← Book details El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 80

Sashe 52

El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Haka ta tattara ta dawo gida, abba ya fito neman inda taje ya ganta da jaka shabe shabe da hawaye.

*

Dr Merah ya shigo dakin da sassafe, ward round kamar yanda yake yi kowace Safiya kafin ya isa office din shi.

Yayi mamakin samun jiddah ita kadai a dakin tunda yake xuwa ita da  el'mustapha yake samun ta ko wace Safiya kuma ai yaga el'mustapha xaune a waje me ya hanasa shigowa, tabbas akwai matsala,

duk da halin-sa-ido ba halinsa bane amma wannan dai confrontation ne like a chase game da yakeson ganin yanda xai qare, el'mustapha a waje ba walwala, jiddah a ciki cikin damuwa.

dan haka yake ganin bai kamata ya kira sa-idon nasa da sunan sa-ido ba sai dai ya kirashi curiosty wanda haline na kowane dan adam akan abinda ya bashi mamaki musamman shi da yake ganin el'mustapha yanxu abokin sa ne, jiddah kuma patient din sa ce.

Bayan ya gama duba ta, kallonta yayi yana fadin lailah ina majnun ya akayi na same ki ke kadai yau,

Murmushi kawai tayi tana kallonsa,

As a professional medical doctor a take dr.merah ya gano cewa akwai damuwa a tare da ita daga yanayin ta, yanda ya san ta da fara'a.

Kujera ya janyo ya xauna yana fuskantarta,

Akwai damuwa jiddan musty ne ko ya kuke cewa, nagano patient dita tana cikin damuwa ni kuma bana son ganin ta cikin damuwa, kullum naxo xan same ki tare da mijin ki, yau kuma meyasa?

Tayi rau rau da idanunta kafin tace ba komai, ya dan fita ne.

Aa jiddah, your eyes shows akwai matsala, idan akwai abinda xan iya taimaka maki just take me as your brother ki gayamin,

Ta bude baki da kyar tana kallonsa, aure yake so ya qara...

Aure? Dr merah ya tambaya cikin tsananin mamaki, meyasa yake son qara auren?

Tace saboda na nakasa yake son qara aure bayan ya manta dalilin sa na fada wannan halin, saboda son da ake mashi aka nemi kasheni a rabani da duniyar..... ta soma kuka sosai har ranta.

Shiru dr merah yayi amma jikinsa yayi sanyi sosai, kuma el'mustapha ya bashi mamaki, kukan jiddah na qara tayar mashi da hankali.

Yace kibar kukan jiddah, nasan el'mustapha yana matuqar son ki, bana jin saboda kin nakasa xai qara wani auren ballantana Ma baki nakasa ba jiddah, xaki tashi aikin da aka maki is successful, nan da wata daya xuwa biyu xaki fara taka qafar.

Ta dubesa idanunta jawur, yana sona ne baxai xauna dani hakan ba.... Ya katse ta,

Ni nasan el'mustapha baxai qara aure ba ki kwantar da hankalin ki, kidaina saka damuwa a xuciyarki kinga baki da lafia, idan har el'mustapha xai qara aure baxai gayamaki a wannan halin da kike ciki ba domin yafi kowa sanin condition din ki, el'mustapha yasan *Labari na* dana gidana, haka shima ya bani nashi har dalilin wannan ciwon naki amma bai taba gayamin yana son wata ko niyar aure ba.

Xai iya gaya maka komai amma baxai taba gayamaka yana cin amanata da mai aikina ba, ita yake so a yanxu kuma ita yake son aure, ka gayamin ina adalci anan, ina son da yake ikirarin yana min idan har xai iya auren yarinyar dana raina a hannuna?

Dr merah ya bata fuska alamar fushi mai tsanani a tare dashi, idan har da gaske kike abinda kika fada el'mustapha bai kyauta ba kuma baxai taba auren yarinyar da kika rena ba sai dai ya auri wata can d..... Jiddah ta katse sa,

Wata din Ma baxai aura ba, a hakan xai xauna dani ko yana so ko baya so, idan har dole sai ya auri wata ni baxan xauna dashi ba, baxan yarda na qara cutar da rayuwata ba duk da na farkon nice sanadi ni na jawa kaina.

Murmushi merah yayi ganin yanda take magana cikin seriousness, ya tashi yana fadin xan turo maki el'mustapha, baxan lamunta da wannan fushin da kuke da juna ba, kuma ina goyon bayanki karki yarda ya qara auro maki wata, idan yace xai qara aure xan gayamaki wani sirri da Afiya ke min barazana dashi a duk lokacin da na kalli wata ko nace xan qara aure koda da wasa ne.

Tayi murmushi cikin jin dadi tana kallonsa tana mamakin girman qasaitarsa tana mamakin yanda yake furta mgn da kyar, duk mgnr da ke fitowa bakinsa idanunsa akan wayarsa wanda idan bata manta lbrn Yarima maina ba da Sarautarsa data qaryata qasaitarsa(masu yawan tambayata labarin dr Merah kuduba littafin mulki ko sarauta a wattpad)

Ya dago yana kallonta,
El'mustapha baxai qara aure ba jiddah, yanxu na xama yayanki baxan bari a qara cutar da ke kamar a baya ba, kema sai kin dage damtse wajen saurin yarda da mutum da bashi amanarki.

Tace nagode... Ya juya ya fice cikin tafiyar sa ta qasaita, yana fitowa ya hadu dasu yusrah sun shigo suka gaisa kana ya dubi el'mustapha yaja hannunsa suka nufi office din sa.

Aure kake son qarawa el'mustapha meyasa? Dr merah ya tambayesa idanunsa akan laptop kamar ba shi bane ke tambayar.

