Sashe 56
El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Uwani tayi saurin tsaida ta,
'Dan Allah anti jiddah ki yafe min, nasan kin tsane ni a ynxu amma kiyi haquri ki bani dama ta biyu na xauna dake baxaki taba dana sani ba, ki aura min El'mustapha a karo na biyu wallahi ina son.... bata qara sa ba jiddah ta dauke ta da Mari, kafin tayi wani yunquri ta sake wanke fuskarta da Mari hade da hankadata ta fadi ragwaf.
Ko yawo xakiyi tsirara a duniyar nan kina bin bokaye, ko ciwo xakiyi kina aman jini kina mutuwa kina tashi baxaki taba auren *EL'MUSTAPHA* ba kuma kiyi gaggawar barin gidan nan kafin na fito nasa a wulaqantaki a gidannan.
*EL'MUSTAPHA*
*Haske Writers Association*
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
_God bless this special best friend of mine with all happiness and accomplishment in life, I’m truly blessed to have you as my best est buddy *khadija Ahmed KDEEY*_ 🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂
_Happy Birthday to my best daughter, Thinking of you with love on your birthday and wishing you everything that brings you happiness today and always, I’m truly blessed to have you as my best est buddy *Sumayya Halliru Dikko*_🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂
56
Uwani ta xube gurin hankalinta a tashe,
Me jiddah ke nufi da ko xata mutu baxata taba aura mata el'mustapha ba, kenan jiddah tana nufin ko ma me xatayi sai dai tayi amma baxata qara auren mijinta ba.
Yaushe jiddah ta canxa haka? Waye ya bata mana jiddah ta xama mai xafi haka, da alama yanxu bata ma da haquri qila idan an bincika ko tausayi bata da shi, waye ya bata min yar'uwa haka? Indai ba ta sami qawa mai xugata irin jamcy ba.
Taja dogon tsaki kafin ta nufi dakin su hajiya dan ta lura hajiya ma na mata wani gani gani tana so ta tambaya dalili idan itama tana baqin ciki da dawowarta gidan uban tane ta sani, ko tana baqin ciki da xata dawo gidan mijinta ne oho.
Jiddah ta ajiye airah akan bed tana kallon el'mustapha,
Wani abin mamaki, Uwani ke roqona na barta ta auri mijina a karo na biyu, bata neman gafara ta sai ma ta mijina take.
El'mustapha ya matsa kadan inda ta shimfide Airah barci take, ya tsurawa fuskarta ido yana kallonta,
Yace ai nasan jiddah mai haquri ce da tausayi, ina tunani ma yanxu tausayin ne ya saka taxo ta gayamin uwani na son komawa dakin mijinta, nasan yanxu xaki fara kuka kina roqona na maida uwani yar uwar kice ciwon xuciya zaya kamata ke kuma baki so ki rasata saboda halaccin iyayenta.
Ta xauna da murmushi a fuskarta wanda bai kai ciki ba, batayi magana ba illah fadawa da tayi kogin tunani, banan da uwani sune matsalar ta a yanxu kuma tana roqon Allah ya taimake ta ya raba ta dasu lafia.
El'mustapha ya daqo yana kallonta,
Tunanin me jiddatulmusty take yi?
Tace ba komai,
Ya tashi ya cire doguwar jallabiyar dake jikinsa, kafin ya qara kallonta,
Ina so na dauko wata mai aiki saboda Airah ke kuma kiji dani,
Ta ware idanu tana kallonsa,
What? Mai aiki, wace irin mai aiki kuma el'mustapha? Kai baka ga halin da nake ciki bane, Dame xanji ni kuma me xanyi da mai aiki.
Ban fahimce ki ba jiddah, wane hali kike ciki wanda ni ban sani ba, menene laifin mai rainon da xan dauko?
Ta tashi tana bata fuskarta tana fadin babu amma ba yar iskar da xata qara xuwa gidannan da sunan aiki ana fakewa akan mijina, kowace mace ta taso mijina, dame el'mustapha yafi sauran maxan ne, why only you?
Sai yanxu el'mustapha ya fahimci inda ta dosa, ya tsura mata ido dubi yanda ta birkice masa daga magana, sam jiddah ta canxa sosai, amma shi baiga laifi anan ba saboda ya dauko mai rainon airah shi me xaiyi da matan ne.
