Sashe 64
El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka taji a xuciyarta kamar damuwarta ta kau, hijab ta saka dama airah barci take sai bata bi ta kanta ba ta soma qoqarin bude qofar, merah na jin haka ya koma cikin falon inda el'mustapha.
El'mustapha ya cika da mamaki sanda jiddah ta fito, wane girma ne na merah a gurin ta haka, meke tsakanin su, meyasa ta dalilinsa ta fito bayan duk magiya da roqon da ake mata tun jiya, ya xuba mata manyan idanuwansa yana kallonta,
Dr merah ya juyo yana kallonta,
Ya salam, meya sami jiddah haka, menene ya saka ki kuka haka har idanunki suka kumbura?
Kamar jira take ta soma kuka kuwa,
Yace saboda me na baki number na jiddah, kin gaya min ke marainiya ce ba uwa ba uba, ba yaya ba qanwa only you an your husband, nace ki dauke ni matsayin yayan ki, xan hada ki da iyayena su xama naki, xan hada ki da yan uwana, matata har qanwata Rumaisa ashe ke baki dauke ni yayan ki ba idan har baxaki iya gayamin damuwar ki ba.
Ya xauna yana fadin, xo xauna nan naji waye ya taba ki haka, idan mijin kine ko yana babban dan sanda baifi qarfin Sarautar mahaifinki ba haka bai fi qarfin Mulkin yayan ki ba, idan ta kama sai na saka a daure min shi na baki bulala kiyi ta dukan sa har sai inda ranki yayi sanyi.
Murmushi tayi wanda bai kai xuciyarta ba, ta qarasa ta xauna inda ya nuna mata,
Banji dadi ba jiddah naxo na same ki cikin wannan halin baki kira kin gayamin ba, aiko a waya ne tsab xan kira na kwatar maki yancin ki, kin ganni nan qanwata rumaisa idan ta sami matsala da mijinta irin wannan, ba wanda xata nema a gida sai ni koda bana gari, kuma ba wanda xai taba ji daga ni sai ita sai mijinta, kuma he is my friend jinina ne shi I told you before, haka xan kirashi idan shine bashi da gaskiya na masa fada ya gyara idan kuma itace ita ma nayi mata fada, Afiya ma sai ta gane ko nayi mata laifi sai taje ga yayanta Bilal xaki ga ya kirani yamin yanda nake masa, and we live happily, idan haka ne meyasa jiddah baxata gayawa nata yayan matsalarta ba.
El'mustapha na xaune baice komai ba ya xuba masu idanu, yana mamakin sauqin kai irin na Dr Merah, a waje idan yana mulki kamar bashi ba, dariyar sa ma baxaka gani ba.
Merah ya dan matso yana fadin, tell me jiddah, don't look at him ba ruwanki dashi da yayanki kike magana,
Batare da bata lokaci ba ta kwashe komai ta gayamasa, tana gamawa kuwa ta fara kuka,
Merah ya dube shi yana fadin, maida uwanin xaka yi ne?
El'mustapha ya girgixa kansa,
Merah has tsuke fuska yana fadin idan kayi haka kuma ka cutar da waccan yarinya, idan kasan baxaka maidata ba saboda me xaka mata qaryar idan ta shiryu xaka maida auren ku, baka tunanin dalilin qin maida auren sai ta koma ruwa ta cigaba da abinda take inma baifi hakan ba, to wane gyara kayi mata?
Idan har iyayenta baxasu iya tankwasa ta su gyarata ba I don't think you can do, kaine wa, uban ta 'ko me?
Xai yi magana dr merah ya katse sa, baxan baka damar magana ba a yanxu just take me to your sister house, ina so naga yarinyar....
Suka tashi suka tafi, a falon anty ikram suka xauna, aka kira uwani tun da ta shigo ta kafe merah da idanu, ina el'mustapha ya sami bature haka mai kyau.
Kallo daya dr merah yayi mata ya gane yarinyar bata da nutsuwa,
Kowa bata gaida ba ta xauna tana kallon el'mustapha da murmushi,
Ai daxu ina taso na kira ka naji muryar ka amma ba kudi a wayana, kuma gidannan ana min baqin ciki ba wanda ya bani wayarsa n.... Merah ya katse ta a fusacce,
Shut up.... ya fada cikin tsawa,
Nan da nan uwani ta nutsu tana kallonsa cikin mamaki da tsoro, shi wannan kuma waye.
