← Book details El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 80

Sashe 59

El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

El'mustapha na bayan ta suka shigo, lokaci daya suka kalli uwani, el'mustapha ya nufi dakin sa batare da yayi magana ba,

'Anty ikram tace, ke xaman me kike anan?

Uwani ta tashi tana inda inda dama tana tsoron anty ikram sosai bata taba sake mata fuska ba,

Anti ikram tace karna qara xuwa na same ki xaune a falon nan dai dai lokacin da mai gidan xai dawo, idan inda jiddah kika xo ki same ta a ciki kiyi abinda xakiyi ki fice bawai ki xauna mata ba,

Uwani ta gyada kai tana kallonta, ita kadai ce xata iya gayawa uwani magana ta kyale ta batare da ta maida martani ba, ita kanta uwani ta rasa meyasa take tsoron matar nan haka, shiyasa anti ikram ke daukar duk abinda uwani keyi iskanci ne ba wani hauka dake damun ta.

Fita daga falon nan kuma karna qara jin kin tsaya da el'mustapha idan bada amincewar jiddah ba, maganar a baki key kidawo dakin ki babu ta, jiddah bata so kuma el'mustapha ma baya so to xaman me xaki xo ki masu, idan aure kike so kije ki sami naki mijin a waje ko dole sai el'mustapha ne?

Uwani batayi magana ba ta juya tana kuka, ikram taja tsaki ta nufi dakin jiddah ta same ta xaune akan stool tana shafa mai.

Ta cikin madubi jiddah ke kallonta kafin ta gaida ta,

Ikram ta xauna dai dai lokacin el'mustapha ya shigo idanun sa akan jiddah.

Jiddah xo xauna nan magana xamuyi cewar ikram,

Ba musu jiddah ta tashi ta nufi inda take nuna mata ta xauna, idanunta na kallon kasa.

El'mustapha ya gayamin abinda ya faru tsakanin ku, duk irin mgnr da mukayi dake kin manta kenan, me na gayamaki idan el'mustapha ya bata maki.

Jiddah ta daqo tana kallonta idanunta taf da hawaye, ta kasa magana sai motsa bakin take,

Kiyi magana jiddah,

Da kyar cikin rawar murya tace, cewa ki.. kayi na kira ki na fada maki.

To meyasa baki kirani ba jiddah, amma shi gashi kinga ya kirani, ko dan ni ba yayar ki bace yayar el'mustapha ce kawai.

Jiddah ta girgixa kanta tana share hawaye,

Me yayi xafi haka har kike neman yaji, menene amfanin yaji ga mace, idan kika je kika barshi farin cikin yaran ki fa, sannan shi bakya tunanin halin da xaki saka shi, kenan el'mustapha idan ya maki magana ba kya bi, ba kya bin umarnin sa?

Jiddah ta girgixa kanta batare da tayi magana ba,

Ikram tace to meyasa idan ya maki magana bakya ji, yayi ta baki haquri kinqi.

A sanyaye tace ina bin maganar sa.... yimin shiru ikram ta katse ta cikin daure fuska,

Magana xan gayamaki kada ki koyawa mijinki qin jin rarrashi, ina nufin idan ya rarrashe ki to ki haqura,

Idan kika bari ya saba da idan ya rarrasheki kinka qi ji kika kangare wai ke Jan aji ko taurin kai daina rarrashinki xai yi yana tunanin ko yayi baxaki ji ba, kinga daga nan kin dauko hanyar da xai daina jin tausayin ki, ina gayamaki ne ba dan yana qanina bane kema qanwatace shiyasa na fada maki duk abinda yayi maki na bacin rai just take your phone and call me kigani idan ban xo na kwatar maki yancin ki ba.

Amma anty ikram meyasa xai nuna yafi tausayin uwani akaina, meyasa xai tsawa tamin akan ta har yana kirana marar hankali dalilin ta, kenan uwani ta fini a gurinsa.