Yace jiddah menene dan na dauko mai tayaki rainon airah, qaramar yarinya ce fa..... ta katse sa,
Qananan yaran ne kemin raino nima ina rainon su da sun girma basu da abin so sai mijina, ni xan iya rainon airah saboda ba abinda nake yi a gidannan sai girkinka da kula da sashen ka, idan ka matsa dole sai an dauko mai raino na amince amma fa namiji xaka dauko yayi rainon airah.
Ya bude idanunsa sosai yana kallonta bayan ya gyara tsayuwarsa,
Namiji jiddah? Wane irin namiji xan dauko yayi min rainon ya'mace? Me ma xai kawo namiji har cikin gidana da falona yana kallon matata.....
Tace nima babu macen da xaa dauko taxo tana kalle min miji, ban nemi xama da mai aiki ko raino ba, ni na gaji haka kuma bana so El'mustapha,
Ni fa wadda xan dauko Nanny ce, ibrahim naji yana magana xai daukowa matarsa shine nima n..... ta katse sa,
Oh God El'mustapha, nanny xaka dauko min ta xauna dani a cikin gida, in maka kwalliya na fito ita kuma ta saka mini skirt ko matsatsen wando ta fito xuwa raino, kai kuma kana kallonta ko?
Yace sharri kuma xaki min jiddah, idan ba kyaso ne kice ba kyaso amma banda sharri kin sanni bani da kallon mata ballantana ma qabila, me xanyi da ita jiddah.
Ta xauna tana fadin to bana so, I can take care of my daughter, in kuma ka matsa dole naji a dauko tsohuwa irin Inna wacce ko haqoran gaba babu a bakinta sai yawun goro na amince,
Ya saki dariya yana xama kusa da ita,
Oh ni El'mustapha duk yanda nayi da jiddah ban mata dai dai ba, nikam na rasa inda jiddah ta dauko wannan halin a yanxu.
Ta tabe baki batare da tayi magana ba.
*
'Abba ni ka saka baki kayiwa jiddah magana ina son el'mustapha ta barni na aure sa dan Allah abba,
Hajiya ta xare idanu tana kallonta,
Anya uwani na da hankali kuwa, kin san me kika fada?
'Abba yace bata da hankali kam, ai na gayamaki har aiki aka mata amma babu canji sai ma nake ganin abin a jinin ta yake ba wani faduwa da xaa fake da ita, an dai ci kudi na ne amma uwani kam sai addua.
Uwani tace Allah abba na shiryu nayi nadama kowa ma ya sanni, waccan karon ba laifina bane, laifin jamcy ne bani da niyar cutar da jiddah itace ta xugani, dan Allah ku taimakeni kada a nuna min baqin ciki a maidani dakina yau.
Hajiya tace sam bada yawu na ba wallahi, babu ruwana kuma idan aka dage da lallai sai uwani ta koma dakin ta baa min adalci ba ta tashi ta fice a fusacce,
Uwani ta bita da kallo kafin ta dubi abba, ita dai hajiya har yanxu abba bata daina nuna min baqin c.... bai bari ta qarasa ba ya bige mata baki,
Kul na qara jin wannan kalmar a bakin ki, ba mahaifiyar ki bace, meyasa ba kya tunani kafin ki furta magana, ki fa yi a hankali da duniya uwani, ki dawo cikin hayyacinki kisan me kike yi, Allah baya barin mai xalunci da kuma mai sabawa iyaye, kar na qara jin haka daga bakin ki.
Tau abba kayi haquri na daina, xanje ma na bata haquri.
Yace maganar el'mustapha wannan karon ma xan gaya maki babu yawuna babu hannuwana aciki kamar farko, kuma bani buri ko fatan naga el'mustapha ya aure ki domin baki cancanta ba, kince naxo dake ne domin kiga jiddah ki roqeta gafara ba wai ki roqeta ta maidaki dakin ki ba, ni babu ruwana duk abinda suka maki ke kika ja tashi kibani guri shashasha.
Ta tashi tana tunxure baki ta fice, tunda baxasu maidata dakin ta ba ita xata maida kanta, a bata key din dakin ta shiga daga yau ta xama matar el'mustapha ta maida kanta dakinta duk mai baqin ciki sai dai ya mutu amma sai ta haihu da el'mustapha.
*
'Washe garin ranar duk basu hadu da jiddah ba sai bayan jiddah ta fito raka el'mustapha xai je gurin aiki suka tsinkayo uwani tsaye a gurin motar sa, taci kwalliya abinta tana jiran fitowarsa.
