Sashe 28
El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mama Ma baa barta baya ba, batan jiddah ya taba xuciyarta har ciwon ta ya dawo saboda damuwa, gwanda ace mutum ya mutu da ace ya bata baa san halin da yake ciki ba.
Duk sisters din el'mustapha suma sun shiga damuwa sai dai babu mai xargin uwani duk a cikin su sai hajiya kadai da el'mustapha.
Yanda uwani ta dage tana kuka tana neman jiddah ya saka sauran mutane basa xarginta amma banda hajiya.
Tace nice na haifeki uwani, na raini ki da hannuna har kika kawo wannan lokacin, ba wanda xai bani labarin halinki ciki da waje sai Ma ni da xan bayar, nafi kowa sanin wacece uwani duk da jiddah ta fini kusanci dake amma Sam bata san halin ki ba, nasan ba kyason jiddah, nasan kin auri mijin tane saboda ki raba ta dashi, ki tuna yanda yarinyar nan tayi shige da fice na ganin kin auri mijinta duk da kowa baya so, ta dauki nauyin karatunki, cin ki, shan ki da suturar ki duk yana hannunta, bata taba aiko mana ko kudin handout naki a bada ba duk itace, ta dauke ki tamkar qanwarta uwa daya uba daya, ta dauki iyayenki da daraja fiye da yanda kika dauke su, ta girmama su tana masu tarbiyar da bakya masu, ta rufa wa iyayen ki asiri da dukiyar ta wacce itace mahaifinki ke juya mata, ta so ki da xuciya daya, ta xauna dake babu cutarwa, ki dubi girman Allah ba dan iyayenki da basu da daraja a gurin ki ba idan kina da sa hannu a batan jiddah kiyi gaggawar maidata kada ki bari a cutar da baiwar Allah, salihar mace mai haquri da yakana.
El'mustapha na labe duk basu sani ba, inda yake labe hawaye yake sai kunga yanda ya koma cikin kwanaki biyu da batan jiddah, ya fita hayyacinsa bashi da lokacin kowa da komai sai na kewar jiddah, xuciyar shi babu sukuni sai faduwar gaba a duk lokacin da ya dubi twins suna neman mahaifiyarsu,
Uwani ta dubi hajiya sosai kalaman hajiya sun shige ta, wannan karon kukan da take na gaskiya ne ba dan komai ba sai dan tausayin jiddah, meyasa jiddah keda masoya haka, meyasa mutane da yawa suka damu da batan jiddah, meyasa mutane da yawa suke kuka suna mata addua, meyasa kowa ke fadin alherin jiddah ake yabata a ko ina,
Taurin kai irin na uwani Sam bai sa taji xata fadi gaskiya ba duk da tayi nadama, tafiso sai burinta ya cika tasan akwai lokacin da watarana xasu manta da jiddah su shafe shafinta a rayuwarsu hakan xai bata damar cimma burinta na ganin ta mallaki el'mustapha yanda take so.
Uwani batayi magana ba sai sharar kwallah take, ita Ma hajiyar kuka take,
Tace indai uwani akwai sa hannunki aciki baxan taba yafe maki ba, kuma baxaki taba cimma duk wani buri naki ko quduri akan jiddah ba, idan kuma babu hannunki ciki ina roqon ko waye Allah ya Toni asirinsa da gaggawa.
Duk wadannan kalamai na hajiya bai sa xuciyar uwani ta karaya ba ita a tunanin ta haqqin mahaifiyarta baxai taba kamata ba tunda ba cin amanar ta tayi ba.
A hankali el'mustapha ya janye jikinsa daga qofar dakin, tafe yake baya ganin gabansa, kuka yake kamar mace idan ya tuna jiddah da cikin dake jikinta, jiri ya soma dibansa, lokaci daya ya fadi gurin ragwaf ba numfashi a tare dashi.
Inna ta saki ihu domin itace a gurin sanda el'mustapha ya fadi, hajiya da uwani suka fito a firgice, securities Ma suka shigo a firgice kowane dauke da bindigarsa tunanin su ko wani abinne daban.
Ganin el'mustapha kwance a gurin yayi matuqar tsorata su, nan da nan aka dauke sa suka nufi asibiti dashi.
Gida da waje maqota abokan arziki, yan uwa babu abinda suke a duk lokacin da suka kai goshin su qasa yayin sujjada banda addu'ar Allah ya bayyana jiddah ya kare ta ya kuma Toni asirin wadanda suka sace ta.
*Team Jiddatulmusty kuyi haquri😒*
*Team Uwanitilmusty kuyi ta murna*
*Team El'mustapha kuje xuwa jinya*.
