← Book details El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 80

Sashe 25

El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Aa bama sai kaxo ba uwani ta fada cikin rudu, ta karbi number tasa har xata juya ya kirata.

Ke mekike nufi inxo gurin ki baxaki bani ko sisi ba, kinma rainamin wayo.

Dubu biyu ne kawai a hannuna yanxu ta fada a tsorace,

Bani sunan, ya karba ya saka aljihunsa, ya tayar da bike din sa ya fice kamar xai bankade ta, uwani ta sauke numfashi tana mamakin wannan kurma da alama kam yana shaye shaye ita kam tsoronsa take.

*

Bayan kwana biyu jiddah na falo ita kadai xaune, t.v take kallo sanda uwani ta shigo falon.

Kallonta tayi a wulaqance tana yatsina fuska, ta xauna tana fadin.

Sai kaga mutum a fuska kamar na kirki a xuciyarsa kuwa kamar na fir'auna, mutum yasan Allah yake kwace miji ana shiga haqqin baiwar Allah da bataji ba bata gani.

Kallonta kawai jiddah tayi, ta dauke kanta gefe tana murmushi.

Anci amanata, ansa an dakeni, ansa miji baya xuwa gurina, ba ruwanshi dani, anyi min wayo an bani mota da Sana'a dan kawai na bar miji a mallakeshi, Allah xai sakamin dan baxan yafe ba.

Nan ma jiddah bata tanka ba, sai Ma qoqarin tashi take ta bar mata falon, uwani Ma ta tashi tana fadin,

Iyayena sun riqi mutum amana amma su anqi a riqa masu amana, iyayena sunyi qoqari su ba mutum tarbiyar dama uwar mutum baxata iya bayarwa b...... bata qarasa ba taji saukar Mari a kuncinta, kafin tayi wani yunquri jiddah ta qara dauke ta da wani Mari, xatayi magana ta qara dauke ta da wani Mari, uwani ta gigice ta fara ihu dafe da kuncinta.

Xan dauki kowane irin iskanci naki amma banda na iyayena, nasan darajar su da qimarsu ke baki isa ki xagi iyayena na barki ba, yanxu Ma darajar cikin nan kika ci da sai kin yabawa aya zaqin ta, daqiqiya kawai, ta fice ranta a matuqar bace.

Wlhy Allah xai sakamin kuma baxan yafe ba sai na dauki mataki, ke ki dake ni mijinki ya dake ni, ai ni ba boya bace, kinci darajar wannan cikin da sai nayi qasa qasa da namanki a gidannan, sai na ji maki ciwo na fasa maki baki, ai ba qarya nayi ba iyaye na ne suka miki tarbiya, idan kin cika ki qara fitowa kice xaki dake ni k...... tayi shiru ganin jiddah ta fito, tana nufo ta, ta yunqura da gudu ta shige dakin ta hade da saka key, still uwani batayi shiru,

Ai ba tsoron ki nake ji tausayamaki nake saboda cikin jikinki, da sai na farfasa maki baki yau, sai na jimaki ciwo kin kwanta a asibiti, insa likita ya cire min wannan baqar xuciyar taki, kuma Allah xai sakamin.

Ta sauke numfashi, ta nufi mirror tana kallon fuskarta har tayi wani kumburi, taja dogon tsaki tana shafa fuska, akwai lokacin da xai xo nima xan rama inda baki da ikon dukana, ashe jiddah xata iya duka kenan, tana nufin kyaleni ne takeyi karma ta qara ragamin nima xan dage damtse infara dukanta ne, harda wani kirana daqiqiya har yanxu tana jin haushi saboda naqi karatu to baxanyi ba sai dai ki mutu, sum sum da ita kamar kifin ruwa mtsewwwww.

A ranar jiddah tana cikin bacin rai sosai, shi kansa el'mustapha yaga hakan,

Ko dai jikin ne jiddah?ta dauke kanta gefe batare da tayi magana ba, ya xauna yana kallonta cikin seriousness,

Talk to me jiddah, what's wrong?

