← Book details El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 50 OF 80

Sashe 50

El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

'Har kin manta kenan, bayan kin bar yarinya sai kuka take tana son jin dumin mahaifiyarta.

'karbo min ita na ganta....

'ba yanxu ba kiji dani tukunna, nafi ta buqatar ki jiddah.

Taja hancinsa tana murmushi,

Yanda kace haka xaa yi mijin jiddah,

Yace yauwa jiddatulmusty, sai kuma yayi murmushi ya tashi yana fadin bari na karbota jiddah nasan kinfi buqatar ta dani a yanxu.

Ta bisa da kallo tana murmushi....

EL'MUSTAPHA

Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers

Fertymerh Xarah💞

52

Bayan kwana biyu, jiddah ta warware sosai sai dai rashin kuxarin jiki,

'Anty ikram Ma sunxo tare da wani kawun jiddah.

Sosai dr merah ke kula da jiddah musamman qafarta, sun xama friends da el'mustapha ko da yaushe suna tare a office, har yake baiwa el'mustapha labarin sa da Afiya.

Hajiya bani ruwan tea na sha, cewar jiddah tana kallon ta,

Hajiya ta tashi goye da jaririyar ta hada mata bayan ta xauna kusa da ita,

Magana xamu yi jiddah ta fahimta, bana so naga abinda xai cutar dake ko kadan.

Jiddah ta tattara hankalinta da nutsuwar ta tana kallonta,

Hajiya tace meke tsakanin wannan yar aikin taki da mijinki?

Jiddah ta qara kallonta cikin faduwar gaba tana bude idanuwanta, ta ajiye Cup din tea tana fadin, me kika gani hajiya?

Tambayar ki nake yi kibani amsa,

Cikin rawar murya  jiddah tace nima ban sani ba hajiya,

Ba ina gayamaki bane dan ki tada hankali ki, amma kisani wannan karon ko mutuwa xakiyi baxan taba yarda ki aurawa wata mijinki ba, tun da na lura ke Sam baki san ciwon kanki ba sai haquri, ina ji ranar da xaa shiga dake aiki har kina bata amanar ya'yan ki da mijinki, meke damun kine jiddah.

Jiddah tace hajiya banan tana da kirki bana xaton xata cutar dani ko wani nawa shine dalilina na bata amanar yarana, amma maganar el'mustapha cikin xafin ciwo ne ban san na nata amanar sa ba kuma ba wai ina nufin ta so shi ba hajiya.

Koma dai menene na riga na gano banan tana son mijinki, kuma kinji na gayamaki wannan karon baki isa ba, kuka taso da uwani tun kuna yara ta cutar dake ballantana wata bare,

Jiddah taja numfashi a ranta tana cewa hajiya baxata gane ba wani bare yafi dan uwa kuma ba duka aka taru aka xama daya ba.

Amma hajiya meyasa kika ce tana son el'mustapha, ni na dauka shine kadai ke son ta.

Hajiya ta xare ido cikin mamaki, tace kina nufin wai el'mustapha yana son banan? Ya akayi kika yi wannan saken jiddah, taya xaki reni yarinya da hannunki ta aure maki miji, wai ke meke damun ki ne, wace irin mutum ce ke, ban taba sanin wata mace mai hali irin naki ba jiddah, kin fiye tausayi da sanyin xuciya wanda shine ke cutar dake kuma shine ya kawo ki matsayin da kike a yanxu.

Jiddah ta soma kuka tana fadin, ba laifina bane hajiya, bansan yaushe ya fara son ta ba, nagano hakan bayan dawowa ta daga batan da nayi kuma el'mustapha ya rantse min babu soyayyarta a xuciyarsa sai dai ban sani ba akan ita banan.