Pherty........ ✍🏻
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
36
Bayan sati biyu
Cikin kwanakin da jiddah tayi ta dawo wata iri, tayi kuka har ta godewa Allah, bata da wani tunani a xuciyarta yanxu sai na mijinta da twins nata.
'Ashe gaskiya el'mustapha yake gaya mata game da uwani, uwani ba mai qaunarta bace, yanxu ne ta gano abinda el'mustapha ke nuna mata a lokacin yake son ta gano, kenan yasan uwani qaryar ciwo take masa domin ta cutar da rayuwarta, she didn't deserve dis hatred from uwani.
Ta soma kuka mai fitar da sauti, mai nuna alama da baqin cikin dake tattare da xuciyarta, tayi nadama kuma ta tsani uwani a rayuwarta, tana jin baxata taba yafewa uwani ba, yau gashi ta dalilin uwani ta kasa sarrafa qafar ta daya, ta raba ta da ya'yanta da mijinta, ta raba ta da jin dadin ta, an kawo ta an girke inda babu kulawa cikin qartin maxa, ta kwana dasu ta yini dasu, basu da aiki sai shan barasa da chacha, sallah Ma a xaune take yin ta shima wai sai sanda suka ga dama suka kawo mata abinci da ruwa take yin rarrafe ta shiga toilet da kyar tana kuka.
Yanxu kuma taji cikin yayi mata wani iri, ya qara nauyi, motsin da yake yi a da yau kam bata jisa ba,
Ya Allah ka raya min abinda ke cikina, ta maida kanta jikin gwiwowinta tana kuka sosai.
Tana haka goga ya shigo, shi dai Allah ya sanya masa tausayin jiddah, sati biyu da yayi tare da ita ya gane tana da sanyi, tana da nutsuwa da kamun kai sosai yanda take ta rufe jikinta da hijab a duk lokacin da xasu shigo.
Bata da rawar kai duk sanda xasu shigo sai ta gaidasu kuma kome suka ce bata masu gardama illah ta gyada kanta wannan dalilin ya saka kurma jin tausayin jiddah a karo na farko a rayuwarsa daya taba tausayin wata halitta.
Ya xuqi sigari yana kallon jiddah,
Tunda uwata ta haifeni ban taba tausayin kowa ba sai ke, saboda sanyin ki da haqurin ki na lura ke Sam baki da hayaniya, sabanin wasu mata da muke kawo wa nan, daga masu tsiwa sai yan iska ni kuma tattakasu nake, na sa belt na xane shegu idan kuma yarinya ta matsamin na dauke ta da alburushi wanda ya kawo ta yamin maganar banxa na kashe shi haka nake kurma game da kissa.
Jiddah ta sunkuyar da kanta tana share kwallah,
Saboda cikin da ke jikinki xan tausayamaki, na dauko maki tsohuwa a cikin gari xata kula dake kullum na maidata dan baxata xauna dake ba, idan kina jin fitsari ko kashi ki daina rarrafawa ita xata kula da komai, waccan shegiyar matar da ta bamu ajiyar ki itace xata biyata dan ubanta, ta biyamu ta biya wannan tsohuwar tace yau xata xo ta kawo kudin, in kuma qarya take min wlhy cikin ta xan farke har cikin gidan mijin nata, yama kika ce sunanki.
Hauwa ta bashi amsa kanta a sunkuye dan bata qaunar ganinsa ko kadan.
'Yauwa sunan uwar babana ce amma ana ce mata kuluwa dan haka kuluwa xan riqa kiranki dan ni bana girmama kowa a rayuwata, uwata Ma kai tsaye nake kiranta da Ladidi, ya juya ya fice yana tangadinsa na maye, jiddah tabi bayansa da kallo tana sharar kwallah.
Baa jima ba taji uwani a gidan, tana jin su suna kururuwa sunga kudi.
Ina kika sami kudin bayan kince baki dasu,
'Na mijina ne na dauko jiya bayan ya fita😀
Kinyi qoqari, saura na waccan tsohuwar dana gaya maki tana kula da kuluwa, dubu dari biyu ne kudin ta.
Uwani ta bata fuska, batayi magana ba saboda tsoron kurma tasan tsab xai iya dukanta a gurin idan ta musa, sai tace idan xata dawo xata xo dasu.
Suka bude kudin suna dubawa suna jin dadi.
Ina so naga anti jiddah, da hannu suka nuna mata dakin da take.
