Sashe 15
Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
marin da ta sauke man a kan fuska ta har guda biyu, su sukayi sanadiyyar datsewar maganar tawa, ɗif nayi dafe da kunci, kaman ruwa ya ci ni, yau ni ce umma ta ta buga, yau ni ce durƙushe gaban mahaifiyar tawa ina faɗa mata malaman da suke barazana ga lafiyar ta, ba zan iya tuna lokacin da umma ta ta ɗauki hannu ta bigeni ba, saboda ita mace ce mai san yin hali, Sam bata da zafi;
kuka na fashe dashi lokaci guda ina mai ƙanƙame jikina, yanda naga ta hassala kaman zata rufe ni da suka.
"Ashe ke shashasha ce hauwau ban sani ba?, ina tarbiyyar da na baki? Ina kika kaita, nan ɗin da kike ganin ana wulaƙanta mu, ya fiye mana cen, in kika koma kashe ki zasu yi, nace kashe ki zasu yi! Ni ma ba zasu barni ba, saboda ke nake zaune nan, dan ki tsira da mutuncin ki, ki tsira da rayuwarki yasa nake zaune nan, nima abun yana man zafi, Amman ko me zasu yi mana ba zasu iya kashe mu ba, zaki mutu ne muddin kika yarda kika koma cen" kwalla ce ke shata ta a idanun umman tawa, abun da ya ƙara matuƙar firgita ni kenan, rarrafawa na shiga yi ina mai zuwa inda take na rungume ta, ture ni ta shiga yi, jeki, je ki nemi mahaifin ki, ƙila zakiyi sa'ar ganin kabarin nashi, ƙila zai iya tashi ya faɗa maki komai, Hauwa'u ban tsammanin akwai ranar da har ke zaki iya zuwa ki sanya ni a gaba ba, ki titsiye ni sai na faɗa maki wacece ke ba, na ɗauka na gama maki komai, na ɗauka na ishe ki komai, ban tsammanin zaki gaji da zama a inda na zaɓa mana rayuwa ba, nace kashe ki zasu yi, muddin kika yarda suka san kina nan da ranki, jeki jeki ki nemo dangin mahaifin ki, ki nemo dangi na, Amman ni kar ki ƙara tambaya ta game da su, kar kuma ki sake ki dawo inda nake, kuma duk Abunda ya same ku ke ce kika siya da kuɗin ki, kar ki ƙara tambaya ta abunda ya shafe su; Ta shiga ƙara ture ni daga jikin ta tana mai share kwallar da take ta ambaliya a fuskar ta.
Ƙara ƙwaƙume ta nayi, ina mai sakin gunjin kuka lokaci guda ina mai faɗin "Umma kiyi haƙuri ki yafe man, ki gafarce ni umma, nayi maki laifi, na aikata maki ba daidai ba umma, na cutar da zuciyoyinmu umma, bansan haka ba, bansan komai ba umma ki yafe man" shiru naji lokaci daƴa kaman ma bata numfashi, A firgice na ɗago, domin in ga me ke faruwa, abunda idanunwa na suka gani ne ya sani sakin razananiyar ƙara da sai da ta cika ilahirin sashen namu. Jikin ta gaba ɗaya ya saki, kaman wadda ta mutu bata numfashi Sam, "umma ki tashi" na shiga faɗi lokaci ɗaya ina mai jijjiga ta "umma ki tashi don Allah na bari, umma ki yafe man, umma kar ki mutu ki barni don Allah, umma ban da kowa sai ke, ke ce uwa ta ke ce uba na umma, ke ce komai nawa umma, kar ki mutu ki barni a cikin gidan nan umma, zan mutu nima in biki wallahi muddin kika barni, umma basa son mu basa ƙaunarmu, kar ki barni ni ɗaya a cikin gidannan" kuka ne gami da majina suka bi suka haɗe a yalwataciyar fuskar tawa, bama ta su nake yi ba, balle in mai da kai wajen share wa, gunjin kuka na nake yi mai cike da ruɗani kala kala, yayin da umman tawa take sharaf a jikina babu alamar numfashi tattare da ita, kwantar da ita na shiga yi lokaci guda ina mai girgiza kaina "umma ta bazata mutu ta barni nan ni kaɗai ba, bansan kowa ba umma sai ke" haka nake faɗa yayin da na tashi na fice da matsanancin gudu zuwa nemo wanda zai duba man ita, a tsakar gida muka haɗu da sauran ƴan aikin gidan da duk sun jiyo kuka na sun fito hankali tashe, hannun uwani na shiga ja ko sauraren ta banyi ba ina faɗin "mama uwani Kuzo ku duba man umma ta kar kuce man ta mutu, kar kuce man bata da rai, kar ku kashe man ita" mama Talatu Kuzo" na saki hannun mama uwani da nufi mama Talatu da gudu itama na shiga jan ta, ina mai sake sakin kuka mai tsuma rai, "me ya samu maman Suhana ɗin ne wai? " mama uwani take tambaya ta, ban iya bata amsa ba, domin naga sun yi tsaye sun ma ƙi shiga ɗakin, hanyar waje na nufa da gudu cikin kuka ina kwala ma baba idi kira, yazo ya duba ban umman tawa.
