← Book details Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 56

Sashe 20

Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Amsa yayi yana dubawa, mamaki fal a ranshi na yanda yarinyar take da ƙoƙari, gashi dai makarantar masu hannu da shuni tayi, saboda Alhaji Mustapha ne ya sanya ta a makarantar har ta gama, kafin abubuwa sukayi mashi yawa ya tafi wani aiki ƙasar Indiya daidai lokacin da Jarabawa tasu ta fito wannan shine ya sanya ya shafa'a da karatun yarinyar koda ya dawo kunsan mnyan mutane, ita kuma Hajiya Kubran bata tina mashi ba, a cewar ta hakan ma ya isa, wa yace ƴaƴan masu aiki na makarantar jami'a (🤔🤨😏 ke kika hana ko Hajiya Kubra)

Takaddu sunyi kyau ya shiga faɗi da ɗan murmushi shi irin na miskilai, kai kace ma bai yi ba, sannan ya miƙe dasu a hannun shi yana mai cewa za'a siya jamb sai in cike tare da course ɗin da nake so, in naga ban iya ba sai in same shi ya koya man (kun ji ba Bigboo, ko ya manta da halin gidan nasu ne?) da to muka bishi da umman tawa, kuɗi ya ajiye kusa da umman tawa masu ɗan dama yana faɗin ko zata buƙaci wani abu, sannan ya ƙara jaddada mata kar taci Abunda likita ya hana, idan muna nuƙatar wani abu muyi mashi magana.

Umman tawa ce ta shiga faɗin lallai ba zata amshi waɗannan kuɗi ba, cikin girmamawa ya shiga bata haƙuri da faɗin duk abin da yayi mana haƙƙinshi ne da yayi mana, wannan ba wani abun damuwa bane, duk ma in muna buƙatar wani abu mu tuntuɓe shi a shirye yake da ya taimaka mana.

Godiya ta shiga ƙara jera mashi da yabanma dukkan in hidima da yayi damu ɗin "ba komai umma, Allah ya ƙara sauƙi" ya faɗa yana mai taka wa ya bar ɗakin riƙe da Takaddu na a hannun shi.

Oh Allah🙏🏻 Ashe zanyi karatu a rayuwa ta? Ashe Ya Ameen na magana haka? Yanda naga ya zage suna ta fira da umma ta, kuma duk wata kalma da zai faɗa cikin taka tsantsan da girmamawa yake yin ta kaman yana magana da Hajiya kubra, murmushi na shiga saki akai akai, ina mai sauke ajiyar zuciya, mafarki a ya kusa tabbata, jikina na bani mun kusa fita daga cikin halin ƙuncin da muke ciki ni da umma ta, daga na gama karatu na samu aiki zan gina mana gida, na ɗauke umman tawa muje cen muyi Rayuwar mu, muma muci gashin kanku, mu rabu da takura da jaraba Hajiya kubra, Allah na gode maka, Allah ka saka ma wannan bawa da
Alkhairi a rayuwar shi, ka haɗa ci da mata ta gari, da zata kula dashi, kuma tayi haƙuri da halin hajiya Kubran.

"Tashi ki naÉ—e dadduman in kin gama murnar" u mata ta faÉ—a cikin murmusawa da ke nuna sallar jin daÉ—in ta, da farin cikin ta.

Yunƙurawa nayi ina mai da rawa a fili na shiga faɗin "umma ai dole inyi murna kin gama man komai, Allah ya cika mana burin mu, ashe da rabon zan yi karatu nima in samu ilimi kaman yanda kowa ke samu?"

Murmusawa tayi tana mai kishingiɗawa tare da faɗin "Ai wannan yaro ɗan albarka ne, Allah dai ya bamu ikon saka mashi da alkhairi kaman yanda yake mana shi da mahaifin shi, ki kauda kuɗin nan ki maida hankali ki ci abinci" da to na bita ina faɗin "ni wallahi ummana tsabar murna ma yasa naji na ƙoshi"

"ki dai maida hankali" umman tawa ta bani amsa tana mai lumshe idanun ta murmushi fal a fuskar ta.

Ta ɓangare guda kuwa Al'ameen ɗin na fita wayar Mom ɗin nashi na na shigowa, tare da umartar shi da cewa ko me yake ya tabbatas ya biyo jirgin yamma ya isa Katsina tana son ganin shi, shi kin mamaki ya shiga tambayar ta ko lafiya? "Lafiya lau" ta bashi amsa tana mai datse kiran, Layin Afnan ya nema gami da tambayar ta, ta faɗa mashi kawai dai taga an kira ta ne daga gidan Amman bata san ko wanene ba, kuma daga gani gulma aka kawo mata, "is OK" ya faɗa yana mai katse kiran ganin kiran babban Abokin nashi da zai kawo mashi ziyara yau ta shigo wayar shi.

Amsawa yayi cikin son kauda zargin komai daga ranshi, bayan sun gaisa ne yake faÉ—a mashi ya iso gashi a airport, cewa yayi ya jira shi yana zuwa É—aukar shi.

Ko da ya isa ya tadda abokin nashi yana jiran shi, cikin son juna da tsantsar farin ciki suka rungume juna suna mai mararin juna da tsantsar ƙauna ga aminan guda biyu, basu bar airport ɗin ba sai da ya yanka masu ticket guda biyu tare da kallon Bilal ɗin ya shiga faɗin "yaro yau ƙauye zaka kwana, ka taddani tafiya ta gaugawa ta taso mani" cikin murmushi Bilal ɗin ya kai mashi ɗan ƙarami duka a damtsen hannu yana mai cewa "To ya zanyi Friend" ai ko ruga ka kai ni dole in kwanta, ya zanyi tinda na riga nazo?"