Jiddah ta rumtse idanuwanta, babu abinda ta tsana a duniyar nan kamar ta dora idanunta a fuskar uwani, ta tsane ta bata son ta ko kadan, to me uwanin taxo tayi a gurinta.
Ayyah anti jiddah haka kika dawo cewar uwani bayan ta shigo dakin.
Kiyi haqurin son mijinki ne ya sakani, kuma gashi har yanxu yaqi ya bani lokacinsa da kulawarsa, bashi da wata damuwa sai ta jiddah, ni kam ya xanyi ne a rayuwata ya soni ki gayamin anti jiddah me kika masa ko kin hada da boka ne.
Shiru jiddah batayi magana ba kuma bata bude idanuwanta ba, uwani ta dafe kanta da goshinta, el'mustapha ya raina min wayo yana hada matsayina da banan, saboda na bigi aryan ya gaya masa ya kecewa duk na sake dukansu banan ta dauki mataki akai, to idan na kashe su ban san wani mataki xaa dauka ba musamman Ma idan na kashe jiddah.
Nan ma jiddah ko motsi batayi ba da uwani xata gane da taja komatsan qafafunta ta tafi ta bar jiddah.
Duk da haka ga zannuwa na kawo maki guda biyu ki qara saboda wannan dake jikinki sunyi datti ga tsamin dauda hala bakya wanka ne.
Jiddah ta bude idanuwanta a hankali tana kallon xannuwan da uwani ta miqo mata, hannu tasa kamar xata karbi xannuwan sai ta fisgo uwani qiris ta fadawa jikinta, ta fadi gurin, takaicin jiddah babu wani abu ko makami a dakin da xata illata uwani, ina Ma qafarta daya nada lafiya ta miqe sosai yanda xataji dadin dukan uwani da kyau.
Ta shaqo wuyan uwani kamar iya qarfinta tana buga kanta a qasa, uwani ta soma ihu tana neman taimako, shigowar su goga ya saka jiddah sakin uwani dan bata qaunar wani daga cikinsu ya taba ta da sunan xai kwaci uwani a hannunta, ta soma kuka.
Uwani ta tashi tana huci, kallabinta a hannu ta gyara rigarta tana kallon jiddah,
Kin jawa kanki anan xaki tabbata ko nasa su kashe min ke, kuma wlhy sai na rama a gurin ya'yan ki.
Ta fice a fusacce goga yabi bayanta dama shi kadai yaxo idan ta kurma ne su kashe kansu ko a jikinsa.
Duk sisters din el'mustapha suma sun shiga damuwa sai dai babu mai xargin uwani duk a cikin su sai hajiya kadai da el'mustapha.
Yanda uwani ta dage tana kuka tana neman jiddah ya saka sauran mutane basa xarginta amma banda hajiya.
Tace nice na haifeki uwani, na raini ki da hannuna har kika kawo wannan lokacin, ba wanda xai bani labarin halinki ciki da waje sai Ma ni da xan bayar, nafi kowa sanin wacece uwani duk da jiddah ta fini kusanci dake amma Sam bata san halin ki ba, nasan ba kyason jiddah, nasan kin auri mijin tane saboda ki raba ta dashi, ki tuna yanda yarinyar nan tayi shige da fice na ganin kin auri mijinta duk da kowa baya so, ta dauki nauyin karatunki, cin ki, shan ki da suturar ki duk yana hannunta, bata taba aiko mana ko kudin handout naki a bada ba duk itace, ta dauke ki tamkar qanwarta uwa daya uba daya, ta dauki iyayenki da daraja fiye da yanda kika dauke su, ta girmama su tana masu tarbiyar da bakya masu, ta rufa wa iyayen ki asiri da dukiyar ta wacce itace mahaifinki ke juya mata, ta so ki da xuciya daya, ta xauna dake babu cutarwa, ki dubi girman Allah ba dan iyayenki da basu da daraja a gurin ki ba idan kina da sa hannu a batan jiddah kiyi gaggawar maidata kada ki bari a cutar da baiwar Allah, salihar mace mai haquri da yakana.
El'mustapha na labe duk basu sani ba, inda yake labe hawaye yake sai kunga yanda ya koma cikin kwanaki biyu da batan jiddah, ya fita hayyacinsa bashi da lokacin kowa da komai sai na kewar jiddah, xuciyar shi babu sukuni sai faduwar gaba a duk lokacin da ya dubi twins suna neman mahaifiyarsu,
Uwani ta dubi hajiya sosai kalaman hajiya sun shige ta, wannan karon kukan da take na gaskiya ne ba dan komai ba sai dan tausayin jiddah, meyasa jiddah keda masoya haka, meyasa mutane da yawa suka damu da batan jiddah, meyasa mutane da yawa suke kuka suna mata addua, meyasa kowa ke fadin alherin jiddah ake yabata a ko ina,
Taurin kai irin na uwani Sam bai sa taji xata fadi gaskiya ba duk da tayi nadama, tafiso sai burinta ya cika tasan akwai lokacin da watarana xasu manta da jiddah su shafe shafinta a rayuwarsu hakan xai bata damar cimma burinta na ganin ta mallaki el'mustapha yanda take so.