Tin daga nesa ya hango ta, Ya Ameen ne da ya fito daga part ɗin nashi cikin shirin zuwa wajen aiki, suit ce sanye jikin shi kalar royal blue, ya matuƙar yin kyau cikin sanyin shi yake takawa da niyya zuwa ɗaukar motar tashi, ya hango ta tayi hanyar fita waje cikin matsanancin gudu, kuka ma take yi, duk ta cukuikuye hijabin tata kaman mahaukaciya, lelleƙawa nayi banga kowa ba, ga dukkan alamu ma basu baro sashen nasu na maza ba da yake cen gefe guda da namu Amman da tazara sosai, juyowa nayi da gudu zan koma sashen namu wajen umman tawa, kuka nake bil haƙƙi da gaskiya ni a tunani na umman tawa ta mutu ne, karo naci da mutum ba tare da sanin ko wanene ba na shiga jan hannun shi, idona ya kulle, bana ganin kowa bana ganin komai, umma ta kawai nake kira, lokaci guda Naji an kama man hannuwa duka an riƙe aka shiga girgiza ni, "ke ki natsu, natsu nace, ki faɗa man me ya sami umman taki? Tana ina ne?" amon murya shi ta bugi dodon kunne na lokaci guda na wara idanuna akan shi, shi dai ne, Ya Ameen ne riƙe dani ni suhan, yana girgiza ni, hannuwa na duka cikin nashi, duk da firici da halin kuka da damuwa da nake ciki, bai hanani jiyo ƙamshin turaren shi ba da kuma taushin hannuwan nashi da suke cike da wani sanyi mai ratsa zuciya, "umma ta, ba zata mutu ba, Ya Ameen kaje ka duba man ita don Allah, bata numfashi, bansan haka ba da ban mata maganar ba, kada ta mutu ta bar ni ni ɗaya cikin gidan nan bansan kowa ba sai ita duk duniyar nan"
Na faɗa cikin kuka ina mai durƙushe wa kan ƙafafu na, gami da sake sakin wani marayan kuka mai ban tausayi ga mai sauraro, durƙusa wa yayi shima gami da kamo dukkanin damatsan hannuwa na ya miƙar dani "is ok, ya isa hakanan, ba zata mutu ba insha Allah muje in ganta" ikon Allah, maimakon ni da ke jan hannuwan waɗanda nake son su taimaka man, wannan karin wanda yake son taimaka man ɗin ne ya shiga jan hannuwa na, kaman makaho da ɗan jagora haka yake janye da hannuwa na, duk da nasan babu kyau hakan, ina jin babu daɗi a jikina duk kuwa da halin da nake ciki, Amman banyi yunƙurin janye hannun nawa ba, saboda da taimakon shi ne nake tafiya, jikina babu kwari Sam, kukan da nayi ya sanya har wata juwa-juwa nake gani, ƙala bance ba, na shiga bin shi kaman wadda bata san hanyar ba, har muka iso bakin ƙofar ɗakin da yake danƙam da ƴan kallon umma ta, dukkan su ma'aikata ne, Amman babu wadda tayi yunƙurin zuwa kusa da umman tawa ma da take yashe a tsakar ɗakin, duk sun tokare wasu daga ciki, wasu kuma daga bakin ƙofar dakin, wannan ƙiyayya har ina?