Suka qarasa jiddah na kallonta,
'Anty jiddah an tashi lfy, yaya barka da fitowa cewar uwani dauke da murmushi a fuskarta,
Duk ba wanda ya amsa a cikinsu,
'Dan Allah kuyi haquri nidai a maidani dakina, a bani key xanje na gyara dakina, wannan karon bani...... tayi shiru sakamakon bugu da taji a tsakiyar kanta, ji kake tum.... ashe jiddah ce ta rarumo wani katon dutse ta buga mata aka...
Uwani ta xube gurin a sume, el'mustapha ya juyo yana kallon jiddah cikin mamaki, xai yi magana tayi saurin tsaida sa,
Kar kace komai, yar uwarka ko tawa, ba ruwan ka she is my sister, shiga mota kayi tafiyar ka.
Yanda idanunta suka juye abin ya bashi tsoro, innalillahi wai meke damun jiddah,
Ya xagayo da sauri yana fadin na tafi ina jiddah, idan kika kashe.....
Nace ba ruwanka el'mustapha,
Ya ja dogon tsaki hankalinsa ya tashi sosai ganin jini na fita ta goshin uwani, kada jiddah tayi kissan kai, yanxu fisabilillah idan iyayenta suka ganta haka ya xasu ji, ya kalli jiddah cikin takaici sai huci take, tsaki ya ja kafin ya bude motarsa tana kallo ya saka uwani a mota xai fita da ita.
Da gudu ta qarasa bakin gate ba inda xai fita da uwani, securities suka taso amma bata damu ba, ta tare hanya sai idan xai taka ta ne ya wuce,
Ko jiddah ta haukace ne, ya tambaya cikin xuciyarsa yana kallonta ta glass din motar, ya fito a fusacce,
Xaki matsa ne ko sai naxo na taka ki,
Wallahi baxaka kai uwani asibiti ba, sai dai ka takani ka wuce.
'Wannan wane irin abin kunya ne jiddah ke janyo masa cikin yaransa,
Yayi ma wani sergeant magana akan yaxo ya kai uwani asibiti, ta matsa tana sauke numfashi suna fita abba ya fito jin hayaniya.
Ni jiddah ni xaki wulaqanta,
Nima ka gama wulaqantani na daukar uwani ka saka a mota kowa yana kallon ka.
Yace tor shikenan, ya juya a fusacce ya nufi cikin gida bai jima ba ya fito dauke da wani key na mota, bai qara bi ta kanta ba ya fice, ta tabe bakinta kawai.
'Dan Allah anti jiddah ki yafe min, nasan kin tsane ni a ynxu amma kiyi haquri ki bani dama ta biyu na xauna dake baxaki taba dana sani ba, ki aura min El'mustapha a karo na biyu wallahi ina son.... bata qara sa ba jiddah ta dauke ta da Mari, kafin tayi wani yunquri ta sake wanke fuskarta da Mari hade da hankadata ta fadi ragwaf.
Ko yawo xakiyi tsirara a duniyar nan kina bin bokaye, ko ciwo xakiyi kina aman jini kina mutuwa kina tashi baxaki taba auren *EL'MUSTAPHA* ba kuma kiyi gaggawar barin gidan nan kafin na fito nasa a wulaqantaki a gidannan.
*EL'MUSTAPHA*
*Haske Writers Association*
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
_God bless this special best friend of mine with all happiness and accomplishment in life, I’m truly blessed to have you as my best est buddy *khadija Ahmed KDEEY*_ 🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂
_Happy Birthday to my best daughter, Thinking of you with love on your birthday and wishing you everything that brings you happiness today and always, I’m truly blessed to have you as my best est buddy *Sumayya Halliru Dikko*_🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂
56
Uwani ta xube gurin hankalinta a tashe,
Me jiddah ke nufi da ko xata mutu baxata taba aura mata el'mustapha ba, kenan jiddah tana nufin ko ma me xatayi sai dai tayi amma baxata qara auren mijinta ba.
Yaushe jiddah ta canxa haka? Waye ya bata mana jiddah ta xama mai xafi haka, da alama yanxu bata ma da haquri qila idan an bincika ko tausayi bata da shi, waye ya bata min yar'uwa haka? Indai ba ta sami qawa mai xugata irin jamcy ba.
Taja dogon tsaki kafin ta nufi dakin su hajiya dan ta lura hajiya ma na mata wani gani gani tana so ta tambaya dalili idan itama tana baqin ciki da dawowarta gidan uban tane ta sani, ko tana baqin ciki da xata dawo gidan mijinta ne oho.
Jiddah ta ajiye airah akan bed tana kallon el'mustapha,
Wani abin mamaki, Uwani ke roqona na barta ta auri mijina a karo na biyu, bata neman gafara ta sai ma ta mijina take.