Yace yayar mu wannan yarinyar a maidata inda iyayenta, suke da haqqi akan kula da tarbiyar ta idan kuma ta gagare su ne su bani inta naje da ita akwai kurkukun da xan jefata a ciki xata gyaru.
Ya dubi uwani yana fadin, el'mustapha yana maki qarya baxai aure ki ba ko kin nutsu ko baki nutsu ba, ki cire wannan a xuciyarki, shi mijin mace daya ne jiddah kawai, alqawarin da yayi maki na maganar xai aure ki idan kin shiryu shima babu, ki dauki kayanki kije gidanku ki xauna da iyayen ki, idan kin ga dama kada ki nutsu kanki kika cuta da iyayenki kuma ba mai auren ki a haka is better ki dawo cikin hayyacinki kisan me kike.....
Duk maganar da yake uwani ido ta xuba masa, bata ma taba tunanin yaji hausa haka ba, shi kuma waye ina ruwanshi da soyayyarta da el'mustapha, ko dai sonta yake yi yaxo ya rabata da el'mustapha dan ya aure ta idan kuwa hakane xata amince da..... Ya katse mata tunani yana fadin daina kallona haka, ashe baki da kunya idan har xaki tsaya kina kallon tsakiyar idanuna.
Uwani tayi saurin sunkuyar da kanta qasa xuciyarta na bugawa kamar ta fashe da kuka take ji.
Ikram tace amma naji dadin wannan abin dan baxan iya xama da wannan yarinyar ba xan karya mata qafafuwa, da axo ana aikin dana sani gwanda tabar gidannan inma gidanka xata je ta xauna wannan tsakanin ka ne da jiddah ba ruwana.
Dr merah yace daga nan gidan ubanta xata je ko jiddah baxata gani ba, ki fito da naki mijin kixo ni xan maki aure in kuma baki dashi ina da wani dogari nawa dake neman matar aure matarshi ta rasu sai na hada ku ai ba wani abu bane, amma ke bakya jin kunya ki dawo kina son mijin jiddah?
Jiddah da kika so kashewa ki rabata da duniya saboda mijinta da ta rufa maki asiri ta baki kika aura, kika sa aka nakasa mata qafa, duk bakya jin nauyi da kunyarta a yanxu, kin manta da wannan, shi wannan mijin naki da kike son koma masa jinin sa fa kika so kashewa a gaban mahaifiyarsa, kinsan xafi da radadin da uwa keji a xuciyarta a duk lokacin da wani abu ya sami dan cikin ta, idan har bakyason jinin el'mustapha qarya kike kice kina sonsa.
Inaji jiddah tare aka raineku kuka taso cikin gida daya qarqashin iyaye daya ta riqe ki da amana tana xaune dake da xuciya daya amma kika iya mata wannan ballantana el'mustapha da baki hada komai dashi ba, kenan shima idan ya bata maki rai watarana xaki iya saka a kashe shi.
Kuma saboda Allah dan baki da kunya da imani ki dawo kina son mijinta, hala ita bata da xuciya a jikine ko an gayamaki dutse ce bata son mijinta, kinxo kina saka damuwa a tsakanin su kina son raba mata da miji kina so ki raba farin ciki da soyayya saboda wata buqata taki ta banxa, to baxaki aure sa ba, kuma el'mustapha baxai aure ki ba.
Duk abinda kika ga kin ma iyayenki sun xuba maki ido kina ganin kamar sun kyaleki ne to akwai wannan baqin cikin a xuciyarsu naki wanda ko basu fito sun gayamaki ba yana damun su a xuciya saboda ke jinin su ba yanda xasu iya dake, dan haka kije ki nemesu gafara ki kuma je ki nemi gafarar jiddah, domin mace ce mai haquri, da ace kin tsaya kin nutsu tun farko wallahi xaki ji dadin xama da ita kuma el'mustapha har yanxu yana mijinki, amma kinyi sake da wannan damar kuma baxaki taba samun sa ba.
Kuka sosai uwani keyi tamkar ranta, sam bata da nutsuwa a tare da ita, hankalinta ya tashi sosai tana ji tana gani anti ikram taje ta fito da kayanta.
Suka fito da ita, sai ga yusuf qanin mijin anty ikram,
'Yauwa yusuf xo ka kai uwani gida,
Yace aa anty ikram ina da wani uxuri baxan iya xuwa har wani gari yanxu ba ki hadata da driver, ya gaisa dasu merah yayi ciki abinsa,
Uwani ta bisa da kallo.