El'mustapha ya qara bata fuska, wato jiddah tana gayawa mutane aure xai qara... Jin shiru ya saka merah kallonsa,

As a friend, ban boye maka kaina ba kai kana boye min, banyi mamaki ba tunda har xaka iya cutar da innocent girl like jiddah ka munafunceta kana tare da mai aikinta, dan me ni baxaka munafurceni ba nida haduwar asibiti ce?

Murmushi ya subulcewa el'mustapha, yanxu abin ya daina bashi haushi,

Yace a tunanin ka saboda me xan qara aure saboda me xanci amanar jiddah?

Yace saboda kana ganin ta nakasa....

'Ashe bakin ku daya da jiddah cewar El'mustapha, ban sani ba ko kai ke shirya mata wannan saboda nasan halin jiddah bata da wannan xafin dana gani a tare da ita jiya.

Dr merah ya dube sa, yace eh nine ke shirya mata me xaka iya yi, idan kai mijinta ne ni kuma qanwata ce kuma patient dita baxan so naga an cutar da ita ba.

El'mustapha yayi murmushi yana fadin ba abinda xan iya yi amma komai mulkin mutum da sarauta baifi qarfin Shari'a ba kuma tsab dan sanda mai babban muqami Irina xai iya kamashi.

Dr merah yace duk wata baraxana ta dan sanda bata tsorata ni ballantana tayi tasiri a kaina inada mulkin da xan saka..... El'mustapha ya katse sa,

Aure na, matsalata, matata ba damuwar ka bane is my personal issue da bana son kowa ya saka kanshi aciki.

Ni kuma dole xan saka kaina aciki an you have to listen, labarin da kabani jiddah tana yin komai ne saboda kai da soyayyar da take Ma, kuma dalilin ka ta shiga wannan halin da take ciki, but why kake son auren mai aikin gidan ka can you imagine, har yaushe ka sake mata wannan fuskar, yaushe ka fara sonta, mace mai kyau da aji, mace mai mulki da sarauta kamar ni bata isheni kallo ba saboda ina ganin na aje wadda ta fiye min ita fiye da komai nawa, nima matata ta wahala dani na gayama, har muka haihu ban taba furta mata kalmar so ba cos a lokacin ban gane miye so ba sai bayan tafiyar ta, na gayama yanda ta wahala da yanda tayi rainon sultan da yanda family suka juyamin baya dalilinta, I told you everything about me an Afiya, wahalar da mukayi da juna baxai saka na iya cin amanarta da kowace mace ba ballantana yar aiki thought ba haramun bane amma Sam bai dace ba tun da ita ce ta raineta, ita Ma yarinyar taci amanar jiddah, ka wahala da jiddah, jiddah ta wahala da kai,

Ita Mace komai girmanta yar rarrashi ce da tarairaya, (care and concern) abinda take so kenan daga namijin da take so, wallahi jiddah tana sonka, dubi idanunta ba Komai aciki sai xallar soyayyar ka, kaima kana son jiddah ni shaida ne, but why El'mustapha?

El'mustapha yaja numfashi yana kallonsa,

Yace Wallahi bana son Banan kuma bani da niyar qara aure a xuciya ta da wata mace ballantana banan, baxan boye Ma ba before na fara jin feelings akan yarinyar tun jiddah nada lafiyarta bawai bayan ta nakasa ba, ban taba sanin jiddah tayi wa yarinyar miji ba sai bayan jiddah ta kwanta asibiti sunxo duba jiddah tare dashi.

A lokacin da jiddah fa gayamin banji haushi sosai ba tunda ban riga na kamu da son ta ba, kuma tun daga lokacin bana mata wani kallon bayan qanwa, ta wahala da yarana ta wahala da jiddah, tayi wa yarana riqon da ko mama ke da rayuwa a yau shi xata yi masu bayan ido na, just tell me Merah wanda ya kula da yaranka ya xauna dasu fitsarin su da kashin su xaka iya wulaqantashi? Idan har na dauki banan a matsayin qanwata saboda me baxan sakar mata fuska ba, dole sai ana soyayya ake sakin fuska, ballantana jiddah bata taba kamani da yarinyar nan ba, kawai xargi take wallahi ban taba tsayuwa da banan da sunan soyayya ba, is either akan yarana or gidana da matata, amma ban san xuciyar yarinyar ba tunda jiddah tace wai banan tana sona, ni ban san da wannan ba kuma ban taba lura ba saboda ban damu da ita ba.

'Na yarda da kai el'mustapha shiyasa na gayawa jiddah bana xaton xaka iya cin amanarta, yanxu na fahimci laifin daga ita banan din ne, tana so ta rusa maku farin ciki da xaman lafiya, idan har jiddah tayi mata miji kuma ta amsa a tana sonsa saboda me xata so mijin uwar rainonta?

Mata kenan... El'mustapha ya fada yana jan tsaki, ya lumshe idonsa cikin takaici.

Banan kin gama hada kayan naki kuwa? Cewar yusrah tana kallon ta,

'Na gama anty ta fada a sanyaye, jikinta duk yayi sanyi jiya ko barci bata samu tayi ba saboda damuwa xata je ta daina ganin sanyin idaniyar ta.

A fakaice ta share hawayen fuskarta, tun bata kai wannan lokacin ba take son el'mustapha tana dawainiya dashi a xuciyarta, ta haqura dashi ta karbi Islam a matsayin mijin auren ta saboda a lokacin tana ganin el'mustapha yafi qarfinta kuma uwani baxata taba yarda a aure ta ba.
Chapter 52 · 0% Book details