Uwani batayi magana ba sai sharar kwallah take, ita Ma hajiyar kuka take,
Tace indai uwani akwai sa hannunki aciki baxan taba yafe maki ba, kuma baxaki taba cimma duk wani buri naki ko quduri akan jiddah ba, idan kuma babu hannunki ciki ina roqon ko waye Allah ya Toni asirinsa da gaggawa.
Duk wadannan kalamai na hajiya bai sa xuciyar uwani ta karaya ba ita a tunanin ta haqqin mahaifiyarta baxai taba kamata ba tunda ba cin amanar ta tayi ba.
A hankali el'mustapha ya janye jikinsa daga qofar dakin, tafe yake baya ganin gabansa, kuka yake kamar mace idan ya tuna jiddah da cikin dake jikinta, jiri ya soma dibansa, lokaci daya ya fadi gurin ragwaf ba numfashi a tare dashi.
Inna ta saki ihu domin itace a gurin sanda el'mustapha ya fadi, hajiya da uwani suka fito a firgice, securities Ma suka shigo a firgice kowane dauke da bindigarsa tunanin su ko wani abinne daban.
Ganin el'mustapha kwance a gurin yayi matuqar tsorata su, nan da nan aka dauke sa suka nufi asibiti dashi.
Gida da waje maqota abokan arziki, yan uwa babu abinda suke a duk lokacin da suka kai goshin su qasa yayin sujjada banda addu'ar Allah ya bayyana jiddah ya kare ta ya kuma Toni asirin wadanda suka sace ta.
*Team Jiddatulmusty kuyi haquri😒*
*Team Uwanitilmusty kuyi ta murna*
*Team El'mustapha kuje xuwa jinya*.
Pherty........ ✍🏻
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
36
Bayan sati biyu
Cikin kwanakin da jiddah tayi ta dawo wata iri, tayi kuka har ta godewa Allah, bata da wani tunani a xuciyarta yanxu sai na mijinta da twins nata.
'Ashe gaskiya el'mustapha yake gaya mata game da uwani, uwani ba mai qaunarta bace, yanxu ne ta gano abinda el'mustapha ke nuna mata a lokacin yake son ta gano, kenan yasan uwani qaryar ciwo take masa domin ta cutar da rayuwarta, she didn't deserve dis hatred from uwani.
Ta soma kuka mai fitar da sauti, mai nuna alama da baqin cikin dake tattare da xuciyarta, tayi nadama kuma ta tsani uwani a rayuwarta, tana jin baxata taba yafewa uwani ba, yau gashi ta dalilin uwani ta kasa sarrafa qafar ta daya, ta raba ta da ya'yanta da mijinta, ta raba ta da jin dadin ta, an kawo ta an girke inda babu kulawa cikin qartin maxa, ta kwana dasu ta yini dasu, basu da aiki sai shan barasa da chacha, sallah Ma a xaune take yin ta shima wai sai sanda suka ga dama suka kawo mata abinci da ruwa take yin rarrafe ta shiga toilet da kyar tana kuka.
Yanxu kuma taji cikin yayi mata wani iri, ya qara nauyi, motsin da yake yi a da yau kam bata jisa ba,
Ya Allah ka raya min abinda ke cikina, ta maida kanta jikin gwiwowinta tana kuka sosai.
Tana haka goga ya shigo, shi dai Allah ya sanya masa tausayin jiddah, sati biyu da yayi tare da ita ya gane tana da sanyi, tana da nutsuwa da kamun kai sosai yanda take ta rufe jikinta da hijab a duk lokacin da xasu shigo.
Bata da rawar kai duk sanda xasu shigo sai ta gaidasu kuma kome suka ce bata masu gardama illah ta gyada kanta wannan dalilin ya saka kurma jin tausayin jiddah a karo na farko a rayuwarsa daya taba tausayin wata halitta.