El'mustapha ya matsa kadan inda ta shimfide Airah barci take, ya tsurawa fuskarta ido yana kallonta,
Yace ai nasan jiddah mai haquri ce da tausayi, ina tunani ma yanxu tausayin ne ya saka taxo ta gayamin uwani na son komawa dakin mijinta, nasan yanxu xaki fara kuka kina roqona na maida uwani yar uwar kice ciwon xuciya zaya kamata ke kuma baki so ki rasata saboda halaccin iyayenta.
Ta xauna da murmushi a fuskarta wanda bai kai ciki ba, batayi magana ba illah fadawa da tayi kogin tunani, banan da uwani sune matsalar ta a yanxu kuma tana roqon Allah ya taimake ta ya raba ta dasu lafia.
El'mustapha ya daqo yana kallonta,
Tunanin me jiddatulmusty take yi?
Tace ba komai,
Ya tashi ya cire doguwar jallabiyar dake jikinsa, kafin ya qara kallonta,
Ina so na dauko wata mai aiki saboda Airah ke kuma kiji dani,
Ta ware idanu tana kallonsa,
What? Mai aiki, wace irin mai aiki kuma el'mustapha? Kai baka ga halin da nake ciki bane, Dame xanji ni kuma me xanyi da mai aiki.
Ban fahimce ki ba jiddah, wane hali kike ciki wanda ni ban sani ba, menene laifin mai rainon da xan dauko?
Ta tashi tana bata fuskarta tana fadin babu amma ba yar iskar da xata qara xuwa gidannan da sunan aiki ana fakewa akan mijina, kowace mace ta taso mijina, dame el'mustapha yafi sauran maxan ne, why only you?
Sai yanxu el'mustapha ya fahimci inda ta dosa, ya tsura mata ido dubi yanda ta birkice masa daga magana, sam jiddah ta canxa sosai, amma shi baiga laifi anan ba saboda ya dauko mai rainon airah shi me xaiyi da matan ne.
Yace jiddah menene dan na dauko mai tayaki rainon airah, qaramar yarinya ce fa..... ta katse sa,
Qananan yaran ne kemin raino nima ina rainon su da sun girma basu da abin so sai mijina, ni xan iya rainon airah saboda ba abinda nake yi a gidannan sai girkinka da kula da sashen ka, idan ka matsa dole sai an dauko mai raino na amince amma fa namiji xaka dauko yayi rainon airah.
Ya bude idanunsa sosai yana kallonta bayan ya gyara tsayuwarsa,
Namiji jiddah? Wane irin namiji xan dauko yayi min rainon ya'mace? Me ma xai kawo namiji har cikin gidana da falona yana kallon matata.....
Tace nima babu macen da xaa dauko taxo tana kalle min miji, ban nemi xama da mai aiki ko raino ba, ni na gaji haka kuma bana so El'mustapha,
Ni fa wadda xan dauko Nanny ce, ibrahim naji yana magana xai daukowa matarsa shine nima n..... ta katse sa,
Oh God El'mustapha, nanny xaka dauko min ta xauna dani a cikin gida, in maka kwalliya na fito ita kuma ta saka mini skirt ko matsatsen wando ta fito xuwa raino, kai kuma kana kallonta ko?
Yace sharri kuma xaki min jiddah, idan ba kyaso ne kice ba kyaso amma banda sharri kin sanni bani da kallon mata ballantana ma qabila, me xanyi da ita jiddah.
Ta xauna tana fadin to bana so, I can take care of my daughter, in kuma ka matsa dole naji a dauko tsohuwa irin Inna wacce ko haqoran gaba babu a bakinta sai yawun goro na amince,
Ya saki dariya yana xama kusa da ita,
Oh ni El'mustapha duk yanda nayi da jiddah ban mata dai dai ba, nikam na rasa inda jiddah ta dauko wannan halin a yanxu.
Ta tabe baki batare da tayi magana ba.
*
'Abba ni ka saka baki kayiwa jiddah magana ina son el'mustapha ta barni na aure sa dan Allah abba,
Hajiya ta xare idanu tana kallonta,
Anya uwani na da hankali kuwa, kin san me kika fada?
'Abba yace bata da hankali kam, ai na gayamaki har aiki aka mata amma babu canji sai ma nake ganin abin a jinin ta yake ba wani faduwa da xaa fake da ita, an dai ci kudi na ne amma uwani kam sai addua.
