Sashe 27
El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk da gajiyar da yake dauke da ita bai hana masa daukan su duka ba, babu walwala a tare dashi, tun daxu yake jin weakness a jikinsa, ga wata irin faduwar gaba da yake ji, tare yake da babban aminin sa ibrahim wurin aikinsu daya sai dai kowa da nashi matsayin.
Ba ku gaida second daddy ba cewar el'mustapha yana kallon yaran,
Suka soma dariya suna kallon ibrahim,
Second daddy ina wuni...
Daga ibrahim har el'mustapha ba wanda baiyi dariya ba, ya sauke su yana kallon banan sanda suka qaraso gurin,
Ta gaidashi tare da abokinsa kanta a sunkuye.
Me kukeyi anan keda twins?
'Anty jiddah ce tun daxu ta fita bata dawo ba, sai ga hawaye sharrr na bin kumatunta.
Nan take yaji gabansa ya fadi, ya juya yana kallon motocin gidan duka suna nan har ta uwani banda ta jiddah, kenan jiddah ita kadai ta fita.
Ibrahim yace kun duba ko ina a gidan bata nan ne?
Tace wlhy ko ina mun duba bata nan.
El'mustapha ya juya ya nufi gate,
Yaushe jiddah ta fita daga gidannan.
Daxu sir, suka amsa masa cikin girmamawa,
Ya akayi kuka barta ta fita ita kadai ko akwai wanda ya bita ne.
Suka soma inda inda cikin rudewa, kowa ya kasa magana saboda tsoro abinda ya qara fusata el'mustapha har yayi masu tsawa, ba shiri daya ya soma magana,
Munyi iya qoqarin mu ta bari muje da ita taqi, tace its urgent an kirata ne yanxu xata da..... Bai qarasa ba el'mustapha ya dauke shi da Mari cikin bacin rai abinda basu taba gani ba tun tarayyar su dashi.
What nonsense are you telling me, ya nayi daku a gidan nan saboda tace haka sai kuka barta ta tafi, kuka xauna kuka miqe qafa anan, to miye amfanin ku if you can't stop her.
Sorry sir suka fada jikinsu a sanyaye,
Waye tace ya kirata..
Bata fada ba sir...
El'mustapha ya furxar da wani xaxxafan iska a bakinsa
Yace believe me idan wani abu ya sami jiddah, ya sami aikin kune, daya bayan daya duk sai na sauke ku, kuje ku nemo ta duk inda ta shiga ina jiranku.....
Ba bata lokaci suka shiga motoci suka raba hanya, el'mustapha ya dafe kansa da hannuwansa biyu, tunani yayi da sauri ya xaro wayarsa aljihunsa ya soma qoqarin kiran layin jiddah, kwata kwata bata shiga, ya kira mamanshi yana tambayar jiddah taje,
Bata xo ba el'mustapha, me ya faru, me ya sami jiddah ne?
Ba komai ya tsinke wayar, hajiya ya kira yana tambayar ta jiddah,
Ba muyi magana da ita xata xo ba kuma bata xo din ba,
Ya tsinke wayar da sauri, hankalin hajiya ya tashi, ta gayawa abba Sam jikinta bai bata akwai lfy ba, Allah yasa ba wani abin ne ya sami jiddah ba.
Duk inda el'mustapha ke sa rai ga ganin jiddah yaje sai ace masa bata je ba, gidan qawayenta duk inda yasan tana xuwa sunje ranar shida ibrahim.
Duk wannan bidirin da ake uwani na dakin ta kwance abinta ta saka earpiece a kunnenta tana shan waqarta abinta batare da damuwa ba.
Banan kuwa tayi qoqarin ganin twins sunci abinci ta saka su barci da kyar saboda fitinar mom din su, ta gabatar da sallolinta tare da addu'ar Allah ya bayyana jiddah ya kare ta daga sharrin masu sharri.
Dawowar su el'mustapha tayi dai dai da dawowar yaransa, kowane jikinsa a sanyaye babu labari amma ga motar ta sun sama a hanya sun rufe sunxo da key kasancewar babu iska a tayoyin.
El'mustapha yayi shiru kamar xaiyi kuka, tunani yake me ya fitar da jiddah, waye ya kirata urgent, su waye suka dauke jiddah, meyasa suka dauke ta, me jiddah tayi masu, sai ya juya xuwa cikin gida, hannunsa yasa yana dauke wasu kwallah.
Insha Allah xaa ganta ka kwantar da hankalin ka xamu tsananta bincike daga yau xuwa gobe, kada kasa damuwa a xuciyarka, cewar ibrahim yana kallon el'mustapha bayan sun xauna a falon.