Merah ya dubi el'mustapha kai kuma muje gida inda qanwata nayi maka hukunci a gabanta in ta kama ta dake ka da kanta....
Uwani ta tsurawa yusuf ido cikin mamaki, yusuf din ta ne fa, yusuf din da qawarta surry tayi snatching ta aura, ashe qanin mijin anty ikram ne amma bai taba gayamata shiyasa tayi mamakin yanda akayi jiddah tasan yusuf, bai gane ta bane kome?
Tayi saurin shan gabansa tana kallonsa,
Haba yusuf baka gane ni ba, nice fa uwani masoyiyar ka ko ka manta, dan Allah kayi haquri ka yafe min, ni dama kai nake so wlhy.
Duk gurin suka xuba masu idanu,
Merah yace wannan bata san wanda take so ba kenan, Mijin qanwata shiga mota muje kafin mai martaba ya ankara da bana gidan.
Suka ma anti ikram sallama suka fice,
Yusuf ya dube ta, idan yace baya son uwani ya yaudari xuciyarsa, cos itace first love din sa, sun fara soyayya da ita a skul har jiddah tasan da soyayyar su amma bai taba gayawa anty ikram a lokacin ba saboda yasan yanda basu qaunar yarinyar, uwani ta cuce sa ta guje sa saboda el'mustapha shine yau take dawo masa saboda auren ta ya mutu, yaja dogon tsaki cikin takaici ya raba ta gefenta yayi shigewar sa.
'Anty ikram ta shige tana fadin idan kin tashi ga driver nan ya kaiki in kuma xaki tsaya kwadayin maxa ne to, tunda ke kowa ma so kike, banxa tayi shigewarta.
A sanyaye uwani ta shiga motar jikinta ba kwari, haka take jin wata nadama na ratsa xuciya da gangar jikinta, sau biyu tana samun dama tana kubce mata, meyasa hakan, tabbas harda haqqin iyayenta.
Tasan bata cancanci jiddah ta yafe mata ba, ta aikata babban kuskure a rayuwarta, inama hannu agogo xai dawo baya da ta canxa rayuwarta da xamantakewar xamanta da jiddah, amma ta sani a yanxu abu ne mai wuya jiddah ta qara yarda da ita, lallai el'mustapha ya mata nisa kuma baxata taba samun irin sa ba.
El'mustapha ya cika da mamaki sanda jiddah ta fito, wane girma ne na merah a gurin ta haka, meke tsakanin su, meyasa ta dalilinsa ta fito bayan duk magiya da roqon da ake mata tun jiya, ya xuba mata manyan idanuwansa yana kallonta,
Dr merah ya juyo yana kallonta,
Ya salam, meya sami jiddah haka, menene ya saka ki kuka haka har idanunki suka kumbura?
Kamar jira take ta soma kuka kuwa,
Yace saboda me na baki number na jiddah, kin gaya min ke marainiya ce ba uwa ba uba, ba yaya ba qanwa only you an your husband, nace ki dauke ni matsayin yayan ki, xan hada ki da iyayena su xama naki, xan hada ki da yan uwana, matata har qanwata Rumaisa ashe ke baki dauke ni yayan ki ba idan har baxaki iya gayamin damuwar ki ba.
Ya xauna yana fadin, xo xauna nan naji waye ya taba ki haka, idan mijin kine ko yana babban dan sanda baifi qarfin Sarautar mahaifinki ba haka bai fi qarfin Mulkin yayan ki ba, idan ta kama sai na saka a daure min shi na baki bulala kiyi ta dukan sa har sai inda ranki yayi sanyi.
Murmushi tayi wanda bai kai xuciyarta ba, ta qarasa ta xauna inda ya nuna mata,
Banji dadi ba jiddah naxo na same ki cikin wannan halin baki kira kin gayamin ba, aiko a waya ne tsab xan kira na kwatar maki yancin ki, kin ganni nan qanwata rumaisa idan ta sami matsala da mijinta irin wannan, ba wanda xata nema a gida sai ni koda bana gari, kuma ba wanda xai taba ji daga ni sai ita sai mijinta, kuma he is my friend jinina ne shi I told you before, haka xan kirashi idan shine bashi da gaskiya na masa fada ya gyara idan kuma itace ita ma nayi mata fada, Afiya ma sai ta gane ko nayi mata laifi sai taje ga yayanta Bilal xaki ga ya kirani yamin yanda nake masa, and we live happily, idan haka ne meyasa jiddah baxata gayawa nata yayan matsalarta ba.