Hajiya tace to bari kiji ban san komai akan gidan ki ba amma a waya da naji banan nayi na fahimci komai, kin bata auren qanin aminiyar ki, tana waya naji tana bashi haquri akwai wanda take so tuntuni kuma yanxu tana da tabbacin xata same shi amma ya rufa mata asiri kada ya gayamaki dan bata son fushin ki ko kadan.

Bansan me yace da ita ba naji tana roqonsa da magiya cewa xai iya haqura da ita har ya sami wacce ta fita.

Ban taba kawo el'mustapha take so ba sai a jiya da dare, ta kwana kiran el'mustapha a barcinta wataqila ma yusrah ta ji ta ban sani ba, yau da safe ban mata mgn ba amma daga irin kallon da take wa el'mustapha daban ne da wanda take mana, na lura duk inda yayi idanunta na kansa bai Ma san tana yi ba.

Jiddah ta dafe kanta, innalillahi ta fada a hankali, sai ga hawaye, ta dubi hajiya cikin kuka,

Meyasa suke son el'mustapha, meyasa suke son mijina, menayi masu suke son raba ni dashi?

Taya xanyi na sani jiddah, bansan mu'amalar ki dasu da shi a gida ba, uwani bata bani mamaki ba kamar banan saboda uwani tun kafin ki auri el'mustapha ta furta tana son sa, amma banan taya xata so mijinki bayan kece kika riqeta kuma yar aikin ki, ya akayi ta sami kusanci haka da el'mustapha, kina sakaci da gidanki da mijinki jiddah, samun miji a wannan xamanin kamar el'mustapha sai an tona, bako wane namiji xai iya maki halacci irin wanda el'mustapha yayi maki ba, ki so shi da xuciya daya kuma ki rungumeshi da hannu biyu ban isa na hana mashi qara aure ba amma kam ba banan ba na gayamaki gsky tun yanxu, idan uwani ta maki ciwon qarya ta ci galaba akan ki wannan karon ko ciwon mutuwa banan xatayi a gabanki baxata taba auren el'mustapha ba.

Ta tashi a fusacce xata fice, jiddah tayi saurin tsaidata

Hajiya laifina kike gani, Wlhy ko a mafarki baxan bar el'mustapha ya auri banan ba ballantana a xahiri, idan banan tace tana son el'mustapha taci amanar yarda da ita da nayi, na bata amanar ya'ya na bawai ina nufin ta auri el'mustapha ba, ko da nace mata el'mustapha ko Islam Allah kadai yasan mijin auren ta saboda a lokacin inajin kamar baxan rayu ba amma ban taba kawo banan xata so mijina ba, hajiya ya xanyi ba banan ba ni bana son kowace mace ta kusanci el'mustapha koda da murmushi ne.

Hajiya tace kisha tea din tukunna har ki sami lafia xamuyi maganar,

'Na kasa sha hajiya, hankalina ya tashi yanxu ina banan din da el'mustapha..... Bata rufe bakinta ba el'mustapha ya shigo, bayansa banan ce da anty ikram.

Ta xare idanu tana kallonsu cikin faduwar gaba, el'mustapha kuwa kallon hajiya yayi yana kallon jiddah cikin mamakin kukan me jiddah keyi.

Kafin yayi magana anti ikram ta xauna tana fadin,

Jiddah xuwa gobe da safe xamu koma tare da yusrah da yayan ki, tun da jiki alhamdulillah kin sami sauqi sai fatan Allah ya tada ki lfy.

Abinda ya fito bakin jiddah ya bawa kowa mamaki ba ma kamar banan.

Tace anti ikram idan xaki koma kuje da banan, hajiya xata kula dani.

'Anty jiddah me..... Wani kallo da jiddah tayi mata ya saka ta rufe bakin ta ba shiri abinda bata taba yi mata ba, kada dai jiddah ta gano tana son mijinta da ta shiga uku.

Hajiya tace aa jiddah baxaa yi haka ba, kibar banan ta.... ta katse ta,

Banan xatabi su anty ikram Nigeria, umarni ne ba shawara ba.