Innocent jiddah, sun dauke min jiddah akan wane dalili?
Wa kake xargi el'mustapha, waye kake ganin xai iya yi maka hakan.
Mutum daya nake xargi, jiddah bata da abokin gaba ko fada, kuma ni a iya tunani ban san nayiwa wani ko wata wani abin da xaa kullace ni ace xaa dauki mataki akan matata ba.
Waye kake xargi,
Uwani nake xargi, el'mustapha ya fada yana kallon ibrahim cikin seriousness.
Nafi kowa sanin uwani bata son jiddah, she can do anything for her I know, idan har uwani na da sa hannu a batan jiddah believe me ibrahim wlhy xan iya kashe ta, I hate her.
Ya daga murya yana kiran banan.
Ina uwani?
Ina ji tana ciki, ita Ma ban ganta ba duk yau.
Kiramin Uwani taxo yanxu.
Pherty...... ✍🏻
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
35
Uwani ta shigo falon tana tauna cingam, yanayin fuskar el'mustapha yasa ta shiga taitayinta, ta tattaro nutsuwarta guri daya ta xauna tana gaida su.
Kallonta el'mustapha keyi da idanunsa da suka rikide, observing yake akan ta, yana son sanin wani abu a tare da ita,
Muryar ibrahim taji yana fadin, Jiddah bata sanar dake inda xata je ba kafin ta fita.
Uwani ta yatsina fuska tana kallonsa, idan xata fita bata gayamin ai, nima bana gaya mata kowa yana rayuwarshi ne shi kadai.
'Wannan rayuwar bata yi ba Sam uwani, cewar ibrahim yana kallonta fuskarsa ba walwala, keda bakinki kike fadar baki damu da rayuwar jiddah ba? Ke wace irin mace ce mai manta alheri? Ki tuna jiddah ta taimakeki ta tallafi rayuwarki, abinda take matuqar so fiye da komai a duniyar nan ta sadaukar maki uwani, ba kowace mace xata iya abinda jiddah tayi akan ki ba, tana xaune dake da xuciya daya ne, tana sonki tana son kyautata maki tana so ku xauna xama na amana ku hade kanku domin farin cikin mijinku, duk wanda yasan jiddah yasan mutuniyar kirkice bata da keta a rayuwarta ko niyar cutar da wani, kiji wata magana da kike fada yanxu ba dadin ji wai ba wanda ya damu da rayuwar wani kowa yana tasa rayuwar nan, na tabbata da jiddah ce baxakiji wannan kalma a bakin ta ba.
Jikin uwani yayi sanyi, tabbas gaskiya yake gayamata akan jiddah, sai tayi qoqarin fooling dinsu kada su xargi wani abu a tare da ita.
Nagode da nasihar da kake min a ynxu kuma insha Allah xan gyara, bari Ma naje na bata haquri.
Ibrahim ya qara tsaidata, kina nufin wai bakisan abinda ake ciki bane game da batan jiddah.
Kallonsa take baki a bude,
Wlhy ban sani ba, ina taje ne.
Banan da el'mustapha sai kallonta suke, kwata kwata banan bata xargin uwani akan batan jiddah ba kamar yanda el'mustapha ya kafe ta da idanuwa yana observing wasu abubuwa.
Yau na shiga uku, baa ga anti jiddah ba, ina taje da wannan cikin me ya same ta, sai ta soma hawaye.
Banan ma ta soma sharar kwallah,
Abinda uwani taji el'mustapha ya furta ne yayi kusan sumar da ita daga inda take xaune,
Jiddah ta gayamin kece kika kirata a waya ta fita, ina kika kai min matata ta?
Ni? Uwani ta tambaya tana fiddo idanuwa saboda tsananin tsoro da rudewa,
Wlhy ban kira ta, bana waya da jiddah, saboda me xan kirata ta fito?
Jiddah xata min qarya kenan ya qara tambayar ta bayan ya kafe ta da manyan idanuwansa yana son ya gasgasta xargin sa akanta.
Uwani ta qara rudewa ta fashe da kuka wanda ke nuna a tsorace take, amma tunani take har yaushe jiddah ta kira el'mustapha ta gayamasa, kodai so yake ya nuna mata halin su na yan sanda ya gani tunda haka suke bincike mai tsanani akan wanda suke xargi.
Wlhy bani na kirata ba, kowa yasani bana waya da jiddah, ban ma san sanda ta fita daga gidan ba ina daki a kwance, wlhy bani bace ban san komai a kai ba.