To fa! Turƙashi, Alhaji ƙarami ne riƙe da hannuwan Suhana yana janye da ita? Me hakan ke nufi? Ita har ta kai ma tsayin wadda Al'Ameen ɗin zai ruƙo ya shigo da ita har cikin ɗakin ta? Take redio masu amfani da jini suka fara naɗar ƙarya da gaskiya, darewa suka shiga yi suna bashi hanya tare da ƙoƙarin gaidashi, ko kallon inda suke baiyi ba, domin shima sun bashi matuƙar mamaki, sai dai Al'Ameen ɗin ba irin mutanen da ke shiga sabgar da babu ruwan shi bace, hannuwan nawa ya saki yayin da yake kamo na umman tawa yana mai ƙoƙarin jin pulse ɗinta.
Miƙewa yayi tare da maida kallon shi kan mama talatin dake tsaye tana recording ɗin duk wani motsi namu a ɗakin ko babu komai yau Hajiya Babba da labari kenan.
"Mama ku kamo ta a sanya ta a mota muje asibiti, bari in fiddo motar" ya faɗa cikin sanyi halin shi mai cike da miskilanci, maganar ma kaman baya son yi, sannan ya juya inda nake tsaye yana faɗin "Muje" a taƙaice, lokaci guda ya shiga takawa da niyya barin ɗakin.
Har yanzu kuma kuka nake, sai dai sauti kukan ya ragu sai dai kwalla da taƙi ta tsaya, bin shi na shiga yi a baya har zuwa parking lot da yake cike da motoci na alfarma; motar shi da tafi kowacce haɗuwa a wurin ya shiga tare da juyo ta daidai saitin da nake tsaye, sannan ya sanya hannu ta ciki ya buɗe man ƙofar gaba ta mai zaman banza, ganin da yayi ina ƙoƙarin shiga baya, banyi musu ba na shiga na zauna ina mai share kwalla ta akai akai, daidai lokacin da mama Talatu da mama uwani suka kamo umma tawa kaman matatta suka buɗe baya suka sanya ta, ya fita ya gyara masu sannan ya umarci mama Talatu da take shugaba ta shiga mu tafi tare da ita, yayin da mama uwani ta juya zuwa sashen namu tana mai taɓe bakin an mata buƙulun shiga haɗaɗɗiyar motar da take ɗauke hankalin duk wani dake zama sashen masu aikin.
kuka na fashe dashi lokaci guda ina mai ƙanƙame jikina, yanda naga ta hassala kaman zata rufe ni da suka.
"Ashe ke shashasha ce hauwau ban sani ba?, ina tarbiyyar da na baki? Ina kika kaita, nan ɗin da kike ganin ana wulaƙanta mu, ya fiye mana cen, in kika koma kashe ki zasu yi, nace kashe ki zasu yi! Ni ma ba zasu barni ba, saboda ke nake zaune nan, dan ki tsira da mutuncin ki, ki tsira da rayuwarki yasa nake zaune nan, nima abun yana man zafi, Amman ko me zasu yi mana ba zasu iya kashe mu ba, zaki mutu ne muddin kika yarda kika koma cen" kwalla ce ke shata ta a idanun umman tawa, abun da ya ƙara matuƙar firgita ni kenan, rarrafawa na shiga yi ina mai zuwa inda take na rungume ta, ture ni ta shiga yi, jeki, je ki nemi mahaifin ki, ƙila zakiyi sa'ar ganin kabarin nashi, ƙila zai iya tashi ya faɗa maki komai, Hauwa'u ban tsammanin akwai ranar da har ke zaki iya zuwa ki sanya ni a gaba ba, ki titsiye ni sai na faɗa maki wacece ke ba, na ɗauka na gama maki komai, na ɗauka na ishe ki komai, ban tsammanin zaki gaji da zama a inda na zaɓa mana rayuwa ba, nace kashe ki zasu yi, muddin kika yarda suka san kina nan da ranki, jeki jeki ki nemo dangin mahaifin ki, ki nemo dangi na, Amman ni kar ki ƙara tambaya ta game da su, kar kuma ki sake ki dawo inda nake, kuma duk Abunda ya same ku ke ce kika siya da kuɗin ki, kar ki ƙara tambaya ta abunda ya shafe su; Ta shiga ƙara ture ni daga jikin ta tana mai share kwallar da take ta ambaliya a fuskar ta.
