← Book details El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 80

Sashe 22

El-mustapha Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Arham ya dubi el'mustapha, daddy kaga mamman anty uwani.

Uwani ta dubeshi a fusacce, a ranta tace xakaci ubanka ne bari na damqeka, sai a lokacin jiddah ta kai kallonta ga uwani, ta kasa boye mamakin ta, wannan wace shiga ce uwani tayi.

'Nikam uwani da kin sauya wannan rigar cewar jiddah tana qoqarin xama kusa da el'mustapha.

Saboda me? Uwani ta tambaya tana kallonta cikin harara.

Saboda ya'yana, basu saba ganin wannan haukar ba kinga sai magana suke ai kada a lalatamin tarbiyar yara, su taso suna sabawa iyayen su.

Sai ki kauda idanunsu daga kallon jikina, amma nida gidan mijina baxaa xabamin kayan da xan saka nayi masa kwalliya ba, ke idan bakya masa ni kinga inayi.

'taya akayi kika san bana masa, dole sai na fito na nunawa kowa ne ko kuma sai na fada, macen da bata da sirrin kanta ballagaza ce, macen dake bayyana sirrin mijin ta wawiya ce, macen da xata nunawa duniya mijinta ya kwanta da ita ba kunya a tare da ita jahila ce, idan kwalliya xaki masa kiyi daga ke sai shi amma ba irin wannan gidan da aka hada da iyali ba, so Aisha aje a canxa kayan bana son ya'yana suna kallon abinda ya haramta a garesu kada suje suna leqen na wasu.

Uwani xatayi magana cikin tsiwa el'mustapha ya katse ta cikin fushi,

Get out pls.....

Yanxu honey ni kake wulaqantawa a gaban matarka da ya'yan ka, menene laifina dan na maka kwalliya, saboda na faranta maka ne na sami lada.

Yace baki ji ba kenan baxa kije ki canxa kayan ba? Uwani ta fice a fusacce batayi mgn ba.

Bata fito ba sai da ta tabbatar ya bar gidan, still da rigar ta fito aryan na ganinta yayi dakin mamansa da gudu yana fadin,

Momy xo kigani bata cire ba akwai mamman ta a waje,

Sai na fadawa daddy arham ya fada yana kallonta, bugu ta kai masa hade da qara bige masa baki, ya saki kuka hade da nufar dakin jiddah, bayansa tabi tana fadin uwarka Ma ciki nake da ita ko ita xan iya duka a gidannan.

Momy anti uwani ta dake ni anan da baki,

An dake ka ko akwai uban da xai rama Ma kane?

Babu shi, jiddah ta fada tana kallonta, saboda me dan kin daki yaranki a rama masu? Ta dubi twins, kuba anti uwani haquri kuxo kuji.

'Anty uwani kiyi haquri suka fada lokaci daya kafin su nufi jiddah,

Uwani taji haushi taso jiddah ta tanka mata ne ta mata dukan tsiya, meyasa jiddah ta cika sanyin xuciya da haquri ne, ita wlhy ynxu ko kunya da nauyinta  bata ji kallon kishiya take mata wace basu taba sanin juna ba sai xaman aure da ya hada su.

Naxo inma mutum gargadi akan a daina sakamin ido a al'amurana wlhy kome xan iya Ma mutum a gidan nan, babu wata dangantaka ko xumunci tsakanina da kowa a gidannan sai xaman kishi ehe, mtsewwwww ta fice.

Jiddah tabe bakinta kawai tayi, ta dubi arham har lokacin hawaye yake yi, taja dogon hancinsa tana murmushi.

My boy babu jarumta, duka kake Ma kuka, babu ruwanku da anti uwani da kayan da take sakawa, share hawayen ka kuma kar naji an gayawa daddy.

Nidai momy sai na gayamasa anty uwani ta daki arham yayi kuka cewar aryan yana tunxuro baki.

