Sashe 13
El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallon sa take tana jin wani sonsa da kishinsa, wai yau el'mustapha ta xai xama mijin wata, watan Ma uwani, batare da tayi magana ba ta juya ta nufi kitchen domin hada breakfast, duk abinda take el'mustapha na kallon ta, yasan kishine ke dawainiya da ita, da shine ya bijiro da aure nan da yanxu yasan babu xaman lafia a tare da jiddah sa.
Dakin dasu banan suke a bayan gidan ta nufa, maaikatan sai gaidata suke cikin girmamawa yara da manya, cikin sakin fuska take amsa masu kamar yanda ta saba, tsofaffin Dany take barkwanci da su kuwa suna tabawa suna dariya kamar wacce bata da damuwa a tare da ita.
Ni kam tun jiya banga banan ba, lafiya dai ko.
Ai banan bata lafiya hajiya tun jiya tana fama da xaxxabi.
Subhanallah amma shine ba wanda ya sanar dani, ta shiga dakin tana fadin tasha magani kuwa.
Banan na kwance xaxxabi take, tun lokacin da taji ana maganar uwani xata auri el'mustapha, ta riqo hannu jiddah jikinta yayi xafi rau sai makyarkyata take,
'Anty jiddah wai da gaske uwani xata auri Alhaji?
Eh mana yau ake daurawa Ma, me akayi.
Banan ta fara hawaye sosai, anty jiddah kar ki barta ta aure sa dan Allah.
Meyasa banan
Saboda ita muguwa ce, bata da tausayi bata dace dashi ba.
Jiddah ta share mata hawaye, ko kadan bata da kyankyami akan masu aikinta, ta riqo banan sosai, tace uwani ta canxa kuma xakiyi mamaki kada kisa damuwa a tare dake, uwani kuma taimakonta xanyi dalilinsa ta kamu da ciwon xuciya.
Banan tayi shiru kenan itama idan anti jiddah taji dalilin el'mustapha ne bata da lafiya itama xata barta ta aure sa, no baxan iyama anti jiddah haka ba xan cigaba da boye mata koda kuwa sonsa xai xama ajalina cos nasan el'mustapha baxai taba son Irina ba, ina Ma ko sau daya ne na ganshi, tunda nake gidannan ban taba ido da ido dashi ba sai dai kallo daga nesa.
Tashi ki shirya yanxu xaa kaiki asibiti kinji banan.
Ba musu kuwa ta tashi ta soma shiryawa, jiddah na fitowa sashen kitchen din ta tanufa,
Har ta gama shirya masa breakfast wani abu na nan a qirjinta ya tokare mata,wai ita ce da kishiya a yau, anya tayi Saar xuwa duniya kuwa, ko da yake itace ta jawa kanta, amma ita da xuciya daya tayi taimakon kuma tasan baxata taba tabewa ba.
Dai dai lokacin da suke ganiyar soyayyar su da el'mustapha a lokacin wata xata shigo rayuwar su, su dinga sharing love, anya xata iya? Wata ta dinga yin abinda suke da mijinta, rumtse idonta tayi ta jingina da bangon kitchen din da yaji marbles, hawaye mala mala a fuskarta a hankali ta dinga furta Inna lillahi wa Inna ilaihir raji'un,
A hankali ta fara samun sa'ida a xuciyarta har ta sami relief, ta kwashi kayan ta soma hadawa a dining,
Ta qara shiga dakin nasa, yana kwance wannan karon kansa na kallon fankar dakin, ya riqe goshinsa da hannunsa daya,
Gefen gadon ta xauna hade da Jan yatsar qafarsa, el'mustapha lafia? Ta fada tana murmushin yaqe
Kura mata ido yayi, shi kansa yasan qarfin hali take wai barawo da sallama,
Your breakfast is ready ta fada cikin sanyin murya uwa tasa ihu take ji, baiyi niyar miqewa ba, hakan yasa ta qara magana, komai bai ce ba ya tashi suka fito tare.
Breakfast suke daga ita har shi bamai cewa qala kowa da abinda yake tunani har lokacin da suka kammala, kallonsa tayi da murmushi a fuskarta,
Oya get ready,
For what ya tambaya yana kallonta,
For bathing mana ango, shiru yayi baice komai ba har lokacin da tajasa toilet, suna wankan tana adduoi a xuciyarta na Allah ya kawo mata sauqin kishin da ke ranta.
El'mustapha kuwa kallonta kawai yake, sai yanda tayi dashi binta yake kamar raqumi da akalarsa.