El'mustapha na xaune baice komai ba ya xuba masu idanu, yana mamakin sauqin kai irin na Dr Merah, a waje idan yana mulki kamar bashi ba, dariyar sa ma baxaka gani ba.
Merah ya dan matso yana fadin, tell me jiddah, don't look at him ba ruwanki dashi da yayanki kike magana,
Batare da bata lokaci ba ta kwashe komai ta gayamasa, tana gamawa kuwa ta fara kuka,
Merah ya dube shi yana fadin, maida uwanin xaka yi ne?
El'mustapha ya girgixa kansa,
Merah has tsuke fuska yana fadin idan kayi haka kuma ka cutar da waccan yarinya, idan kasan baxaka maidata ba saboda me xaka mata qaryar idan ta shiryu xaka maida auren ku, baka tunanin dalilin qin maida auren sai ta koma ruwa ta cigaba da abinda take inma baifi hakan ba, to wane gyara kayi mata?
Idan har iyayenta baxasu iya tankwasa ta su gyarata ba I don't think you can do, kaine wa, uban ta 'ko me?
Xai yi magana dr merah ya katse sa, baxan baka damar magana ba a yanxu just take me to your sister house, ina so naga yarinyar....
Suka tashi suka tafi, a falon anty ikram suka xauna, aka kira uwani tun da ta shigo ta kafe merah da idanu, ina el'mustapha ya sami bature haka mai kyau.
Kallo daya dr merah yayi mata ya gane yarinyar bata da nutsuwa,
Kowa bata gaida ba ta xauna tana kallon el'mustapha da murmushi,
Ai daxu ina taso na kira ka naji muryar ka amma ba kudi a wayana, kuma gidannan ana min baqin ciki ba wanda ya bani wayarsa n.... Merah ya katse ta a fusacce,
Shut up.... ya fada cikin tsawa,
Nan da nan uwani ta nutsu tana kallonsa cikin mamaki da tsoro, shi wannan kuma waye.
Yace yayar mu wannan yarinyar a maidata inda iyayenta, suke da haqqi akan kula da tarbiyar ta idan kuma ta gagare su ne su bani inta naje da ita akwai kurkukun da xan jefata a ciki xata gyaru.
Ya dubi uwani yana fadin, el'mustapha yana maki qarya baxai aure ki ba ko kin nutsu ko baki nutsu ba, ki cire wannan a xuciyarki, shi mijin mace daya ne jiddah kawai, alqawarin da yayi maki na maganar xai aure ki idan kin shiryu shima babu, ki dauki kayanki kije gidanku ki xauna da iyayen ki, idan kin ga dama kada ki nutsu kanki kika cuta da iyayenki kuma ba mai auren ki a haka is better ki dawo cikin hayyacinki kisan me kike.....
Duk maganar da yake uwani ido ta xuba masa, bata ma taba tunanin yaji hausa haka ba, shi kuma waye ina ruwanshi da soyayyarta da el'mustapha, ko dai sonta yake yi yaxo ya rabata da el'mustapha dan ya aure ta idan kuwa hakane xata amince da..... Ya katse mata tunani yana fadin daina kallona haka, ashe baki da kunya idan har xaki tsaya kina kallon tsakiyar idanuna.
Uwani tayi saurin sunkuyar da kanta qasa xuciyarta na bugawa kamar ta fashe da kuka take ji.
Ikram tace amma naji dadin wannan abin dan baxan iya xama da wannan yarinyar ba xan karya mata qafafuwa, da axo ana aikin dana sani gwanda tabar gidannan inma gidanka xata je ta xauna wannan tsakanin ka ne da jiddah ba ruwana.
Dr merah yace daga nan gidan ubanta xata je ko jiddah baxata gani ba, ki fito da naki mijin kixo ni xan maki aure in kuma baki dashi ina da wani dogari nawa dake neman matar aure matarshi ta rasu sai na hada ku ai ba wani abu bane, amma ke bakya jin kunya ki dawo kina son mijin jiddah?
Jiddah da kika so kashewa ki rabata da duniya saboda mijinta da ta rufa maki asiri ta baki kika aura, kika sa aka nakasa mata qafa, duk bakya jin nauyi da kunyarta a yanxu, kin manta da wannan, shi wannan mijin naki da kike son koma masa jinin sa fa kika so kashewa a gaban mahaifiyarsa, kinsan xafi da radadin da uwa keji a xuciyarta a duk lokacin da wani abu ya sami dan cikin ta, idan har bakyason jinin el'mustapha qarya kike kice kina sonsa.