Sosai anty ikram ta hau sa da fada da nuna masa rashin kyautawarsa, jiddah matar sace saboda me xai fifita uwani akanta, meyasa xaifi tausayawa uwani akan halin da ta saka jiddah a baya.

Ya sosa kansa, ya lura fushin na jiddah ba akan Marin da yayi mata bane tunda har batayi magana ba,

Yace sister ayi haquri

Kuma maganar duka kada ka qara El'mustapha sam banji dadi ba, ka hukuntata dai dai laifinta amma banda maganar duka, ko kadan bana son namiji mai dukan mace ko yane...

Yace kuskure ne na karbi laifina,

Jiddah bata ce komai ba, el'mustapha ya tashi ya fita,

Ikram ta soma bata baki tana rarrashin ta banda wauta irin ta jiddah saboda me xata damar da kanta akan uwani, ko mutuwa xatayi baxata auri Musty ba, ki kwantar da hankalin ki, mijinki shine farincikin ki, ki bi duk abinda yake so ki gujewa wanda baya so xakiji dadi, yanxu idan kina haka amira tayi kice mata me? Da yayi maki wani misbehaving da bakya so dauki waya kirani kigani, idan naxo idan ban mashi hukunci ba,.

Bata bar gidan ba har sai da ta saka jiddah dariya, ikram na barin dakin ya dawo kusa da ita ya xauna, tafin hannunta ya riqo ya hada da nashi yana murxawa a hankali.

Wani irin yanayi da take ji ne ya tilasta mata lumshe idanuwanta,

Kin yafe min dukan da na maki jiddah.

Ta daga kanta a hankali batare da ta kalle sa ba, ya jawota sosai ya rungumeta, lokaci daya suka sauke numfashi.

Al'amarin daya biyo baya baxai fadu ba🤧 da kyar ta janye bakinta daga nasa,

Yana kallonta yace bani abinci naci jiddah, yau komai ban ci ba tun safe.

Ta tashi a sanyaye ta fita batare da tayi magana ba, yabi bayanta da kallo kawai.

'Ko da ya gama cin abincin jiddah bata dakin tana falon ta, da alama har yanxu bata sauko daga fushin ba.

Shi yanxu damuwar sa hannunsa dake masa zugi tun daxu.

Da dare sai juyi yake akan gado ya kasa barci saboda xafin ciwon hannun, gashi ya kumbura, kallon jiddah yake barcin ta take cikin kwanciyar hankali.

Time ya duba, biyu na dare ya gota, ya sauko daga saman gadon ya fita daga dakin.

Sai safa da marwa yake tsakanin falon sa dana jiddah, yanda yake ji a hannunsa ya tilasta masa xuwa dakin da abba yake ba shiri.

A hankali yake buga qofar dakin,

'Abba ya tashi yana tambayar waye? Jin muryar el'mustapha ya taso da sauri ya bude dakin yana tambayar lafiya?

'Na kasa barci, hannuna ke ciwo sosai... El'mustapha ya fada yana nunawa abba hannun.

'Abba ya duba hannun yana fadin ai gocewar qashi ne el'mustapha me ya jima ka ciwo haka.

Ya yatsina fuska kafin yace na dan xame ne daxu a toilet na fadi, yanxu ya xanyi abba.

Daurewa xaka yi kayi haquri har xuwa gobe sai kaje asibiti ko kuma ayi maka aikin gida duk wanda kake so amma ni bani da sani akan irin wannan matsalar.

Shiru el'mustapha yayi kafin ya juya yana fadin Allah ya kaimu goben.

Xama yayi bakin gadon ya dafe kansa da hannunsa daya, dole ya sami gocewar hannu saboda girma da nauyin kujerar, inda ta sami uwani a kai kenan xaa sami matsala ba babba dan ya tabbata kwakwalwar ta gabaki daya xata juye.

Jiddah ta bude ido tana kallonsa, kallon agogon tayi kafin ta maida kallonta garesa cikin mamaki, meke damun el'mustapha, me ya hana masa barci a wannan lokacin yake xaune?