Da kanta ta shiryasa, yau kam harda babbar riga, ta feshe shi da taurare mai sanyin qamshi, ta tsura masa ido,
Shikenan yau beautiful man din ta xai dawo nasu ita da yar'uwarta, wasu hawaye suka xo mata da sauri ta rungumesa sosai kyam a jikinta, ya saki ajiyar xuciya, rungumota yayi sosai yana shafar jikinta hade da dora kansa a kafadunta.
Jiddah ko a fasa auren ne please, nima bana so kinsani.
Ta girgixa kanta bayan ta dago tana kallonsa, auren shekara daya ne el'mustapha kayi min alqawari da lokacin ya cika xaka sauwaqe Ma uwani.
Nayi alqawari,
Kayi min alqawari baxaka taba son uwani ba amma xaka kare haqqinta na aure,
Nayi alqawari,
Kayi min alqawari baxaka juyamin baya saboda ita ba.
Nayi alqawari, sai me jiddah, tayi shiru tana sharar kwallah, talk jiddatulmusty el'mustapha naki ne, yana matuqar sonki baxai taba iya hada soyayyar ki da wata ba, trust me jiddah, idan na karya daya daga cikin alqawarin ki kibarni har abada, ta kallesa cikin son gasgasta maganar kuma hakanne.
Yau 25th ne ranar da ta amshi daurin auren El'mustapha Maneer da Aisha Adam (Uwani) miji ga Hauwa Ahmed (Jiddah ).
Auren da akayi sa acikin masallaci bayan sallah.
Jiddah ta dawo daga duba jikin banan sosai ta warware har Ma taci abinci ta saka ta tayi wanka, tana qoqarin shiga sashen ta sukayi kicibis da uwani na qoqarin fitowa, cikin wani uban lace Blue, baqaramin kyau tayi ba tasha make up wanda ya fito da sirrin kyawunta, idanu jiddah ta xuba mata cikin tsoron irin kyau da uwani tayi.
Murmushi uwani tayi tasan ko jiddah bata fada ba yanayin ta kawai ya nuna kwalliyar ta ta qawatar, ina ma el'mustapha xai shigo ya ganta shima, russunawa tayi cikin girmamawa,
'Anty jiddah tun daxu nake neman ki, yau bamu gaisa ba, kuma gashi yau rananr farin cikina ce burina ya cika na mallakar abinda nake so, qirjina ma 'ga daina min ciwo a yanxu xuwa shekara daya inaji komai xai dai dai ta na bar miki shi.
Da kyar jiddah ta iya hadiye wasu yawu da qarfi, ta tattaro nutsuwarta tana kallon uwani.
Nagani kam kwalliya kika xo ki nuna min kuma kinyi kyau, amma wanda akayi domin sa ba gani xaiyi ba ballantana ya yaba.
Nikam anty jiddah banxo dan kiji haushi ba idan Ma kika ce inje incire yanxu xanje na cire, idan kuma magana ta ce tabaki haushi kiyi haquri, xama nake so muyi dake na amana ba cutar wa.
Da xanfi farin cikin haka, ni ban iya cutar da mutum ba ballantana nayi qoqarin cin amanarsa, duk wanda nake xaune dashi da xuciya daya ne,
Ni xan iya baiwa duniya labarin wannan, kina da hali mai kyau ki godewa Allah.
Jiddah bata qara mgn ba tana qoqarin ficewa ta tsaidata,
'Anty jiddah nace kada ki gaji dani, kima yaya mgn ko ba komai ina da haqqi amin kayan aure, idan suma baida kudin ne ni xan iya rantawa na aramasa kudin yayi min,
Murmushi jiddah tayi,
Ai yanxu uwani kin fini kusa dashi, kece yar gaban goshi, ko kin manta yau kece amaryarsa sai yanda kikayi dashi,
Hakane kinyi gaskiya anti uwani daga nan ma xan masa mgnr honey moon din mu.
Kallon ta kawai jiddah tayi batace komai ba ta fice xuciyarta na mata xafi, ina Ma bata yarda da auren ba da waye uwani da xata tsaya gayamata magana haka,
Da dare uwani ta uban gayu ta gyara dakinta sai qamshin turaren wuta yakeyi, ta shirya kanta cikin wata hadaddiyar rigar barci, sai kai da kawowa take a dakin ta tana jiran xuwan el'mustapha.