Ƙara ƙwaƙume ta nayi, ina mai sakin gunjin kuka lokaci guda ina mai faɗin "Umma kiyi haƙuri ki yafe man, ki gafarce ni umma, nayi maki laifi, na aikata maki ba daidai ba umma, na cutar da zuciyoyinmu umma, bansan haka ba, bansan komai ba umma ki yafe man" shiru naji lokaci daƴa kaman ma bata numfashi, A firgice na ɗago, domin in ga me ke faruwa, abunda idanunwa na suka gani ne ya sani sakin razananiyar ƙara da sai da ta cika ilahirin sashen namu. Jikin ta gaba ɗaya ya saki, kaman wadda ta mutu bata numfashi Sam, "umma ki tashi" na shiga faɗi lokaci ɗaya ina mai jijjiga ta "umma ki tashi don Allah na bari, umma ki yafe man, umma kar ki mutu ki barni don Allah, umma ban da kowa sai ke, ke ce uwa ta ke ce uba na umma, ke ce komai nawa umma, kar ki mutu ki barni a cikin gidan nan umma, zan mutu nima in biki wallahi muddin kika barni, umma basa son mu basa ƙaunarmu, kar ki barni ni ɗaya a cikin gidannan" kuka ne gami da majina suka bi suka haɗe a yalwataciyar fuskar tawa, bama ta su nake yi ba, balle in mai da kai wajen share wa, gunjin kuka na nake yi mai cike da ruɗani kala kala, yayin da umman tawa take sharaf a jikina babu alamar numfashi tattare da ita, kwantar da ita na shiga yi lokaci guda ina mai girgiza kaina "umma ta bazata mutu ta barni nan ni kaɗai ba, bansan kowa ba umma sai ke" haka nake faɗa yayin da na tashi na fice da matsanancin gudu zuwa nemo wanda zai duba man ita, a tsakar gida muka haɗu da sauran ƴan aikin gidan da duk sun jiyo kuka na sun fito hankali tashe, hannun uwani na shiga ja ko sauraren ta banyi ba ina faɗin "mama uwani Kuzo ku duba man umma ta kar kuce man ta mutu, kar kuce man bata da rai, kar ku kashe man ita" mama Talatu Kuzo" na saki hannun mama uwani da nufi mama Talatu da gudu itama na shiga jan ta, ina mai sake sakin kuka mai tsuma rai, "me ya samu maman Suhana ɗin ne wai? " mama uwani take tambaya ta, ban iya bata amsa ba, domin naga sun yi tsaye sun ma ƙi shiga ɗakin, hanyar waje na nufa da gudu cikin kuka ina kwala ma baba idi kira, yazo ya duba ban umman tawa.
Tin daga nesa ya hango ta, Ya Ameen ne da ya fito daga part ɗin nashi cikin shirin zuwa wajen aiki, suit ce sanye jikin shi kalar royal blue, ya matuƙar yin kyau cikin sanyin shi yake takawa da niyya zuwa ɗaukar motar tashi, ya hango ta tayi hanyar fita waje cikin matsanancin gudu, kuka ma take yi, duk ta cukuikuye hijabin tata kaman mahaukaciya, lelleƙawa nayi banga kowa ba, ga dukkan alamu ma basu baro sashen nasu na maza ba da yake cen gefe guda da namu Amman da tazara sosai, juyowa nayi da gudu zan koma sashen namu wajen umman tawa, kuka nake bil haƙƙi da gaskiya ni a tunani na umman tawa ta mutu ne, karo naci da mutum ba tare da sanin ko wanene ba na shiga jan hannun shi, idona ya kulle, bana ganin kowa bana ganin komai, umma ta kawai nake kira, lokaci guda Naji an kama man hannuwa duka an riƙe aka shiga girgiza ni, "ke ki natsu, natsu nace, ki faɗa man me ya sami umman taki? Tana ina ne?" amon murya shi ta bugi dodon kunne na lokaci guda na wara idanuna akan shi, shi dai ne, Ya Ameen ne riƙe dani ni suhan, yana girgiza ni, hannuwa na duka cikin nashi, duk da firici da halin kuka da damuwa da nake ciki, bai hanani jiyo ƙamshin turaren shi ba da kuma taushin hannuwan nashi da suke cike da wani sanyi mai ratsa zuciya, "umma ta, ba zata mutu ba, Ya Ameen kaje ka duba man ita don Allah, bata numfashi, bansan haka ba da ban mata maganar ba, kada ta mutu ta bar ni ni ɗaya cikin gidan nan bansan kowa ba sai ita duk duniyar nan"