Ba komai ta fada a hankali tana kallon,

Akwai komai, from your face nagani, indai ba nine akace nayi wani abin ba,

Idan kaine wannan xaman da kayi a gabana xan rufe ka da duka ne,

Dana ji dadi jiddana ta bige ni, nasan nayi mata laifi ne ta hukuntani da hakan.

Shiru batayi magana ba, babu walwala a fuskarta,

Idan bani bane waye, please tell me...

Uwani ce ta bashi amsa kamar xatayi kuka,

Me uwani tayi?

Iskancin ya tashi kaina ya koma kan iyayena da basu a duniyar ma, I can't take it anymore el'mustapha,

Yaja numfashi yana kallonta, uwani.. Uwani... Uwani... Am tired of her jiddah duk laifin kine, meyasa tunda uwani ke maki rashin mutunci baki daukar mataki, yanxu ta bata maki rai kinxo kin xauna kina fushi kina kuka an you know your condition meke nan,

Tana min gorin iyayenta sun min tarbiya, ita meyasa batayi amfani da tarbiyar da suka mata ba, ta tashi tana fadin idan ban daki uwani ba baxan sami nutsuwa a xuciyata ba.

El'mustapha ya sha gabanta da sauri,

Calm down jiddah, idan kika ce kiyi fada da uwani da wannan cikin ai xata ji maki ciwo, idan taci riba akan ki gobe kome xai hadaku qoqarin fada xatayi dake, respect yourself, tun a lokacin da tayi maki iskanci ya kamata ki dauki hukunci akai.

'Na mare ta sau uku, amma xuciyata batayi sanyi ba, ina jin haushin uwani a yau, I can do anything for her idan bata kiyayeni ba ko.....

'Ashe haka jiddana keda xafin xuciya I don't know, yau uwanin da ake tausayi ce aka Mara har sau uku, how I wish ina gurin ne na ganewa idanuna jiddah ta dauki hukunci da hannunta, ya riqota suka xauna.

Haqurin da kike bani akan uwani nima shi xan baki, wata uku ne xata bar miki miji harda gidan Ma, xata koma gidan iyayenta ta cigaba da xama dama saboda karatu take xaune a gidan kuma ta ajiye batayi kinga sai ta tattara komai nata ta bar mana gida.

'Naji kamar wata uku yaxo gobe, dana sani ban hada wannan auren ba, har yau na kasa gano inda uwani ta dosa akaina.

Is better ki gano jiddah ina so naji kin furta da bakinki uwani taci amanar ki, uwani bata sonki.

Tayi shiru kawai batare da tayi magana ba.

*

Tun daga lokacin suka soma wasan buya, uwani ko kadan bata so taga jiddah ko abinda xai hada ta da jiddah cos a tsorace take da ita tun lokacin da taga fushin jiddah, ashe haka jiddah take, shiru shiru kamar baxatayi fada ba ballantana ta kai ga duka.

Sai plan suke hadawa ita da kurma yanda xasu bullowa su sace jiddah.

Islam ke son banan, yasmeen ta fada tana kallon jiddah, tun ranar da kika aiko ta gidana ya ganta yake min maganarta.

Jiddah ta bayyana farin cikinta tana kallon yasmeen,

Kice banan tayi sa'a, amma yasan wacece banan din kuwa, bana son abinda xai xo ya cutar da yarinyar, marainiya ce bata da kowa a duniyar ni sai ni da kakarta, rayuwar Islam daban ce da banan, she is not dat wise irin yanda Islam ke so you know it, last month ta gama skul.

Tun da Islam yace yana son ta nasan da gaskiya yakeyi yana son ya, kuma kinga shine ya ganta yace yana so har ya matsamin lallai sai naxo na sanar dake, banan tana da kyau kuma yarinyace kamar shi so banga rashin dacewar su anan ba, sai idan kece ba kyaso jiddah.