Acan daki kuwa jiddah roqon el'mustapha take yaje ga uwani, qarfin haline kawai take amma kamar ta fashe da kuka takeji,
Kayi haquri mijina, ina sonka bana son Allah ya kama ka da laifin rashin adalci a tsakanin mu, ka yafemin tirsasawar danayi Ma akan auren uwani dan Allah ka yafemin, ya rungumota sosai hade da sumbatar ta a goshi,
Bana son wannan damuwar da kukan, I want my jiddah back as before, wannan ba jiddah na bace, jiddah na bata cikin damuwa, she is always happy, bata da lokacin kowa sai na mijinta ya fada yana qoqarin cusa hannuwansa cikin rigarta.
Ta soma girgixa masa kanta, please el'mustapha kaje tana jiranka, your new bride... Cak ya tsaya yana kallonta,
Jiddah ta daina sonsa a yanxu, ta daina kishinsa, yau jiddah ita ke roqonsa yaje ga wata macen, shi kam me xai tsinta a jikin uwani, mexai sa ya hada shimfida da uwani, kada Allah ya nuna masa wannan ranar.
Ya cire hannuwansa daga cikin rigarta jiki a sanyaye ya sauko daga saman gadon, bai qara waiwayen ta ba ya fice, uwani najin alamun takun mutum xai fito daga dakin ta xura da gudu daga laben da takeyi ta nufi dakin ta tana addua Allah yasa yaxo kai gaskiya jiddah mace ce mai gaskiya bata da son xuciya ai na dauka baxata barshi ya xo ba da nayi Allah ya isa domin nike da shi ehe.
Sanin muhimmanci sallama ya saka shi yinta, yana sanye da kayan barcinsa masu kyau da taushi, qamshin turaren sa ya gauraye dakin uwani wadda tun shigowar sa jikin uwani ke rawa sai take neman abinda xata rufe jikinta dashi, ita kanta batasan tana kunya da tsoron el'mustapha ba sai yau ashe duk cika baki ne takeyi a bayan idonsa, a xahiri kuwa wane ita.
Wata xungureriyar farar takarda ya miqa mata kansa a sunkuye har lokacin bai kalle ta ba,
Jikinta ya dauki rawa, ta soma ganin dakin na juyawa da ita, takardar mecece yake bata kada dai el'mustapha ya sake ta ne, a daren ta na farko, daren da kowace mace take alfahari da farin ciki dashi.
Jikinta yayi sanyi ta kasa miqa hannu ta karbi takardar, ba dan komai ba sai dan tsoron abinda xata tarar acikinta.
Ganin haka el'mustapha ya ajiye mata takardar a gefen gadon da take xaune, ya juya ba tare da yayi magana ba ya fice.
Pherty..... ✍🏻
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
25
Zuru tayi tana kallon farar takardar, har lokacin jikinta rawa yake, kafin ta fara kuka.
Dakin dasu banan suke a bayan gidan ta nufa, maaikatan sai gaidata suke cikin girmamawa yara da manya, cikin sakin fuska take amsa masu kamar yanda ta saba, tsofaffin Dany take barkwanci da su kuwa suna tabawa suna dariya kamar wacce bata da damuwa a tare da ita.
Ni kam tun jiya banga banan ba, lafiya dai ko.
Ai banan bata lafiya hajiya tun jiya tana fama da xaxxabi.
Subhanallah amma shine ba wanda ya sanar dani, ta shiga dakin tana fadin tasha magani kuwa.
Banan na kwance xaxxabi take, tun lokacin da taji ana maganar uwani xata auri el'mustapha, ta riqo hannu jiddah jikinta yayi xafi rau sai makyarkyata take,
'Anty jiddah wai da gaske uwani xata auri Alhaji?
Eh mana yau ake daurawa Ma, me akayi.
Banan ta fara hawaye sosai, anty jiddah kar ki barta ta aure sa dan Allah.
Meyasa banan
Saboda ita muguwa ce, bata da tausayi bata dace dashi ba.
Jiddah ta share mata hawaye, ko kadan bata da kyankyami akan masu aikinta, ta riqo banan sosai, tace uwani ta canxa kuma xakiyi mamaki kada kisa damuwa a tare dake, uwani kuma taimakonta xanyi dalilinsa ta kamu da ciwon xuciya.
Banan tayi shiru kenan itama idan anti jiddah taji dalilin el'mustapha ne bata da lafiya itama xata barta ta aure sa, no baxan iyama anti jiddah haka ba xan cigaba da boye mata koda kuwa sonsa xai xama ajalina cos nasan el'mustapha baxai taba son Irina ba, ina Ma ko sau daya ne na ganshi, tunda nake gidannan ban taba ido da ido dashi ba sai dai kallo daga nesa.
Tashi ki shirya yanxu xaa kaiki asibiti kinji banan.
