu cikin soyayyar mijinta, ta hada kanta da gwiwarta hade da sakin wani kuka mai narkar da xuciya.
Asalin labarin.......
Hajiya Zubaida itace mahaifiyar jidda, macece mai haquri da tawakkali, tana da riqon amana da rashin son abin duniya, Jiddah kadai ce ta mallaka tun bayan rasuwar mijinta,
Hajiya zubaida aminiya ce ga hajiya maimuna, xama suke na amana irin wanda yayi qaranci a wannan xamanin namu, xama suke batare da hassadar juna ba.
Suna rayuwa a gida daya ne, kasancewar mijin hajiya maimuna ba wani mai qarfi bane sosai yana xaune a gidan haya, wulaqanci iri iri yake gani sanadiyar hakan hajiya zubaida ta umurci da su dawo a gidan ta su xauna tunda bata da miji kuma gidan yana da girma sosai.
Yan uwan hajiya xubaida irin mutanen ne masu son cin dukiya hassada da kyashi ba abinda suke so daga gare ta kamar abin hannunta.
Sanda ta kwanta wani ciwo mai tsanani ta soma ganin take taken su tun tana da rai suke kissafa dukiyarta saboda sun dora mata mutuwa, tana tuna mahaifin Jiddah sanda yana raye shima haka sukayi saboda auren xumunci ne dama a tsakaninsu.
Dalilin haka hajiya zubaida ta tara su duka, ta basu wani abu cikin dukiyarta kada bayan mutuwarta su tayar da wata fitina, sauran kuwa ta damqawa hajiya maimuna tare da amanar jidda lokacin tana shekara goma a duniya, Uwani tana shekara biyar itace yar'hajiya maimuna.
Baa dauki wani dogon lokaci ba Allah ya yiwa hajiya xubaida cikawa, tashin hankalinsu a ranar bai misaltuwa, musamman jidda kusan sau biyu tana suma.
Jidda ta taso cikin maraici ba uwa ba uba, amma ta sami kulawa sosai a gurin hajiya maimuna tamkar yar'ta Uwani babu banbanci ko hantara tsakanin su, ta dauki jidda hannu biyu tana bata tarbiya gwargwadon iyawarta.
Ta hada kan ya'yanta, abu mai kyau da marar kyau duk tana nuna masu kuma tare da illar sa, duka family suna son junansu musamman jidda da bata da hayaniya, tana da sanyin hali da kauda ido akan komai, gata da girmama iyayenta sabanin uwani da ita a rayuwarta tana son ta ganta da manyan qawaye masu kudi, komai dai ayi qarya, kun dai gane😀
Sannu sannu har jidda ta kammala secondary School din ta, a lokacin ta hadu da elmustapha hajiya ta aike ta banki.
Daga yanayin tafiyarta xaka gane nutsuwarta da kamalarta, kai tsaye ta shiga bankin hannuwanta duka Acikin Jakarta da alama abu take nema tana tafe tana dubawa,
dai dai lokacin ya fito daga cikin bank din, sanye da baqaqen suit, hannuwansa wayar sa yana tafe shima yana latsa ta cikin sauri da alama wani yake son kira...
Kicibis sukayi karo da juna, wayar dake hannunsa ta subulce ta fadi qasa, ya daqo a fusacce ya dora idanuwansa akanta dai dai lokacin da ta sunkuya domin dauko masa waya.
Tun da taga wayar ta tarwatse hankalinta ya tashi, jikinta ya dauki rawa ta kasa daqowa illah hada kai da tayi da gwiwarta ta soma kuka cikin tashin hankali, abinda bata tabayi ba, yau tayi wa wani hasarar abu mai muhimmanci a garesa.
Turus yaja ya tsaya yana kallonta har lokacin baiga fuskarta ba, sai dai fuskarsa da xuciyarsa cike suke da tsananin mamakin yarinyar dake tsugunne a gabansa......
Vote me on wattpad phertymerh1
*EL_MUSTAPHA*
HASKE WRITER'S ASSOCIATION
(home of experts and perfect writers)
Fertymerh Xarah 💞
12
Hannu yasa ya xame wayarsa daga hannunta, kallo daya yayi wa wayar, hankalinsa ya qara tashi,
Daga yanayinsa xaka gane bai ji dadin hakan ba, ya juya da sauri ya bar gurin, yana gab da shiga motar sa yaji muryarta.
'Dan Allah kayi haquri ka yafemin kada ka tafi da fushina a xuciyarka.....
Juyowar da xaiyi ya ganta tsaye a bayansa ta harde hannuwanta duka biyu alamar tana roqansa, idanuwanta har sunyi ja, hakan da tayi yaji tausayinta matuqa.
'yace ba komai, kidaina kukan domin bai da amfani a yanxu.
'tace nagode, ta juya batare da taji amsar sa ba ta fice, kallonta yake yana observing akan ta har lokacin da ta shiga cikin bankin, ya jingina da motar sa yana kallon wayar,
Bude wayar yayi ya ciro sim din sa, kana ya bude motar ya dauko qaramar wayarsa ya bude da sauri ya sanya sim din.
Qoqarin kunna babbar wayar yake yagani ko xata tashi, cikin sa'a kuwa ta tashi, tunani yayi to kodai screen guard dinne ya tarwatse, da kuwa yayi murna sosai ya cilla wayar cikin mota.
Yana qoqarin shiga ya ganta ta fito, wannan karon waya take amsawa
Kallo ya bita dashi har sanda tayo gab dashi dai dai lokacin tana qoqarin mai da wayar a jaka, ko kadan batayi tunanin sake kallon sa ba saboda cike take da tsoronsa gani take kamar xai iya dukanta, meyiwuwa tsayuwar sa anan Ma ita yake jira,
Kamar ance ta dago, suna hada ido yayi mata alama da hannu taxo, sai da hantar cikinta ta motsa, ta juya tana kallon wani security tunani take ko xata hada shi da shine kada yayi mata wani abin, bata qara tsorata ba sai sanda ta gansa yana xuwa da kansa, ta riqe jakarta dam jikinta ya dauki rawa kamar ta xura da gudu take ji,
'amma ai nace kayi haquri ko, cikin rashin sani ne dan Allah kada ka cutar dani.... ta rumtse idanunta,
Idanu ya xura mata kallonta yake sama da qasa har xuwa lokacin da ta bude idanuwanta, irin kallon da yake mata ya qara ruda ta,
'your name? Shine abinda taji ya fada,
Tace ni.. ni... Hauwau Ahmed suna na am.. am.. Sai kuma ta kasa qarasawa,
'ki nutsu, ni ba mugu bane da xan cutar dake, ya nuna mata card dinsa, am a police, ko wani naga xai cuta maki xan kare ki.
Sai ta fara sauke numfashi ahankali ba dan ta nutsu dashi, ita kawai ya barta ta tafi xata fi samun nutsuwa fiye da tsayuwa dashi, ya nemi address nata ba gardama ta bashi, da sauri ta bar gurin yana ganin lokacin da ta shiga napep ta bar gurin.
Tana xuwa gida ta bawa hajiya labari, sosai sukayi dariyar ta bama kamar uwani,
'Anti Jiddah kin fiye tsoro ne meyasa xaki tsaya masa kuka,
Jidda ta tashi ta nufi dakin ta tana fadin ai kuma tunda ba ke bace ni sai ki barni.
*
El'Mustapha Maneer (CP) yana dawowa gida ba abinda ya fara sai maganar ya sami matar aure,