Na faɗa cikin kuka ina mai durƙushe wa kan ƙafafu na, gami da sake sakin wani marayan kuka mai ban tausayi ga mai sauraro, durƙusa wa yayi shima gami da kamo dukkanin damatsan hannuwa na ya miƙar dani "is ok, ya isa hakanan, ba zata mutu ba insha Allah muje in ganta" ikon Allah, maimakon ni da ke jan hannuwan waɗanda nake son su taimaka man, wannan karin wanda yake son taimaka man ɗin ne ya shiga jan hannuwa na, kaman makaho da ɗan jagora haka yake janye da hannuwa na, duk da nasan babu kyau hakan, ina jin babu daɗi a jikina duk kuwa da halin da nake ciki, Amman banyi yunƙurin janye hannun nawa ba, saboda da taimakon shi ne nake tafiya, jikina babu kwari Sam, kukan da nayi ya sanya har wata juwa-juwa nake gani, ƙala bance ba, na shiga bin shi kaman wadda bata san hanyar ba, har muka iso bakin ƙofar ɗakin da yake danƙam da ƴan kallon umma ta, dukkan su ma'aikata ne, Amman babu wadda tayi yunƙurin zuwa kusa da umman tawa ma da take yashe a tsakar ɗakin, duk sun tokare wasu daga ciki, wasu kuma daga bakin ƙofar dakin, wannan ƙiyayya har ina?
To fa! Turƙashi, Alhaji ƙarami ne riƙe da hannuwan Suhana yana janye da ita? Me hakan ke nufi? Ita har ta kai ma tsayin wadda Al'Ameen ɗin zai ruƙo ya shigo da ita har cikin ɗakin ta? Take redio masu amfani da jini suka fara naɗar ƙarya da gaskiya, darewa suka shiga yi suna bashi hanya tare da ƙoƙarin gaidashi, ko kallon inda suke baiyi ba, domin shima sun bashi matuƙar mamaki, sai dai Al'Ameen ɗin ba irin mutanen da ke shiga sabgar da babu ruwan shi bace, hannuwan nawa ya saki yayin da yake kamo na umman tawa yana mai ƙoƙarin jin pulse ɗinta.
Miƙewa yayi tare da maida kallon shi kan mama talatin dake tsaye tana recording ɗin duk wani motsi namu a ɗakin ko babu komai yau Hajiya Babba da labari kenan.
"Mama ku kamo ta a sanya ta a mota muje asibiti, bari in fiddo motar" ya faɗa cikin sanyi halin shi mai cike da miskilanci, maganar ma kaman baya son yi, sannan ya juya inda nake tsaye yana faɗin "Muje" a taƙaice, lokaci guda ya shiga takawa da niyya barin ɗakin.
Har yanzu kuma kuka nake, sai dai sauti kukan ya ragu sai dai kwalla da taƙi ta tsaya, bin shi na shiga yi a baya har zuwa parking lot da yake cike da motoci na alfarma; motar shi da tafi kowacce haɗuwa a wurin ya shiga tare da juyo ta daidai saitin da nake tsaye, sannan ya sanya hannu ta ciki ya buɗe man ƙofar gaba ta mai zaman banza, ganin da yayi ina ƙoƙarin shiga baya, banyi musu ba na shiga na zauna ina mai share kwalla ta akai akai, daidai lokacin da mama Talatu da mama uwani suka kamo umma tawa kaman matatta suka buɗe baya suka sanya ta, ya fita ya gyara masu sannan ya umarci mama Talatu da take shugaba ta shiga mu tafi tare da ita, yayin da mama uwani ta juya zuwa sashen namu tana mai taɓe bakin an mata buƙulun shiga haɗaɗɗiyar motar da take ɗauke hankalin duk wani dake zama sashen masu aikin.