Kuyi haquri baxata qara dukan kowa ba, inma ta qara ni xan rama maku, back to our lesson, kowa ya dauko nayi masa marking naga wayafi qoqari, suka fita da gudu.

Bata jima da sallame sallah ba el'mustapha ya shigo,

Yauwa ba sai kin cire hijab din kixo xamuje ku gaida mama bata lafiya.

Sun fito uwani sai tunxure tunxure take Allah ya gani batayi niyar xuwa ba ita ina ruwanta da mamanshi da xataje gaidata bata da lafiya,

Gidan gaba ta shiga tana fadin ai girkin tane ita xata xauna da mijinta, murmushi kawai jiddah tayi ta shiga baya tare da twins din ta, el'mustapha kuwa ko kallon inda take baiyi ba.

Yaran da gudu suka nufi mama, sun kwana biyu basu je ba sai murna suke, ita Ma sosai taji dadin ganinsu harda yayyun el'mustapha mata duka sunxo dubinta.

Jiddah ta gaidasu kafin ta nufi mama tana yi mata ya jiki.

Uwani kuwa gefe taja tunga tana fadin ina wunin ku.

Suka amsa ba yabo ba fallasa musamman sun san uwani a gidan jiddah basu jituwa da ita sai gashi taxo ta auri qaninsu inda suka qara jin tsanar ta kenan.

El'mustapha takaici ya rufe shi, ko ya jiki baxata iya Ma mahaifiyar sa bane,

Mama Ma kallonta kawai take tana Allah ya wadarai a xuciyarta, dakin sai hira ake da dariya banda uwani dake cika tana batsewa ita matar AIG😂.

Sun jima sosai ganin dare yayi twins har sunyi barci ya saka suka fito,

Abincin da tayi ranar qin ci yayi yaji ya qara tsanar yarinyar tunda baxata iya girmama iyayenshi da yan uwansa ba, juice kawai ya sha abinda bai sani ba uwani ta saka pills a ciki😀

Sanda ya fara jin feelings sai ga uwani ansha kwalliya cikin wata farar night gown, tayi kyau kam, kallonta kawai el'mustapha yayi wannan karon abin baiyi qarfi kamar wancan ba,

'me kike min a daki?

Honey kaine fa kace duk ranar girkina naxo muriqa kwanciya tare nayi missing dinka kwana biyun nan haquri kawai nake.

Kallonta yake da idanunsa da suka rikide xallar sha'awa ce aciki sai ya fara ganinta kamar jiddansa, uwani taxo tana shafa jikinsa, qirjinsa har cikin kansa.

Hannu yasa ya rungumota yana kissing din ta, hancinsa ya kai dai dai wuyanta yana shaqar qamshin jikinta, uwani da kanta take cire kayan jikinta yanda xataji dadin abin.

Tsura mata ido yayi yana kallonta lokacin da take qoqarin cusa harshenta cikin bakinsa.

Ya kauda kansa gefe, kamar wanda aka tsikara ya miqe xumbur ya bar dakin,

Takaici kamar xai kashe uwani, harda xaginsa a bayyane, sai da ta fara jin dadin abin xai guje ta, ita ta rasa gane wane irin turare ne wannan yake amfani dashi mai dadi, ta fito dakin bayan ta rufe jikinta kallon qofar dakin jiddah take.

Kambu ni xaa kaiwa wata kwana na, bala'i wannan Ma cin amana ne wlhy baxan yarda ba.

Kamar a mafarki jiddah taji ana shafar jikinta ta bude idanuwanta a hankali, baxata iya ganinsa ba saboda duhun dakin qamshin turarensa taji ta gane shi, ta riqe hannuwansa da sauri lokacin da yake qoqarin cusa su a cikin rigarta.

'kai kuma yaushe ka fara shige ne,

Baiyi magana ba,  sai ta fara qoqarin janye jikinta,

Cikin murya rada rada a kunnuwanta yake mgn,

Let me, pls jiddah I can't control my self bansan meyasa ba.

