← Book details El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 80

Sashe 47

El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tace meyasa Dr, dan Allah kaje ka duba ta a yanxu kada mu rasa jiddah.

Ko naje ba abinda xan iya mata a yanxu tunda bata farfado ba, tun da aka shiga aikin da ita na lura tana jin jiki, akwai nurses tare da ita da ta motsa xasu sanarda ni, just pray for her domin shine abinda take buqata, nan da awa biyar idan bata farfado ba sai wani iko na Allah.

Jikinta yayi sanyi farin cikin dake xuciyarta ya kau, ta tashi a hankali cikin dauriya xata fice ya tsaidata,

Wani rubutu yayi akan takarda ya miqa mata,

Asiyo su yanxu because of the child xaa yi mata amfani da su, sai a bawa wata nurse ta hada mata,

Tace meyasa sai nurse xata hada mata, kai baxaka yi bane? Ta fada cikin son gwada shi taji,

Murmushi yayi batare da ya kalleta ba, yace ba abin damuwa bane, ki kawo xan hada mata, ai d'a na kowa ne beside Ma am here to safe a life,

Duk mgnr da yake fuskarsa a sake, wanda baisan halin sa bane yake masa kallon mai girman kai da mulki kamar yanda mutane suke fada, dr merah yana da sauqin kai da son mutane amma mulki da sarauta sun rinjaye shi wanda mutane ke masa wani kallo daban.

Ta juya ta fita batare da tayi magana ba,

Ya kishingida hade da lumshe idanuwansa yana tuna halin da jiddah take ciki, yana ji itace mace ta uku da ya taba tausayi a rayuwarsa bayan Dr Fulani Gafai.

Yayi saurin kauda tunaninsu a xuciyarsa ta hanyar janyo wayarsa yana laluben number Gimbiya Afiya.

*

Alamar shigowa gidan taji, tana leqawa ta window ta tsinkayo fitowar ta cikin motar tare da wata yarinya da baxata wuce sa'an ta ba.

Hajiya Mariya bata manta da abinda uwani tayi mata ba cos sosai ranta ya baci da yanda ta lalata mata riga.

Uwani ta dauke kanta tana hade fuska cikin tambayar,

Wacece wannan kuma, me taxo yi gidan mu?

Gidan mu? Hajiya ta maimaita tana kallon uwani, can you imagine, ta bata fuska tana fadin xo ki rage min tsawon ki anan uwani I have to deal with you,

Cikin rashin fahimta tace taya xan rage maki tsawona bayan haka Allah ya yini idan gaskiya ne ke ki rage naki mugani, ta tunxure baki tana rungume hannayenta,

Wai wacece wannan hajiya, meyasa wannan qaxamar take xaune a gidannan, ni ban san ta ba cewar budurwa.

Cikin bacin rai hajiya tace barta mai aiki ce na dauko take min wannan iskanci, maganin ta xanyi yanxu, ta shiga dakin ta a fusacce,

Uwani ta dubi yarinyar ta matsa kadan cikin shigar munafurci, tace kin shiga uku, wannan matar yar iskace ta dauko ki tayi iskanci dake, nima haka ta daukoni amma ni ba yar iska bace ban yarda ba shine taqi maidani, karki bari ta lalata ki a banxa ki fara kuka tun yanxu ta maidaki.

Budurwar taja tsaki tana ture uwani,

Tace ke dallah matsamin a jiki sai tsamin dauda kike, ai kece yar iskar ma kuma sai na gayamata.

Uwani tace to idan kin gayamata me xata min, daga kawai nace mata yar iska, to nace na qara cewa yar iska ce, kuma har dake din, tsamin dauda da nake yafiki tsabtar jikinki mai qamshi domin gurbatacce ne, maqiyiyar Allah, lalatatta mai qaton hanci, dubi bakin ta kamar na kare, qilama kwadayi ya kawo ki gidanmu, kinxo kici dadi da shegen bakin nan mai kama da...... Bata qara saba taji saukar duka a bayanta.

Kafin tayi wani yunquri ta soma jin ana dukanta da bulala ta ko ina,

Sai ihu take tana neman ceton wannan budurwar,

'Dan Allah kiyi haquri hajiya baxan qara ba, na tuba, wayyo hajiyata kixo xata kasheni ta rabani da duniyar saboda baqin ciki, ke shegia kixo ki taimakeni kixo kice mijinki ya daina dukana, yar baqin ciki to baxan mutu ba.

Tun tana magana har tayi shiru tana maida numfashi,

Hajiya Mariya ta yarda bulalar tana fadin sai na gyara ki a gidannan wlhy,

Uwani dake kwance tana nishi da kyar tace nima sai na gyara ki duk kika min sai na rama,

Har xata qara dukanta budurwar ta tare ta,

Kyaleta dan Allah a matse nake idan mun gama kixo ki daki shegia son ranki,

Kece shegia tambadadiya, ina tashi sai na karya maki wannan qugun da kike girgixawa karuwa kawai.

Basu kula ta ba suka shige rungume da juna suna shafar juna.

Suna shiga dakin suka soma cire kayansu, batare da tunanin komai ba hajiya Mariya ta dauko wannan qoqon ta debo abin a yatsa, ita Ma yarinyar ta diba kowacce ta sunkuya suna shafawa a qasan su.

Lokaci daya suka dago suna kallon juna idanunsu a waje saboda wani radadi da suka ji......

EL'MUSTAPHA

Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers

Fertymerh Xarah💞

50

Da gudu kowacce su ta nufi toilet neman ruwa.