Lol, saboda me xance baxan so dan'uwanki ba, kinsan yaran yanxu baa masu dole, kuma banda tabbacin tana da wanda take so ko kuma babu, xan tuntube ta yasmeen ki kwantar da hankalin ki insha Allah xata auri Islam nima ina mata sha'awa dashi.

Murmushi yasmeen tayi, ta kawar da xancen tana fadin jiya baban baby ya dawo daga dubai, ya kawo min kaya masu kyau na jaririrai.

Xan gayawa el'mustapha idan ya dawo, sai ki aiko da kayan ya gani duk da ya gama siyayyar kayan haihuwa tuntuni amma nasan idan sun masa kyau xai siye.

Insha Allah xan aiko, wannan cikin naki wai wata nawa ne?

Bakwai ne fa kin ganshi da girma barakallah.

Wlhy kuwa kuma girman ya taso lokaci daya, before ma baa gane kina da ciki, qila wasu biyun ne xasu xo again.

Murmushi kawai jiddah tayi tana fadin Allah dai ya raba lafiya.

Amin cewar yasmeen tana qoqarin barin gidan.

Kinji Islam ke son ki banan, am happy for you, yaron yana da kirki sosai.

Banan ta bata fuska tana kallon jiddah,

Waye shi anti jiddah ni ban san shi ba.

Qanin qawata ne yasmeen, sanda kika je gidan ya ganki yana so, nikam nace xan bashi banan saboda na yarda dashi nasan baxai cutar dake ba.

Banan ta dafe kanta, sai yanxu ta tuna shi, shine Ma ya maidota gida, tayi shiru batayi magana ba, ita dake son el'mustapha ya xatayi da Islam, wai samun guri inji wata xuciyar, masu aiki nawa ne suka sami irin gatan da ta samu saboda jin dadi xatace xata auri mai gidan, baxata iyama anti jiddah hakan ba.

Taji muryar jiddah na magana, idan kuma kinada wanda kike so ne to, baxan maki dole ba, duk wanda kike so dashi xaa yi, buri na ki auri wanda xai riqe ki amana kuma yasan darajar ki, kada ki biyewa xuciyarki ga samarinnan na yanxu masu qaryar banxa ki xauna kina ta jiran warabuka dan baki da tabbacin xasu fito neman auren ki ko baxasu fito ba, nidai baxan cutar dake ba ko na kaiki inda xaa cutar dake kinsani, kije kiyi tunani akai.

Ta sunkuyar da kanta feeling guilty idanunta suka ciko da hawaye,

Shikenan ta rasa el'mustapha har abada, mutumin da bai san tana yi ba, ita kadai ke haukanta kuma tasan baxai aure ta ba, koma xai aure ta baxata iya xaman kishi da jiddah ba, jiddah ta xama tamkar uwa agare ta yanxu dole kuma xata haqura da el'mustapha ta yaqi xuciyarta na ganin ta cire sonsa.

Ta yarda ta rasa el'mustapha har abada, xata cigaba da rayuwa babu el'mustapha sai xabin Allah, yeah tafi kowa sanin jiddah baxata cutar da rayuwarta ba,

Da gaske kenan da jiddah tace ta kama mai son ta wato Islam domin shi kadai ne yanxu wanda ke son ta, ta rabu da jiran tsammanin wato el'mustapha saboda shine baisan tanayi ba,  dan haka ta rungumi mijin da duk Allah ya rubuta mata da hannu bibbiyu Kuma xatayi biyayya ga jiddah dan cimma rayuwa mai amfani a duniya da lahira.

Ta amince ta yarda Islam shine xabin Allah, ta soma siffantoshi a idanuwanta....

Tunanin me kike banan? Jiddah ta katse ta.
Chapter 25 · 0% Book details