Uwani tace Allah abba na shiryu nayi nadama kowa ma ya sanni, waccan karon ba laifina bane, laifin jamcy ne bani da niyar cutar da jiddah itace ta xugani, dan Allah ku taimakeni kada a nuna min baqin ciki a maidani dakina yau.
Hajiya tace sam bada yawu na ba wallahi, babu ruwana kuma idan aka dage da lallai sai uwani ta koma dakin ta baa min adalci ba ta tashi ta fice a fusacce,
Uwani ta bita da kallo kafin ta dubi abba, ita dai hajiya har yanxu abba bata daina nuna min baqin c.... bai bari ta qarasa ba ya bige mata baki,
Kul na qara jin wannan kalmar a bakin ki, ba mahaifiyar ki bace, meyasa ba kya tunani kafin ki furta magana, ki fa yi a hankali da duniya uwani, ki dawo cikin hayyacinki kisan me kike yi, Allah baya barin mai xalunci da kuma mai sabawa iyaye, kar na qara jin haka daga bakin ki.
Tau abba kayi haquri na daina, xanje ma na bata haquri.
Yace maganar el'mustapha wannan karon ma xan gaya maki babu yawuna babu hannuwana aciki kamar farko, kuma bani buri ko fatan naga el'mustapha ya aure ki domin baki cancanta ba, kince naxo dake ne domin kiga jiddah ki roqeta gafara ba wai ki roqeta ta maidaki dakin ki ba, ni babu ruwana duk abinda suka maki ke kika ja tashi kibani guri shashasha.
Ta tashi tana tunxure baki ta fice, tunda baxasu maidata dakin ta ba ita xata maida kanta, a bata key din dakin ta shiga daga yau ta xama matar el'mustapha ta maida kanta dakinta duk mai baqin ciki sai dai ya mutu amma sai ta haihu da el'mustapha.
*
'Washe garin ranar duk basu hadu da jiddah ba sai bayan jiddah ta fito raka el'mustapha xai je gurin aiki suka tsinkayo uwani tsaye a gurin motar sa, taci kwalliya abinta tana jiran fitowarsa.
Suka qarasa jiddah na kallonta,
'Anty jiddah an tashi lfy, yaya barka da fitowa cewar uwani dauke da murmushi a fuskarta,
Duk ba wanda ya amsa a cikinsu,
'Dan Allah kuyi haquri nidai a maidani dakina, a bani key xanje na gyara dakina, wannan karon bani...... tayi shiru sakamakon bugu da taji a tsakiyar kanta, ji kake tum.... ashe jiddah ce ta rarumo wani katon dutse ta buga mata aka...
Uwani ta xube gurin a sume, el'mustapha ya juyo yana kallon jiddah cikin mamaki, xai yi magana tayi saurin tsaida sa,
Kar kace komai, yar uwarka ko tawa, ba ruwan ka she is my sister, shiga mota kayi tafiyar ka.
Yanda idanunta suka juye abin ya bashi tsoro, innalillahi wai meke damun jiddah,
Ya xagayo da sauri yana fadin na tafi ina jiddah, idan kika kashe.....
Nace ba ruwanka el'mustapha,
Ya ja dogon tsaki hankalinsa ya tashi sosai ganin jini na fita ta goshin uwani, kada jiddah tayi kissan kai, yanxu fisabilillah idan iyayenta suka ganta haka ya xasu ji, ya kalli jiddah cikin takaici sai huci take, tsaki ya ja kafin ya bude motarsa tana kallo ya saka uwani a mota xai fita da ita.
Da gudu ta qarasa bakin gate ba inda xai fita da uwani, securities suka taso amma bata damu ba, ta tare hanya sai idan xai taka ta ne ya wuce,
Ko jiddah ta haukace ne, ya tambaya cikin xuciyarsa yana kallonta ta glass din motar, ya fito a fusacce,
Xaki matsa ne ko sai naxo na taka ki,
Wallahi baxaka kai uwani asibiti ba, sai dai ka takani ka wuce.
'Wannan wane irin abin kunya ne jiddah ke janyo masa cikin yaransa,
Yayi ma wani sergeant magana akan yaxo ya kai uwani asibiti, ta matsa tana sauke numfashi suna fita abba ya fito jin hayaniya.
Ni jiddah ni xaki wulaqanta,
Nima ka gama wulaqantani na daukar uwani ka saka a mota kowa yana kallon ka.
Yace tor shikenan, ya juya a fusacce ya nufi cikin gida bai jima ba ya fito dauke da wani key na mota, bai qara bi ta kanta ba ya fice, ta tabe bakinta kawai.