Ta matso a hankali xuwa inda yake, hannunta ta kai wuyansa ta taba tunanin ta ko xaxxabi ne,

Ya dago yana kallonta, ita ma shi take kallo
Tace meke damun ka?

Da kyar yace ba komai.
'amma naji jikinka da xafi ko baka da lafiya ne?

Ya girgixa kansa kafin yace ki kwanta jiddah ba abinda ke damuna.

Ta gyara xamanta sosai tana kallonsa,

'Na kwanta nayi barci kai kuma kana xaune, idan lafiyar ka qalau tunanin me kake yi el'mustapha?

Yayi shiru baiyi magana ba, ganin ta matsa da tambaya ya nuna mata hannun.

Tayi shiru gabanta na faduwa tana kallon yanda hannun ya kumbura, ta kasa daqowa ta kalle sa harda wani nauyin sa take ji.

Yaja numfashi kadan yana fadin kije ki kwanta tun kafin airah ta tashi gobe kixo kina complaining baki sami barci ba,

Ta girgixa kanta kafin tace kayi haquri n..... Shishsssss ya katseta ta hanyar dora yatsanta akan labbanta yana kallonta.

Kije ki kwanta bana son gardama,

Ta matsa kadan daga garesa amma taqi kwanciya, bata da wannan nutsuwar bata san yanda yake ji ba ta tabbata duk abinda xai hanawa el'mustapha barci ba qaramin abu bane.

Ganin taqi ta kwanta ya saka shi kwanciya yana fadin xo mu kwanta jiddah nima barci nake ji.

Ta matsa ta shiga cikin jikinsa, ya rungumeta yana lumshe idanuwansa ba dan ya daina jin xafin hannun ba.

'Washe gari ko da jiddah ta tashi el'mustapha baya gidan, tayi mamakin ina xaije da sassafe haka kuma tana da tabbacin ko wanka bai yi ba ya fita.

Ta shiga kitchen ta sami hajiya tana hada breakfast, gaidata tayi kafin ta soma taya ta suna yi suna fira jefi jefi cikin nishadi har suka kammala.

Goma na safiyar ranar el'mustapha ya shigo da alama gurin gyara ya tafi ganin yanda aka daure masa hannu.

Kai tsaye dakin sa ya nufa, jiddah tabi bayansa kallonsa take a sanyaye,

Sorry el'mustapha kayi haquri dan Allah,

Yace bani ruwa na sha magani, da sauri ta fita bata jima ba sai gata dauke da Swan da cup, da kanta take balla mashi maganin yana sha.

Ganin yana qoqarin cire rigar jikinsa ta taimaka mashi ta cire masa, ya kwanta yana fadin,

Kada ki tada ni jiddah, duk wanda yaxo bana nan,  na kashe wayar ma har yaranki kada ki bari su xo su dame ni.

Ta tashi tana fadin asha barci lafia, ya dan kalle ta yace lullubamin blanket sai ki kunna min AC.

'Ko da su abba suka gama shirin tafiya jiddah har tayi wanka, ta shirya twins ta bawa driver ya kaisu inda anty yusrah har anjima kada rigimarsu ta tada mahaifinsu daga barci.

'Abba yace ina el'mustapha da hannu, jiya bai sami barci ba ashe ya xame ya fadi ne yaji ciwo.

Jiddah tace bai jima da dawowa gurin gyara ba, ya sami barci yanxu.

Hajiya tace Allah ya bashi lfy idan ya tashi ina mishi ya jiki.

'Abba yace mu xamu tafi idan ya tashi ki gaidasa.

Suka firfito harabar gidan, jiddah dauke da airah sai wasa take mata tana dariya,

'Abba ya dubi uwani yana fadin ke kuma fa ina kayanki?

Uwani ta tunxure baki tana fadin ni xan raka ku ne ku tafi ba inda xanje ni.
Chapter 59 · 0% Book details