Cikin walwala da jin daɗi suka bari airport ɗin direct gida ya wuce dashi domin yaje yayi wanka ya huta kafin lokacin sallar azahar ta ƙarasa.

~Oum-Deedat ce~
[8/5, 8:24 PM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺

*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._

_*Page ~13~*_

_To Readers_ --- *Abun da kuka ji da zai amfane ku ku ɗauka, wanda kuka ji akwai kuskure ciki, kuyi watsi dashi, mu ba muji wahalar zaunawa muyi amfani da idear ɗinmu ba mu rubuta maku labarin da zai amfane mu ba baki ɗaya ba, sai ku da zakuyi comment ƙarƙarinta layi biyu zuwa uku, shine zai ke maku wahala, Anya kuwa readers kuna kyautawa🤔? Muna maraba da gyara ko ƙorafi, Amman ba ta hanyar zagi, ko cin zarafi ba, kuskure kowa nayi indai kai ɗan adam ne, kuma ajizi, so saboda haka muna shawartar ku da ku dinga ƙarfafa mana guiwa, wadda kuma taga labarin baiyi mata ba, toh ta bar mana abunmu ba sai ta karanta ba, bamu sanya kowa dole ba, imfact ma babu dole sai rai yaso a rayuwa. fans muna godiya da irin supporting ɗin da kuke bamu 💓muna yinku over, Allah ya bar ƙauna, wannan saƙo ne daga ƴan ƙungiyar ~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION~*

°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°

Fira sosai suka shiga yi da aminin nashi da bashi da kamar shi, kaman ba Ya Ameen ɗin da kuka sani ba, har yana zaulayar abokin nashi, akan zancen bikin nashi da za'ayi watanni ƙalilan masu zuwa inda anan Abuja zai auri yarinyar ya tafi da ita cen.

Sai da sukayi wanka suka shirya tsaf sannan suka wuce wani eatery mai bala'i kyau da tsada suka ci abinci sannan suka koma gida domin ƙara hutawa.

Al'ameen ɗin ba mai yawan yawo bane indai yana ƙasa, yafi ganewa ya zauna a gida a part ɗin nashi yayi aiki.

Yanzu ma hakan ce ta faru, yayin da ya jawo laptop ɗinshi ya shiga aiki, wannan ce ta sanya Bilal ɗin fahimtar cewa ƴan maganar sun bar kan aminin nashi, to ko wacce magana zai yi mashi fa zai yi mashi shiru ne, har sai lokacin da yaso tankawar kuma baya maido da zancen da ya riga ya wuce, wannan ɗabi'ar shi ce tin yana ƙarami, balle yanzu da ya girma.

Kwanciya Bilal ɗin yayi domin yana jin baccin gajiya gashi ya ƙoshi har wani lumshe ido yake yi.

Bilal ɗan gayu ne na ƙarshe, yana da hankali da tunani sosai duk da kasancewar shi cikin jajayen fata, hakan bai canza halin shi da mu'amala shi ba, wannan ce ta sanya abotar su da Al'ameen ɗin da take tin ta yarinta take daɗa ƙarko har kwanan zancen.

Aikin shi yake yi cikin salo da kwarewa yake sarrafa kwamfuta, kaman dama cen shi ne ya ƙera ta, to ai dama karatun shi kenan kada ku manta.

Kiran salla ne ya farkar da Bilal ɗin yayin da Al'ameen ɗin har ya ɗauro tashi alwalar, bayan Bilal yayo ne suka nufi masallacin da yake gefe ta jikin ɓari ɗaya na gidan nasu.

Ƙarfe biyar daidai sukayi shirin barin garin, yayin da Al'ameen ɗin ya tara dukkanin ma'aikatan gidan domin bar masu jan kunne tinda za'a bar gidan ba kowa sai mu kaɗai.

Ni da umma ta ce kawai bama wurin, ja masu kunne yayi sosai akan su kula da komai, Bilal É—in na tsaye gefen shi yana ta murmusawa domin ya san abokin nashi kwarai da rashin son wargi, gashi dai ya iya mu'amala da ma'aikata dama cen, sai dai shi mutum ne mai son taka tsantsan da kula.

Bayan ya gama dasu ne, ya nemi Bilal ɗin da ya raka shi ɗakin namu domin ƙara duba jikin umman tawa.

Kwarai Bilal ɗin yayi mamakin ina yake nufa haka da yake ta ratsa sashen ma'aikata haka, sai dai bai ce mashi komai ba ya cigaba da bin shi a baya har zuwa bakin ƙofar ɗakin namu da yake tsaf a share tas,

Sallama sukayi, yayin da umman tawa ta basu izinin shiga, kai tsaye suka cusa kansu cikin É—akin namu da babu wadatar abubuwa.

Miƙewa nayi ga barin karanta littafin *Jinnul Ashique* (na Harira ƴar fillo) domin littafin ya tafi da hankali na akwai tsantsar soyayya da abun al'ajabi da ban mamaki cikin shi, ina ma nima zan samu wanda zai gwada man irin wannan soyayya haka? (zaku iya neman shi ku karanta, zaku same shi online)

Darduma mai ɗan girma na shimfiɗa masu lokacin da nake ficewa a ɗakin, Sam bazan lamunci zama na wuri ɗaya dashi ba, ƙamshin shi, idanun shi, ba ƙarami makami bane da kan taimaka wajen ruɗewa ta ba.
Chapter 20 · 0% Book details