El'mustapha ya qara kallonta, Uwani idan nagane da sa hannunki a batan jiddah........ sai kuma yayi shiru ya barwa kansa sani, ya cigaba da fadin ke nake xargi kuma har yanxu xuciyata ke take xargi, xan iya shigar da qara kotu akan ina xargin ki da batan matata saboda nasan ba kyason jiddah baki da buri a duniya na ganin kin kawar da jiddah saboda ki mallaki xuciyar el'mustapha, kinsan nasan bakya qaunar jiddah itace din dai bata gano hakan ba, itace ta rasa gano illar uwani a tare da ita, ta dauki so da amana ta baki wanda ke baki da wani buri na ganin kin cutar da jiddah,
A matsayina na dan sanda xan cigaba da bincike lungu da saqo na ganin masu sa hannu a batan jiddah, xanje na nemota a duk inda take, indai kina da sa hannu a batan jiddah ayi gaggawar maidata inda aka dauketa, ko rantsuwa nayi baxanyi kaffara ba indai da sa hannu uwani a batan jiddah believe me ibrahim alqawari ne nine mutum na farko da xan fara kamata dumu dumu da hannuna, ya tashi ya fice zuciyarsa na quna.
Ibrahim ya kalle ta shima jikinsa yayi sanyi sosai,
Kinji abinda el'mustapha yace uwani, tsakanin ki da Allah ba hannunki a batan jiddah, ki fada min gaskiya ni xan iya kare ki a gurin sa kuma nayi maki alqawari baxan taba bari ya sake ki ba hassalima xanyi qoqarin ganin na dai dai ta ku ya so ki kamar jiddah.
Iya kar gaskiya ta nake fada maku banda masaniya akan batan jiddah.
Indai kinsani dan Allah karku cutar da jiddah,
Ya tashi yabi bayan el'mustapha suka barta anan, banan Ma tashi tayi ta barta.
Washe gari tunda sassafe ibrahim da el'mustapha suka baxa yan sanda bincike ta ko ina, sai sanarwa ake ga duk wanda ya ganta idan kuma kidnapping ne a sanar da su ko nawa ne xasu biya amma kada su taba lafiyar jiddah.
Sai lokacin da hajiya taga hoton jiddah a TV ana sanarwa batan ta sa'anan ta san halin da ake ciki, kuka tayi shi sosai, ranar ita da abba suka je abuja babu kwanciyar hankali tare dasu.
Ba ku gaida second daddy ba cewar el'mustapha yana kallon yaran,
Suka soma dariya suna kallon ibrahim,
Second daddy ina wuni...
Daga ibrahim har el'mustapha ba wanda baiyi dariya ba, ya sauke su yana kallon banan sanda suka qaraso gurin,
Ta gaidashi tare da abokinsa kanta a sunkuye.
Me kukeyi anan keda twins?
'Anty jiddah ce tun daxu ta fita bata dawo ba, sai ga hawaye sharrr na bin kumatunta.
Nan take yaji gabansa ya fadi, ya juya yana kallon motocin gidan duka suna nan har ta uwani banda ta jiddah, kenan jiddah ita kadai ta fita.
Ibrahim yace kun duba ko ina a gidan bata nan ne?
Tace wlhy ko ina mun duba bata nan.
El'mustapha ya juya ya nufi gate,
Yaushe jiddah ta fita daga gidannan.
Daxu sir, suka amsa masa cikin girmamawa,
Ya akayi kuka barta ta fita ita kadai ko akwai wanda ya bita ne.
Suka soma inda inda cikin rudewa, kowa ya kasa magana saboda tsoro abinda ya qara fusata el'mustapha har yayi masu tsawa, ba shiri daya ya soma magana,
Munyi iya qoqarin mu ta bari muje da ita taqi, tace its urgent an kirata ne yanxu xata da..... Bai qarasa ba el'mustapha ya dauke shi da Mari cikin bacin rai abinda basu taba gani ba tun tarayyar su dashi.
What nonsense are you telling me, ya nayi daku a gidan nan saboda tace haka sai kuka barta ta tafi, kuka xauna kuka miqe qafa anan, to miye amfanin ku if you can't stop her.
Sorry sir suka fada jikinsu a sanyaye,
Waye tace ya kirata..
Bata fada ba sir...
El'mustapha ya furxar da wani xaxxafan iska a bakinsa
Yace believe me idan wani abu ya sami jiddah, ya sami aikin kune, daya bayan daya duk sai na sauke ku, kuje ku nemo ta duk inda ta shiga ina jiranku.....