Ba musu kuwa ta tashi ta soma shiryawa, jiddah na fitowa sashen kitchen din ta tanufa,
Har ta gama shirya masa breakfast wani abu na nan a qirjinta ya tokare mata,wai ita ce da kishiya a yau, anya tayi Saar xuwa duniya kuwa, ko da yake itace ta jawa kanta, amma ita da xuciya daya tayi taimakon kuma tasan baxata taba tabewa ba.
Dai dai lokacin da suke ganiyar soyayyar su da el'mustapha a lokacin wata xata shigo rayuwar su, su dinga sharing love, anya xata iya? Wata ta dinga yin abinda suke da mijinta, rumtse idonta tayi ta jingina da bangon kitchen din da yaji marbles, hawaye mala mala a fuskarta a hankali ta dinga furta Inna lillahi wa Inna ilaihir raji'un,
A hankali ta fara samun sa'ida a xuciyarta har ta sami relief, ta kwashi kayan ta soma hadawa a dining,
Ta qara shiga dakin nasa, yana kwance wannan karon kansa na kallon fankar dakin, ya riqe goshinsa da hannunsa daya,
Gefen gadon ta xauna hade da Jan yatsar qafarsa, el'mustapha lafia? Ta fada tana murmushin yaqe
Kura mata ido yayi, shi kansa yasan qarfin hali take wai barawo da sallama,
Your breakfast is ready ta fada cikin sanyin murya uwa tasa ihu take ji, baiyi niyar miqewa ba, hakan yasa ta qara magana, komai bai ce ba ya tashi suka fito tare.
Breakfast suke daga ita har shi bamai cewa qala kowa da abinda yake tunani har lokacin da suka kammala, kallonsa tayi da murmushi a fuskarta,
Oya get ready,
For what ya tambaya yana kallonta,
For bathing mana ango, shiru yayi baice komai ba har lokacin da tajasa toilet, suna wankan tana adduoi a xuciyarta na Allah ya kawo mata sauqin kishin da ke ranta.
El'mustapha kuwa kallonta kawai yake, sai yanda tayi dashi binta yake kamar raqumi da akalarsa.
Da kanta ta shiryasa, yau kam harda babbar riga, ta feshe shi da taurare mai sanyin qamshi, ta tsura masa ido,
Shikenan yau beautiful man din ta xai dawo nasu ita da yar'uwarta, wasu hawaye suka xo mata da sauri ta rungumesa sosai kyam a jikinta, ya saki ajiyar xuciya, rungumota yayi sosai yana shafar jikinta hade da dora kansa a kafadunta.
Jiddah ko a fasa auren ne please, nima bana so kinsani.
Ta girgixa kanta bayan ta dago tana kallonsa, auren shekara daya ne el'mustapha kayi min alqawari da lokacin ya cika xaka sauwaqe Ma uwani.
Nayi alqawari,
Kayi min alqawari baxaka taba son uwani ba amma xaka kare haqqinta na aure,
Nayi alqawari,
Kayi min alqawari baxaka juyamin baya saboda ita ba.
Nayi alqawari, sai me jiddah, tayi shiru tana sharar kwallah, talk jiddatulmusty el'mustapha naki ne, yana matuqar sonki baxai taba iya hada soyayyar ki da wata ba, trust me jiddah, idan na karya daya daga cikin alqawarin ki kibarni har abada, ta kallesa cikin son gasgasta maganar kuma hakanne.
Yau 25th ne ranar da ta amshi daurin auren El'mustapha Maneer da Aisha Adam (Uwani) miji ga Hauwa Ahmed (Jiddah ).
Auren da akayi sa acikin masallaci bayan sallah.
Jiddah ta dawo daga duba jikin banan sosai ta warware har Ma taci abinci ta saka ta tayi wanka, tana qoqarin shiga sashen ta sukayi kicibis da uwani na qoqarin fitowa, cikin wani uban lace Blue, baqaramin kyau tayi ba tasha make up wanda ya fito da sirrin kyawunta, idanu jiddah ta xuba mata cikin tsoron irin kyau da uwani tayi.
Murmushi uwani tayi tasan ko jiddah bata fada ba yanayin ta kawai ya nuna kwalliyar ta ta qawatar, ina ma el'mustapha xai shigo ya ganta shima, russunawa tayi cikin girmamawa,
'Anty jiddah tun daxu nake neman ki, yau bamu gaisa ba, kuma gashi yau rananr farin cikina ce burina ya cika na mallakar abinda nake so, qirjina ma 'ga daina min ciwo a yanxu xuwa shekara daya inaji komai xai dai dai ta na bar miki shi.
Da kyar jiddah ta iya hadiye wasu yawu da qarfi, ta tattaro nutsuwarta tana kallon uwani.