Inaji jiddah tare aka raineku kuka taso cikin gida daya qarqashin iyaye daya ta riqe ki da amana tana xaune dake da xuciya daya amma kika iya mata wannan ballantana el'mustapha da baki hada komai dashi ba, kenan shima idan ya bata maki rai watarana xaki iya saka a kashe shi.
Kuma saboda Allah dan baki da kunya da imani ki dawo kina son mijinta, hala ita bata da xuciya a jikine ko an gayamaki dutse ce bata son mijinta, kinxo kina saka damuwa a tsakanin su kina son raba mata da miji kina so ki raba farin ciki da soyayya saboda wata buqata taki ta banxa, to baxaki aure sa ba, kuma el'mustapha baxai aure ki ba.
Duk abinda kika ga kin ma iyayenki sun xuba maki ido kina ganin kamar sun kyaleki ne to akwai wannan baqin cikin a xuciyarsu naki wanda ko basu fito sun gayamaki ba yana damun su a xuciya saboda ke jinin su ba yanda xasu iya dake, dan haka kije ki nemesu gafara ki kuma je ki nemi gafarar jiddah, domin mace ce mai haquri, da ace kin tsaya kin nutsu tun farko wallahi xaki ji dadin xama da ita kuma el'mustapha har yanxu yana mijinki, amma kinyi sake da wannan damar kuma baxaki taba samun sa ba.
Kuka sosai uwani keyi tamkar ranta, sam bata da nutsuwa a tare da ita, hankalinta ya tashi sosai tana ji tana gani anti ikram taje ta fito da kayanta.
Suka fito da ita, sai ga yusuf qanin mijin anty ikram,
'Yauwa yusuf xo ka kai uwani gida,
Yace aa anty ikram ina da wani uxuri baxan iya xuwa har wani gari yanxu ba ki hadata da driver, ya gaisa dasu merah yayi ciki abinsa,
Uwani ta bisa da kallo.
Merah ya dubi el'mustapha kai kuma muje gida inda qanwata nayi maka hukunci a gabanta in ta kama ta dake ka da kanta....
Uwani ta tsurawa yusuf ido cikin mamaki, yusuf din ta ne fa, yusuf din da qawarta surry tayi snatching ta aura, ashe qanin mijin anty ikram ne amma bai taba gayamata shiyasa tayi mamakin yanda akayi jiddah tasan yusuf, bai gane ta bane kome?
Tayi saurin shan gabansa tana kallonsa,
Haba yusuf baka gane ni ba, nice fa uwani masoyiyar ka ko ka manta, dan Allah kayi haquri ka yafe min, ni dama kai nake so wlhy.
Duk gurin suka xuba masu idanu,
Merah yace wannan bata san wanda take so ba kenan, Mijin qanwata shiga mota muje kafin mai martaba ya ankara da bana gidan.
Suka ma anti ikram sallama suka fice,
Yusuf ya dube ta, idan yace baya son uwani ya yaudari xuciyarsa, cos itace first love din sa, sun fara soyayya da ita a skul har jiddah tasan da soyayyar su amma bai taba gayawa anty ikram a lokacin ba saboda yasan yanda basu qaunar yarinyar, uwani ta cuce sa ta guje sa saboda el'mustapha shine yau take dawo masa saboda auren ta ya mutu, yaja dogon tsaki cikin takaici ya raba ta gefenta yayi shigewar sa.
'Anty ikram ta shige tana fadin idan kin tashi ga driver nan ya kaiki in kuma xaki tsaya kwadayin maxa ne to, tunda ke kowa ma so kike, banxa tayi shigewarta.
A sanyaye uwani ta shiga motar jikinta ba kwari, haka take jin wata nadama na ratsa xuciya da gangar jikinta, sau biyu tana samun dama tana kubce mata, meyasa hakan, tabbas harda haqqin iyayenta.
Tasan bata cancanci jiddah ta yafe mata ba, ta aikata babban kuskure a rayuwarta, inama hannu agogo xai dawo baya da ta canxa rayuwarta da xamantakewar xamanta da jiddah, amma ta sani a yanxu abu ne mai wuya jiddah ta qara yarda da ita, lallai el'mustapha ya mata nisa kuma baxata taba samun irin sa ba.