Ba bata lokaci suka shiga motoci suka raba hanya, el'mustapha ya dafe kansa da hannuwansa biyu, tunani yayi da sauri ya xaro wayarsa aljihunsa ya soma qoqarin kiran layin jiddah, kwata kwata bata shiga, ya kira mamanshi yana tambayar jiddah taje,
Bata xo ba el'mustapha, me ya faru, me ya sami jiddah ne?
Ba komai ya tsinke wayar, hajiya ya kira yana tambayar ta jiddah,
Ba muyi magana da ita xata xo ba kuma bata xo din ba,
Ya tsinke wayar da sauri, hankalin hajiya ya tashi, ta gayawa abba Sam jikinta bai bata akwai lfy ba, Allah yasa ba wani abin ne ya sami jiddah ba.
Duk inda el'mustapha ke sa rai ga ganin jiddah yaje sai ace masa bata je ba, gidan qawayenta duk inda yasan tana xuwa sunje ranar shida ibrahim.
Duk wannan bidirin da ake uwani na dakin ta kwance abinta ta saka earpiece a kunnenta tana shan waqarta abinta batare da damuwa ba.
Banan kuwa tayi qoqarin ganin twins sunci abinci ta saka su barci da kyar saboda fitinar mom din su, ta gabatar da sallolinta tare da addu'ar Allah ya bayyana jiddah ya kare ta daga sharrin masu sharri.
Dawowar su el'mustapha tayi dai dai da dawowar yaransa, kowane jikinsa a sanyaye babu labari amma ga motar ta sun sama a hanya sun rufe sunxo da key kasancewar babu iska a tayoyin.
El'mustapha yayi shiru kamar xaiyi kuka, tunani yake me ya fitar da jiddah, waye ya kirata urgent, su waye suka dauke jiddah, meyasa suka dauke ta, me jiddah tayi masu, sai ya juya xuwa cikin gida, hannunsa yasa yana dauke wasu kwallah.
Insha Allah xaa ganta ka kwantar da hankalin ka xamu tsananta bincike daga yau xuwa gobe, kada kasa damuwa a xuciyarka, cewar ibrahim yana kallon el'mustapha bayan sun xauna a falon.
Innocent jiddah, sun dauke min jiddah akan wane dalili?
Wa kake xargi el'mustapha, waye kake ganin xai iya yi maka hakan.
Mutum daya nake xargi, jiddah bata da abokin gaba ko fada, kuma ni a iya tunani ban san nayiwa wani ko wata wani abin da xaa kullace ni ace xaa dauki mataki akan matata ba.
Waye kake xargi,
Uwani nake xargi, el'mustapha ya fada yana kallon ibrahim cikin seriousness.
Nafi kowa sanin uwani bata son jiddah, she can do anything for her I know, idan har uwani na da sa hannu a batan jiddah believe me ibrahim wlhy xan iya kashe ta, I hate her.
Ya daga murya yana kiran banan.
Ina uwani?
Ina ji tana ciki, ita Ma ban ganta ba duk yau.
Kiramin Uwani taxo yanxu.
Pherty...... ✍🏻
EL'MUSTAPHA
Haske Writers Association
Home of experts and perfect writers
Fertymerh Xarah💞
35
Uwani ta shigo falon tana tauna cingam, yanayin fuskar el'mustapha yasa ta shiga taitayinta, ta tattaro nutsuwarta guri daya ta xauna tana gaida su.
Kallonta el'mustapha keyi da idanunsa da suka rikide, observing yake akan ta, yana son sanin wani abu a tare da ita,
Muryar ibrahim taji yana fadin, Jiddah bata sanar dake inda xata je ba kafin ta fita.
Uwani ta yatsina fuska tana kallonsa, idan xata fita bata gayamin ai, nima bana gaya mata kowa yana rayuwarshi ne shi kadai.
'Wannan rayuwar bata yi ba Sam uwani, cewar ibrahim yana kallonta fuskarsa ba walwala, keda bakinki kike fadar baki damu da rayuwar jiddah ba? Ke wace irin mace ce mai manta alheri? Ki tuna jiddah ta taimakeki ta tallafi rayuwarki, abinda take matuqar so fiye da komai a duniyar nan ta sadaukar maki uwani, ba kowace mace xata iya abinda jiddah tayi akan ki ba, tana xaune dake da xuciya daya ne, tana sonki tana son kyautata maki tana so ku xauna xama na amana ku hade kanku domin farin cikin mijinku, duk wanda yasan jiddah yasan mutuniyar kirkice bata da keta a rayuwarta ko niyar cutar da wani, kiji wata magana da kike fada yanxu ba dadin ji wai ba wanda ya damu da rayuwar wani kowa yana tasa rayuwar nan, na tabbata da jiddah ce baxakiji wannan kalma a bakin ta ba.