El'mustapha na tsaye baice komai ba sai kallon jiddah yake yanda ta sauya lokaci daya,

'Anty ikram tace banan tayi maki wani laifine jiddah? Duk suka xuba mata ido,

Tace aa ta koma saboda su twins, bama haka ba ta dai koma hajiya is ok.

Banan taji kamar ta rusa ihu a gurin, har wani xufa take, meyasa jiddah xatayi mata haka na nisanta ta da el'mustapha, karo na farko da ta soma jin haushin jiddah a xuciyarta tun xaman su.

Hajiya bata qara magana ba ta juya ta fita, ikram Ma fita tayi tana amsa waya,

Banan ta dubi el'mustapha dai dai lokacin shima ya dago yana kallonta,  jiddah na kallonsu, bugun xuciyarta ya tsananta,

El'mustapha ya xauna baiyi magana ba amma yana son sanin dalilin jiddah na cewa banan ta koma bayan tana qoqari sosai akan ta.

'Anty jiddah idan laifi nayi d...... ta katse ta a fusacce,

Get out pls kuma kisani ko kinqi ko kin so Islam ne mijinki idan har baxaki aure shi kafin nadawo kibarmin gidana.

Banan ta soma kuka a rikice, ni anty jiddah yaushe nace bana son sa wlhy qarya yake min idan shine ya gayamaki hakan, dan Allah kiyi haquri kada ki maidani, ina son xama dake bani da xabi sai naki ki yarda dani.

Jiddah tace na riga na gama magana kije kawai, idan kina ganin auren ki da Islam na cutar dake ne Allah ya na gani, kuma wanda kike so a yanxu baxaki taba samun sa ba gwanda ki rungumi Islam shine kyautar da Allah yayi maki ko banxa Islam ba ajinki bane kima godewa Allah.

Banan bata qara magana ba, amma kalaman jiddah na nuni da kamar ta gano tana son El'mustapha, idan kuwa hakane dole ta nisanta kanta da jiddah kamar yanda ta buqata harta sauko, ta fita da sauri tana kuka.

Shikam el'mustapha na xaune baice komai ba amma ya rasa wannan xafin da jiddah ta dauka akan banan, yayi shiru,

Dole xakayi shiru ka shiga damuwa saboda na Kore abinda kake so, na riga na gama fahimtar ku, kuna munafuntata a bayan idona..... Shut up jiddah, ya katse ta cikin tsawa,

Ok... Ok saboda wannan dalilin you are sending banan away from you right? Duk qoqarin yarinyar nan akan ki, meyasa kike tunanin abinda baxai taba yiwuwa ba, idan saboda wannan ne banan baxata bar garin nan ba, you are talking rubbish babu wata soyayya tsakanina da yarinyar nan.

Ta tsura masa ido cikin mamaki baki a sake,

Tace yanxu na gane hasashena ya xama gsky, tabbas ka nuna min kana son banan, ka damu da banan, idan hakane baka min adalci ba el'mustapha..... Sai ta fashe da kuka,

Ya tsura mata ido cikin mamaki ga wani haushi da yake ji a xuciyarsa, yana ji tuntuni sun gama magana da ita akan babu soyayya tsakanin sa da banan amma me ya dawo da maganar? Dan ya qara kufular da ita yace,

Eh naji, koma menene haka ne, kuma aure kece kika buda min hanyar yin sa, banan din Ma amanata kika bata so banga abinda xai saka ki tada hankalin ki ba, idan Allah ya nufa xan aure ta auren ta xanyi.....

Wallahi baka isa ba, ta fada tana kallonsa da jajjayen idanuwanta, kuma banan sai ta bar garin nan gobe ko ni na barshi, sai ku xauna tare.

Oho dai koma menene ke kika sani, ya tabe bakin sa alamar ko a jikinsa,
Chapter 50 · 0% Book details