← Book details Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 56

Sashe 33

Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tabbas ya san shine ya jaza masu, ba tare da sanin su ba, ta yaya zai bi ya warware wannan tsanar da suke fuskanta? Laifin shi ne, ina ma ace da wata yayi wannan trap ɗin ba suhana ɗin ba, "Huh" ya sauke ajiyar zuciya cikin sanyin jiki ya ja ƙafafu shi daƙyal ya isa ga bakin gadon ya zauna yana mai dafe kanshi cikin matsananci yar damuwa, menene ya sanya yanzu yake yawan kula da al'amarin yarinya ne? Menene ya sanya yanzu tinanin ta baya fita a ranshi? Hannu ya sanya gami da jawo wata farar leda, fiddo Abunda yake ciki yayi ya shiga juyawa a hannun shi, waya ce mai masifar kyau, sabuwa dal a kwalin ta, ƙirar Samsung galaxy.

Tunani yake ta yanda wayar zata isar mata ba tare da kowa ya fahimta ba yanzu, tinda ƴan gidan sun dawo, su kansu munafuka masu aikin yanzu zasu dinga kai komo acikin gidan, wani tinani ne ya faɗo mashi arai, maida wayar yayi cikin ledar ya miƙe gami da aza ta bisa mirror ɗin da yake ɗakin ya fice domin zuwa yi ma Mom ɗin tashi barka da zuw.

A babban falo dukan su ya tada su, sun baje gajiya tayi masu ligif, Hajiya Kubra ce kawai bata wajen ita da aminan nata, suna cen sun ƙule a sashe na Hajiyar suna tattauna wa, gaida shi suka shiga yi, ya amsa masu babu yabo babu fallasa, sannan ya maida hankalin shi akan Hafsat ɗin da take jingine da kujera saman carpet, cikin ɗan dakin fuska yace "Hafsat ya gajiyar tafiya, fatan kun dawo lafiya?" ɗan murmushi tayi tana mai cewa "lafiya ƙalau yaya, ya muka same ku?" Lafiya lau ya bata amsa, yana mai nufar upstair domin zuwa ga Mom ɗin tashi.

Ƙwanƙwasa ƙofar ya shiga yi, daga cen ciki aka bashi umarni ya shiga, cikin takun shi na ingarma namiji ya taka ya shiga bakin shi ɗauke da siririya sallama, da kallon ƙauna mahaifiyar tashi ta bishi, ɗan nesa dasu ne ya samu kujera gami da zama, ya shiga gaida su harda ƙawayen mahaifiyar tashi, cikin fara'a suka gaida shi suna tambayar shi wajen aiki, ya amsa masu da lafiya, yana mai tambayar su hanya, duka lafiya suka shaida mashi, miƙewa yayi gami da cewa "Mom zan ɗan fita kafin ki gama dasu, ina dawowa anjima"

Bai jira cewar ta ba, ya fice daga falon, cen ƙasan ranshi, haushi fal na abokan mahaifiyar tashi, domin shi fa in ba zuga ta ba, da ƙara kambama mata kai baiga abinda suke yi ba, baiga dalilin ta ba ma na kwasar su su wani tafi siyayyar aure ba, Abunda ko daga nan gida nigeria zaka iya Kyi order ɗin duk abinda kake so, ya iso maka kuma har gida, salon ɓarnatar da kuɗi kawai, da son neman suna😒

Da kallo suka bishi dukan shi, har ya idasa ficewa a falon, ajiyar zuciya suka shiga sauke wa, sa'ilinbda Hajiya sa'a ta kalli Hajiya Kubra, "Lallai Hajiya ta, Al'ameen ne ya ƙara girma haka? Kina me da har yake neman jawo maki magana da raini, ta hanyar auren waccen koɗaɗɗar? Kiyo iya yin ki duk yanda zakiyi kiga kin daƙile wannan maganar wallahi, yaro mai jini a jiƙa kaman wannan ga naira ga kyau ga gayu? Tabɗi gaskiya kinyi sake, ni ba ma ga amfanin zaman da suke yi a cikin gidan ba, har ma zai dinga iya ganin ta kullum, kiyi amfani da damar ki, tin kafin kina kallon ruwa kwaɗo yazo yayi maki ƙafa, kina dai gani irin waɗannan yaran su ne yaran masu kuɗi da faɗa aji a faɗin duniya suke so su samu, ba ma nigeria ba, yo wannan ko a India yaga wata yace yana so ai wallahi ba zata yi mashi musu ba, balle waɗancen talakawan"
Hajiya Kubra ce ta nisa gami da cewa " Humm bari dai Sa'a, wallahi kina ganin shi haka shegen tarin kai ne dashi kaman mahaifin shi, ba yanda banyi ba Amman abun yafi ƙarfi na, dama da dukiya nake taƙama, tau duk kansu daga shi har mahaifin nashi babu wanda bai fini ba a halin yanzu, nayi ƙoƙarin nuna ƙarfin uwa akan shi, Alhaji yana man ba razana da aure na, ni kau kjnga ba zanyi sake in rasa alhaji ba, samun kaman Alhaji a yanzu zai yi mani wahala... " Hajiya Laila ce ta katse ta da cewa ki bar mana komai a hannun mu Kubra, ba zai gagara ba, me aka yi a kayi Maryama balle wata ɗiyar ta cen, bari a gama hidimar nan zamu san abun yi, in ance ya ƙara kallon su ma ba zai kalla ba ko da kuɗi, kuma beside ma ni bana tinanin son ta yake yi, kinsan fa waɗannan miskilan yanda suke, nafi tinanin dai yana so ya kulle maki baki ne akan zancen aure da kike mashi" duk kansu sun gamsh Sa da hakan sun kuma sha alwashi ɗaukar mataki bayan kammala bikin Saudat da Nihal ɗin da yake saura sati biyu ayi.