Ya xuqi sigari yana kallon jiddah,
Tunda uwata ta haifeni ban taba tausayin kowa ba sai ke, saboda sanyin ki da haqurin ki na lura ke Sam baki da hayaniya, sabanin wasu mata da muke kawo wa nan, daga masu tsiwa sai yan iska ni kuma tattakasu nake, na sa belt na xane shegu idan kuma yarinya ta matsamin na dauke ta da alburushi wanda ya kawo ta yamin maganar banxa na kashe shi haka nake kurma game da kissa.
Jiddah ta sunkuyar da kanta tana share kwallah,
Saboda cikin da ke jikinki xan tausayamaki, na dauko maki tsohuwa a cikin gari xata kula dake kullum na maidata dan baxata xauna dake ba, idan kina jin fitsari ko kashi ki daina rarrafawa ita xata kula da komai, waccan shegiyar matar da ta bamu ajiyar ki itace xata biyata dan ubanta, ta biyamu ta biya wannan tsohuwar tace yau xata xo ta kawo kudin, in kuma qarya take min wlhy cikin ta xan farke har cikin gidan mijin nata, yama kika ce sunanki.
Hauwa ta bashi amsa kanta a sunkuye dan bata qaunar ganinsa ko kadan.
'Yauwa sunan uwar babana ce amma ana ce mata kuluwa dan haka kuluwa xan riqa kiranki dan ni bana girmama kowa a rayuwata, uwata Ma kai tsaye nake kiranta da Ladidi, ya juya ya fice yana tangadinsa na maye, jiddah tabi bayansa da kallo tana sharar kwallah.
Baa jima ba taji uwani a gidan, tana jin su suna kururuwa sunga kudi.
Ina kika sami kudin bayan kince baki dasu,
'Na mijina ne na dauko jiya bayan ya fita😀
Kinyi qoqari, saura na waccan tsohuwar dana gaya maki tana kula da kuluwa, dubu dari biyu ne kudin ta.
Uwani ta bata fuska, batayi magana ba saboda tsoron kurma tasan tsab xai iya dukanta a gurin idan ta musa, sai tace idan xata dawo xata xo dasu.
Suka bude kudin suna dubawa suna jin dadi.
Ina so naga anti jiddah, da hannu suka nuna mata dakin da take.
Jiddah ta rumtse idanuwanta, babu abinda ta tsana a duniyar nan kamar ta dora idanunta a fuskar uwani, ta tsane ta bata son ta ko kadan, to me uwanin taxo tayi a gurinta.
Ayyah anti jiddah haka kika dawo cewar uwani bayan ta shigo dakin.
Kiyi haqurin son mijinki ne ya sakani, kuma gashi har yanxu yaqi ya bani lokacinsa da kulawarsa, bashi da wata damuwa sai ta jiddah, ni kam ya xanyi ne a rayuwata ya soni ki gayamin anti jiddah me kika masa ko kin hada da boka ne.
Shiru jiddah batayi magana ba kuma bata bude idanuwanta ba, uwani ta dafe kanta da goshinta, el'mustapha ya raina min wayo yana hada matsayina da banan, saboda na bigi aryan ya gaya masa ya kecewa duk na sake dukansu banan ta dauki mataki akai, to idan na kashe su ban san wani mataki xaa dauka ba musamman Ma idan na kashe jiddah.
Nan ma jiddah ko motsi batayi ba da uwani xata gane da taja komatsan qafafunta ta tafi ta bar jiddah.
Duk da haka ga zannuwa na kawo maki guda biyu ki qara saboda wannan dake jikinki sunyi datti ga tsamin dauda hala bakya wanka ne.
Jiddah ta bude idanuwanta a hankali tana kallon xannuwan da uwani ta miqo mata, hannu tasa kamar xata karbi xannuwan sai ta fisgo uwani qiris ta fadawa jikinta, ta fadi gurin, takaicin jiddah babu wani abu ko makami a dakin da xata illata uwani, ina Ma qafarta daya nada lafiya ta miqe sosai yanda xataji dadin dukan uwani da kyau.
Ta shaqo wuyan uwani kamar iya qarfinta tana buga kanta a qasa, uwani ta soma ihu tana neman taimako, shigowar su goga ya saka jiddah sakin uwani dan bata qaunar wani daga cikinsu ya taba ta da sunan xai kwaci uwani a hannunta, ta soma kuka.
Uwani ta tashi tana huci, kallabinta a hannu ta gyara rigarta tana kallon jiddah,
Kin jawa kanki anan xaki tabbata ko nasa su kashe min ke, kuma wlhy sai na rama a gurin ya'yan ki.
Ta fice a fusacce goga yabi bayanta dama shi kadai yaxo idan ta kurma ne su kashe kansu ko a jikinsa.