Meya sami uwani ne, ko ka manta girkinta ne.

I know jiddah, bana son uwani, I don't want anything from her, she can't satisfy me.

Idan kayi haka baka kyauta ba, ka dauko kwananta ka kawo min batare da amincewar ta ba, munci amanar ta, nima baxan so ayimin hakan ba, yaushe kadawo haka el'mustapha, yaushe sha'awa ta fara maida ka haka, you can't control yourself why? Kodai wani abin kaje ka sha ne?

Nima ban sani ba jiddah, pls help me kada ki gujeni.

Ni baxan iya ba ta fada a fusacce bayan ta juya masa baya.

Shikenan jiddah ki barni na mutu sai ki huta, yayi xaune ya dafe kansa da hannuwansa duka biyu, dakin har wani juyamasa yake,haka yaji marar sa ta fara ciwo, ya juya yana kallon jiddah a karo na biyu ji yake kamar ya kamata yayi mata ko ta qarfi ce amma he can't baxai iya Ma jiddah hakan ba.

Jiddah bakya tausayi na yanxu, kinsan me nake ji kuwa, tunda nake dake baki taba juya min baya ba sai yau why jiddah? Muryarsa ta fara rawa kamar xaiyi kuka ita kanta dake kwance qarfin hali kawai take amma tausayinsa ya cika xuciyarta, bata juyo ba har sanda taji ya kwanta a bayanta, tana jin fitar numfashin sa da sauri da sauri, ta matsa kadan kafin ta juyo tana kallonsa.

Kasani saboda son ka baxai sa na cutar da waccan ba Allah xai kamani da laifi saboda me baxakaje gare ta ba.

Wata dabara ta fado masa nan take a xuciyarsa, da kyar ya iya magana.

'Na yarda kije yanxu ki tambayeta kiji, period take yi jiddah itace ta amince min.

Ita uwanin?ta tambaya cikin mamaki,

Ya gyada kansa, bai yarda ta qara magana ba ya fisgota matse ta yayi sosai a jikinsa.

'Washe garin ranar bai bar dakin ba sai da jiddah ta gayamasa cikin da take dauke dashi.

Are you serious?ya tambaya cikin tsananin mamaki, ta gyada kai tana kallonsa da murmushi,

Jiddah na ba haquri, kin dora min auren da bana so saboda ya'ya yau gashi Allah ya baki bai bata ba, meke nan, nikam kin cuci rayuwata na hadani da waccan matar.

Ta lakaci hancinsa tana dariya, dama can matar kace believe me nice sanadi amma uwani tana cikin qaddarar ka, kadaina cewa na cuce ka mijina ni kaina na cuci kaina *NAYI NADAMAR* auren ka da Uwani.

Ya juya yana fadin xo in goyaki jiddana, na nuna maki farin cikina akan wannan cikin, ina maraba dashi kuma ina tsananin qaunarsa kamar yanda nake son jiddah.

Da sauri jiddah ta haye bayansa tana dariya, ta sumbace shi tana fadin, Allah ya barmin kai mijina, ina sonka el'mustapha💕💕💕💕💕💕

Uwani bata nunawa jiddah komai a fuska ba amma a xuciyarta ta barwa kanta sani, ko ni pherty banda masaniya akan wannan🤧

Bayan kwana biyu jiddah ta shirya xataje gida ganin su hajiya ta kwana biyu bata je ba, sai ta tambayi uwani ko xataje.

Tace baxan jeba, inma xan je ne batare da ke ba, nida iyayena anuna min anfi son wata bare dani, ni saboda me ma xanje na gansu mutanen da basu farin ciki dani basu farin ciki da aurena.

Jiddah tace shiyasa kika kasa ganin haske a rayuwar auren ki, kin kasa gane inda mijinki ya dosa akanki saboda iyayen ki suna fushi dake kuma ke baxakije ki nemesu gafara ba taya kike son rayuwar auren ki tayi kyau.
Chapter 22 · 0% Book details