Kai tsaye sashen shi ya koma, baya jin ma mararin fitar, idan ma ya fita ba inda za shi, shi ba mutum bane mai yawo, Shiyasa ma ko abokan kirki baya dasu, sau tari yafi buƙatar ya zauna gida yana aiwatar da dukkan muhimman abubuwa a cumputer ɗinshi akan ya fita ya ɓata lokacin shi ga banza wajen abokai, duk kuwa da yanda samari da dama ke fatan ace shi ɗin abokin su ne, koda kuwa na wucin gadi ne.

Bilal ya kira suka sha firar su, yake sanar dashi shigowar shi satin sama, domin su fara tsara yanda tashi hidimar zata kasance, "Abokina kayi ƙoƙari kaima ka fidda matar aure, duk da na san kai mata basa ga anka, Amman ai ba zaka ci gaba da zama haka ba, ko so kake yi ne sai mun haɗa ka da abie ne sannan zaka yi auren, ka kuwa san lokacin ka tsufa babu wadda zata gani ta ƙyasa"

Murmushi yayi irin wanda ke ƙara ƙawata mashi kyakkyawa fuskar shi, sannan ya shiga maida mashi da amsa "Ai sai kazo kayi mani malan, na lura kaima team ɗin Mom kake, Kaga mubar maganar nan sai kazo zamu tattauna, bari in tashi in fita wajen mata san cen da na sanya a tattara mani zamuyi meeting dasu da ƙarfe biyar na yammaci kasan yanda abubuwan suke yanzu wallahi, ina tinanin zan basu hutu ne har agama hidimar nan ta bikin yaran nan, kada kwalwa ta ta buga hakanan" "Is ok Friend sai kunyi magana" Bilal ɗin ya amsa mashi ta ɗaya ɓangaren, sallama sukayi yayin da ya tashi ya fice hannun shi ɗauke da ledar wayar nan.

MuÉ—i driver ya ba, ya umarce shi da ya kawo mani, shi zai fita ne sai ya dawo mmanka kula.

Cikin hanzari kuwa ya russuna ya amsa yana mai cewa "To yallaɓai" kai tsaye motar shi ya nufa, yayin da mudinya nufi sashen namu ba tare da ya damu da ya san menene acikin ledar ba.

Sallamar mudin ce ta katse ni daga shirya mana kaya da nake ta faman yi a wardrop, amsawa nayi gami da zura hijabina na leƙa ina mai gaida shi, amsawa yayi yana mai miƙo manledar dake hannun shi, "Gashi inji Alhaji ƙarami yace in kawo maki" amsa nayi ina mai cewa tou Mudi an gode, juyawa yayi ya bar wajen tin kafin wani ya gashi, yayin da na koma cikin ɗaki ina mai nuna ma umma ta dake zaune bisa darduma tana karatu.

"Wai Ya Ameen ne yace ya kawo mani" na faÉ—a ina dire ledar gabanta, ba tare da na damu da sanin menene ciki ba, duk a zato na Abunda ya danganci karatu na ne.

"Ki buÉ—e mana kiga menene a ciki" cewar umman tawa, tana mai É—an É—aure fuska haka kaÉ—an bansan menene dalili ba.

Kwalin dake cikin ledar na fiddo, gaba na ne ya faÉ—i, na É—an É—ago na saci kallon umma ta da ta tura mani idanu taga yanda zanyi, hannu na kuma Sanyawa na zaro Æ´ar mitsitsiya waya ta da Naji tana vibrating a cikin ledar.

Saƙo ne ya shigo, number ce ban damu da in buɗe ba balle inga Abunda aka rubuta, durkushe nake gaban umman tawa kawai ina so inji hukuncin da zata yanke a kaina game da amsar kyautar waya daga hannun yaya Al'ameen ɗin.

~Oum-Deedat ce~
[9/15, 7:53 AM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

🌹 *BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺

*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._

*Page ~20~*

°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°

Sai faman zare idanu nake yi, kaman wadda tayi ma sarki ƙarya, hukuncin umman tawa kawai nake jira inji me zata yanke akai.

Shiru tayi na tsawon minti biyar, nazari ɗiyar tata take yi, fatan take ace ba ita ce ta roƙeshi ba.

Nisawa tayi kaÉ—an a hankali ta muskuta, tana mai ajiye littafin dake hannun ta, har yanzu bata É—auke idanun ta akai na ba.

" Suhan! Ina fatan dai ace ba kece kika roƙeshi waya ba, ba zaki iya haƙuri da wadda Allah ya baki ba" na tsinkayo muryar ta kwatsam cikin kunne na.

Girgiza mata kai na cigaba da yi, ina cewa "a'a umma wallahi ban roƙeshi ba" kwashe yanda muka yi da yaran nan nayi a makaranta kwana biyu da suka wuce, har zuwa kan inda ya ɗauki wayar bai bani ba, Amman ban gaya mata ya goge man ƙwalla ba, balle ince ya kama man hannu, don na san tashin hankalin da zan fuskanta.

Shiru ta sake yi sannan tace "Allah shi kyauta, an gode, Amman ina so ki riƙe talaucin ki, ki dinga juya ma abun duniya baya, wannan ƴar ƙaramar ta isheki, sai dai bazan hana ki amfani da wannan ba, saboda zamani ne yazo da ita"
Chapter 33 · 0% Book details