Nagani kam kwalliya kika xo ki nuna min kuma kinyi kyau, amma wanda akayi domin sa ba gani xaiyi ba ballantana ya yaba.
Nikam anty jiddah banxo dan kiji haushi ba idan Ma kika ce inje incire yanxu xanje na cire, idan kuma magana ta ce tabaki haushi kiyi haquri, xama nake so muyi dake na amana ba cutar wa.
Da xanfi farin cikin haka, ni ban iya cutar da mutum ba ballantana nayi qoqarin cin amanarsa, duk wanda nake xaune dashi da xuciya daya ne,
Ni xan iya baiwa duniya labarin wannan, kina da hali mai kyau ki godewa Allah.
Jiddah bata qara mgn ba tana qoqarin ficewa ta tsaidata,
'Anty jiddah nace kada ki gaji dani, kima yaya mgn ko ba komai ina da haqqi amin kayan aure, idan suma baida kudin ne ni xan iya rantawa na aramasa kudin yayi min,
Murmushi jiddah tayi,
Ai yanxu uwani kin fini kusa dashi, kece yar gaban goshi, ko kin manta yau kece amaryarsa sai yanda kikayi dashi,
Hakane kinyi gaskiya anti uwani daga nan ma xan masa mgnr honey moon din mu.
Kallon ta kawai jiddah tayi batace komai ba ta fice xuciyarta na mata xafi, ina Ma bata yarda da auren ba da waye uwani da xata tsaya gayamata magana haka,
Da dare uwani ta uban gayu ta gyara dakinta sai qamshin turaren wuta yakeyi, ta shirya kanta cikin wata hadaddiyar rigar barci, sai kai da kawowa take a dakin ta tana jiran xuwan el'mustapha.
Acan daki kuwa jiddah roqon el'mustapha take yaje ga uwani, qarfin haline kawai take amma kamar ta fashe da kuka takeji,
Kayi haquri mijina, ina sonka bana son Allah ya kama ka da laifin rashin adalci a tsakanin mu, ka yafemin tirsasawar danayi Ma akan auren uwani dan Allah ka yafemin, ya rungumota sosai hade da sumbatar ta a goshi,
Bana son wannan damuwar da kukan, I want my jiddah back as before, wannan ba jiddah na bace, jiddah na bata cikin damuwa, she is always happy, bata da lokacin kowa sai na mijinta ya fada yana qoqarin cusa hannuwansa cikin rigarta.
Ta soma girgixa masa kanta, please el'mustapha kaje tana jiranka, your new bride... Cak ya tsaya yana kallonta,
Jiddah ta daina sonsa a yanxu, ta daina kishinsa, yau jiddah ita ke roqonsa yaje ga wata macen, shi kam me xai tsinta a jikin uwani, mexai sa ya hada shimfida da uwani, kada Allah ya nuna masa wannan ranar.
Ya cire hannuwansa daga cikin rigarta jiki a sanyaye ya sauko daga saman gadon, bai qara waiwayen ta ba ya fice, uwani najin alamun takun mutum xai fito daga dakin ta xura da gudu daga laben da takeyi ta nufi dakin ta tana addua Allah yasa yaxo kai gaskiya jiddah mace ce mai gaskiya bata da son xuciya ai na dauka baxata barshi ya xo ba da nayi Allah ya isa domin nike da shi ehe.
Sanin muhimmanci sallama ya saka shi yinta, yana sanye da kayan barcinsa masu kyau da taushi, qamshin turaren sa ya gauraye dakin uwani wadda tun shigowar sa jikin uwani ke rawa sai take neman abinda xata rufe jikinta dashi, ita kanta batasan tana kunya da tsoron el'mustapha ba sai yau ashe duk cika baki ne takeyi a bayan idonsa, a xahiri kuwa wane ita.
Wata xungureriyar farar takarda ya miqa mata kansa a sunkuye har lokacin bai kalle ta ba,
Jikinta ya dauki rawa, ta soma ganin dakin na juyawa da ita, takardar mecece yake bata kada dai el'mustapha ya sake ta ne, a daren ta na farko, daren da kowace mace take alfahari da farin ciki dashi.
Jikinta yayi sanyi ta kasa miqa hannu ta karbi takardar, ba dan komai ba sai dan tsoron abinda xata tarar acikinta.
Ganin haka el'mustapha ya ajiye mata takardar a gefen gadon da take xaune, ya juya ba tare da yayi magana ba ya fice.
Pherty..... ✍🏻
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
25
Zuru tayi tana kallon farar takardar, har lokacin jikinta rawa yake, kafin ta fara kuka.