Hargowar da suke ya dakatar da uwani daga kukan da take, ta kashe kunne sosai tana sauraren su,

A hankali ta tashi ta nufi dakin basa nan suna toilet, tayi shiru tana tunanin ko ihun me suke haka? Qilama iskan cin ne suke, yan iska.

Sadaf sadaf ta shiga dakin, hanyar toilet din ta nufa, qofar a bude take ta leqa taga me suke yi haka ne,

Abinda ta gani ya saka ta xare ido hade da dawowa baya da sauri tana kallon qoqon da ta sakawa yaji.

Gabanta ya tsananta bugawa ta san mai hana suci ubanta yau sai Allah,

Ta dora hannuwanta duka biyu aka sai ga hawaye shar na bin kumatunta,

'Na shiga uku ni uwani, Allah na tuba ka yafe min ka ceceni,

Ta fita daga dakin da sauri, harabar gidan ta nufa tana kallon gate din gidan,

Ta rasa yanda ake bude wannan gate, ga katangar mai tsayi ballantana ta haura.

Dabara ta fado mata, xata sami mabuya ta buya idan sunxo fita da mota ta fita ta gudu, ta koma cikin gidan da sauri dakin nasu ta nufa har lokacin basu fito ba.

Ta kyalkyace da dariya tana jin wani farin ciki a xuciyarta yanxu, ta qara leqawa tana kallonsu yanda suka bada muhimmanci wajen wanken abin da ruwa, ta dora hannunta a baki tana dariya🤭,

Jakar hajiya Mariya ta bude batare da tunanin komai ba ta dibi kudi bata san ko nawa bane, jikinta na rawa ta fice daga dakin, can harabar gidan ta nufa ta boye bayan wata flower tana jiran fitowarsu, yau kam xata bar garin sai inda hajiyarta, sai murna take.

Sun dauki kusan rabin awa aciki kafin su fito kowane fuskarsa ba annuri tunanin budurwar sharrin hajiya ne ko dama da saninta, sai ta soma hada kayanta tana maida kayanta a jiki.

Kallonta hajiya tayi sheqeqe,

Tace me kike yi haka Hadixa, ba dai tafiya xakiyi ba.

Batayi magana ba ta dauki jakarta da gyalenta, hajiya ta riqo ta da sauri,

Kiyi haquri wallahi ba laifina bane, ni kaina bansan da abin haka yake ba, kuma ko da safe da naje gurin ki na saka shi lfy lau ba wannan abin, ban san menene aka saka ba, banma san wanda ya saka ba, amma kiyi haquri ki tsaya har gobe kinji.

Ko na tsaya ba abinda xan iya maki, gurin xafi yake min sosai, ina so naje gida na duba kaina,

Haba hadixa yanxu ya kike so nayi, xo ni nasan yanda xan maki ya daina xafi, nima nawa ai xafin yake amma na haqura.

Bata saurare ta ba ta fice da sauri saboda xafin da take ji, tana son taje gida ta baje gurin a iskan fanka, idan tace tayi hakan gaban hajiya baxata barta ba da jarabarta.

Fitowarta duk akan idon uwani dake labe, tayi mamakin yanda ta bude gate din kai tsaye, dama dai ban iya bane, tana ficewa uwani ta biyo bayanta da gudu ta bar gidan har tana bankade hadixa a hanya, bata damu ba ko waiwaye burinta taga ta fice daga unguwar gabaki daya.

Sai safa da marwa take tsakiyar dakin cikin tunanin ko waye xai mata wannan danyen aikin.

Uwani ta fado mata a xuciya, lallai kuwa xanci ubanki a yau domin ke xan saukewa buqatata ko kina so ko bakya so,

Ta fita a fusacce tana kiran uwani, shiru baa amsa ba, ta soma duba wa ko ina tana kiran sunanta,

Wayam babu uwani ba alamarta, tana fitowa harabar gidan taci karo da gate din a bude.

Taja numfashi cikin jin haushi, rufe gate din tayi ta koma cikin gida tamkar xuciyarta xata fado saboda haushi da baqin ciki, Allah ya hada ta da uwani ko a hanyane.

Uwani na barin gidan a haukace ta shiga taxi sai tasha, duk da dattin dake jikinta bata damu ba, haka ta shiga motar ana hantarar ta da kyamarta ko a jikinta illa qara baje duwawu da tayi tana fadin

Mutum kudi ya biya na biya muka shigo motar, bata gidan uban kowa bace ballantana a fiddani, wanda ke jin wari ya saka hancinsa a window ina ruwana, ta cigaba da cin biredi ta da pure water batare da damuwa ba.

Da yawa kallon da suke mata a motar bata da hankali, in ba haka ba wane marar hankali xai fito haka ba mayafi ba takalmi kuma cikin datti, bugu da qari cin biredi da pure water cikin maxa.

Tana gama ci ta qulle sauran biredi ta rungume abinta a qirji tana fadin,

Duniyar nan bata da tabbas idan kayi sake ayi maka sakiya, nasan mutane da yawa acikin motar nan guntun biredi nan suke jira idan nayi sake a sace min na rasa wanda ya dauka yanda ake ta kallo na haka, gwanda na rungume abina idan na tashi barci na qarasa cinyewa.

Sai kallonta suke suna tausaya mata qila sabuwar hauka ce, amma da uwani tasan tunanin da suke kanta na cewa mahaukaciya ce da sai ta xage su tsab😂

Suna cikin tafiya barci ya dauke ta rungume da biredi ta, ta kwantowa wanda ke kusa da ita a kafada, sai matsawa yake cikin kyankyaminta yana ture ta, ta bude idanunta da suka soma ja tana kallonsa,
Chapter 47 · 0% Book details