Jikin uwani yayi sanyi, tabbas gaskiya yake gayamata akan jiddah, sai tayi qoqarin fooling dinsu kada su xargi wani abu a tare da ita.
Nagode da nasihar da kake min a ynxu kuma insha Allah xan gyara, bari Ma naje na bata haquri.
Ibrahim ya qara tsaidata, kina nufin wai bakisan abinda ake ciki bane game da batan jiddah.
Kallonsa take baki a bude,
Wlhy ban sani ba, ina taje ne.
Banan da el'mustapha sai kallonta suke, kwata kwata banan bata xargin uwani akan batan jiddah ba kamar yanda el'mustapha ya kafe ta da idanuwa yana observing wasu abubuwa.
Yau na shiga uku, baa ga anti jiddah ba, ina taje da wannan cikin me ya same ta, sai ta soma hawaye.
Banan ma ta soma sharar kwallah,
Abinda uwani taji el'mustapha ya furta ne yayi kusan sumar da ita daga inda take xaune,
Jiddah ta gayamin kece kika kirata a waya ta fita, ina kika kai min matata ta?
Ni? Uwani ta tambaya tana fiddo idanuwa saboda tsananin tsoro da rudewa,
Wlhy ban kira ta, bana waya da jiddah, saboda me xan kirata ta fito?
Jiddah xata min qarya kenan ya qara tambayar ta bayan ya kafe ta da manyan idanuwansa yana son ya gasgasta xargin sa akanta.
Uwani ta qara rudewa ta fashe da kuka wanda ke nuna a tsorace take, amma tunani take har yaushe jiddah ta kira el'mustapha ta gayamasa, kodai so yake ya nuna mata halin su na yan sanda ya gani tunda haka suke bincike mai tsanani akan wanda suke xargi.
Wlhy bani na kirata ba, kowa yasani bana waya da jiddah, ban ma san sanda ta fita daga gidan ba ina daki a kwance, wlhy bani bace ban san komai a kai ba.
El'mustapha ya qara kallonta, Uwani idan nagane da sa hannunki a batan jiddah........ sai kuma yayi shiru ya barwa kansa sani, ya cigaba da fadin ke nake xargi kuma har yanxu xuciyata ke take xargi, xan iya shigar da qara kotu akan ina xargin ki da batan matata saboda nasan ba kyason jiddah baki da buri a duniya na ganin kin kawar da jiddah saboda ki mallaki xuciyar el'mustapha, kinsan nasan bakya qaunar jiddah itace din dai bata gano hakan ba, itace ta rasa gano illar uwani a tare da ita, ta dauki so da amana ta baki wanda ke baki da wani buri na ganin kin cutar da jiddah,
A matsayina na dan sanda xan cigaba da bincike lungu da saqo na ganin masu sa hannu a batan jiddah, xanje na nemota a duk inda take, indai kina da sa hannu a batan jiddah ayi gaggawar maidata inda aka dauketa, ko rantsuwa nayi baxanyi kaffara ba indai da sa hannu uwani a batan jiddah believe me ibrahim alqawari ne nine mutum na farko da xan fara kamata dumu dumu da hannuna, ya tashi ya fice zuciyarsa na quna.
Ibrahim ya kalle ta shima jikinsa yayi sanyi sosai,
Kinji abinda el'mustapha yace uwani, tsakanin ki da Allah ba hannunki a batan jiddah, ki fada min gaskiya ni xan iya kare ki a gurin sa kuma nayi maki alqawari baxan taba bari ya sake ki ba hassalima xanyi qoqarin ganin na dai dai ta ku ya so ki kamar jiddah.
Iya kar gaskiya ta nake fada maku banda masaniya akan batan jiddah.
Indai kinsani dan Allah karku cutar da jiddah,
Ya tashi yabi bayan el'mustapha suka barta anan, banan Ma tashi tayi ta barta.
Washe gari tunda sassafe ibrahim da el'mustapha suka baxa yan sanda bincike ta ko ina, sai sanarwa ake ga duk wanda ya ganta idan kuma kidnapping ne a sanar da su ko nawa ne xasu biya amma kada su taba lafiyar jiddah.
Sai lokacin da hajiya taga hoton jiddah a TV ana sanarwa batan ta sa'anan ta san halin da ake ciki, kuka tayi shi sosai, ranar ita da abba suka je abuja babu kwanciyar hankali tare dasu.