← Book details Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 56

Sashe 18

Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yayi Alƙawarin taimaka ma Suhan ɗin domin jin ta yake kaman Afnan ɗinshi, da ƙaunar da Afnan ɗin ke mata da sanyi halin ta da kuma tarbiyyar da ta samu daga wajen umman tata, sai kuma halin da suke ciki da musguna masu da Mahaifiyar tashi ke yi, su suka ƙara mashi ƙaimi wajen ganin son ya taimaka masu bil haƙƙi da gaskiya, baya jin wani abu dangane da Suhan ɗin illa wani narkon tausayinta da ke malala cikin zuciyar shi, yarinya da ita, ba tafi shekara ishirin ba Amman tana fuskantar wannan waƙi'ar, wannan halin da suke ciki kan ƙara jefa zuciyoyin su a damuwa da shi kuma baya jin zai iya lamunta.

A haka ya samu bacci ɓarawo ya sace shi, zuciyar shi fal da tinanin halin da umman ta Suhan ɗin take ciki.

~Oum-Deedat ce~
[8/5, 8:24 PM] Aminatu Hassan: https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

🌹*BAN FI ƘARFIN TA BA* 🌹

🌺🌺🌺🌺🌺

*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*
*~we write assidiously perceive no pain~.*
*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*
*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>>

*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_

*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_

*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._

*Page ~12~*

°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°

Washe gari kuwa tin da safe kowa ya shirya a gidan, wannan umarnin Alhaji Mustapha ne domin yana so su isa da wuri domin ticket ɗin safe aka samu, aika Afnan yayi tayi kiran Ya Ameen ɗin da shi kaɗai ake jira bai fito ba, sai gashi kuma cikin takun shi na ƙasaita da sanyin shi da kan ƙara mashi kwarjini a fuskar jama'a

Sanye yake cikin wani lallausan yadi kalar sky blue, an mashi ɗinki Abuja style, da gani dai yana son ɗinkin, rigar iya rabin cinya ta tsaya bata kai guiwa ba, hakan ya ƙara fiddo da asalin kyawon halittar da Allah yayi mashi, kan shi babu hula sai dai gyaran fuskan da kan ƙara ƙawata fuskar tashi. Takalmin shi da hankachip ɗin da ke hannun sau ciki, shi duk kalar kayan ne sai zuba ƙamshi yake yi. Cikin ɗan sassarfa ya isa ga Lahajin dake tsaye da alama jiran shi yake yi ya fito.

Gaida dad ɗin nashi ya shiga yi cikin girmamawa, yayin da Alhajin ya miƙa mashi hannu don suyi musabaha, na daga cikin halin Alhajin ne sauƙin hali da sauƙin kai, hakan kan ƙara mashi shaƙuwa da ƴaƴan nashi fiye ma da mom ɗin tasu.

Matsawa yayi ga Hajiya Kubran da fitowar ta kenan cikin shigar wani ɗanyen boyel mai taushi da walƙiya, ɗan rungumo ta yayi cikin murmushi mai ƙara ƙayata kyakkyawar fuskar tashi, amsa gaisuwar tashi ta shiga yi cikin jin daɗi da ƙauna ga ɗanɗan nata, duk da bata manta ƙin yarda da maganar tata da yayi da a daren jiya, Amman ta bar ma zuciyar ta, ta kuma sha Alwashin ganin zargin ta da hasashen nata bai zama gaskiya ba.

Sauran ƙannen nashi suka shiga gaida shi yayin da ya duka yana ma Nasreem wasa da miƙa ma Ayan hannu sukayi musabaha yana mai gaida yayar tashi cikin sakin fuskan da sai yana cikin family ɗinshi ne kawai zaka ganta.

Shafo kanshi tayi tana faɗin "Brother fatan ka tashi lafiya" ta faɗa cikin murmushi da kan ƙara nuna tsantsar ƙaunar ta ga ƙanen nata.

Alhaji Mustapha ne ya kauda masu gaisuwar da suke yi cikin cewa "Al ameen ina ganin ya kamata mu zo mu wuce ko kasan da ƙarfe 08:00am ne lokacin tashin flight ɗin. ɗan sosa kan shi ya shiga yi da ɗan makullin motar shi da ke hannun shi sannan ya shiga faɗin" Dad ina ganin ni ba zan biku ba sai dai ko zuwa gobe ko jibi ne zan iske ku cen ɗin, saboda aikin construction ɗin nan naga yana neman tsayawa, Eng ɗin ne naga yana san sanya shiririta dan yaga na cika mashi cikon kuɗin shi, and Bilal ma yace man yau zai iso ina jin ma sun taso yanzu, Ga kaya da kamfani zai fitar yau ina so inje ayi komai gabana, kasan yanzu rashin gaskiya ta yawaita" ɗan murmusawa Alhajin nashi yayi, sarai ya fahimci Ya Ameen ɗin baya son bin nasu ne, May be dan yana gudun maganar da Hajiyar tasu ta taso ita ne jiya, tana iya zuwa ta zuga Granny Zuwaira akan zancen; ɗan ƙara murmusawa yayi yana faɗin " is ok Al ameen Amman wanne kamfani ne zai fidda kaya yau?" (Domin Al'ameen ɗin shine manager ɗin duka kamfanonin Alhajin duk da shima yana da nashi) "Eh sabon na costimetics ɗin nan ne" Ya shiga faɗi da ɗan guntun murmushi akan fuskar shi yana mai son Alhajin nasu ya yarda da uziri nashi, "Tau ba matsala for now, Amman dai ina fatan zaka je cen ɗin cikin lokaci, Kaga ka kwana biyu ba kaje ba, duk da kuna waya, ya kamata kaje kaima Kaga lafiyar kakannin naka"

"to Dad" ya bashi amsa yana mai buɗe mashi gidan baya ya shiga ya zagaya ya buɗe ma Mom ɗin tasu, da bata ƙara tankawa ba don duk ya tushe mata plan ɗin nata, amman ba komai, ai bata ma jin sai tayi kamun ƙafa da wani akan al'amari yaron nata, duk isar ta da dukiya ta, ita ta haife shi in ya san wata ai bai san wata ba;

Mota biyu sukayi É—aya Alhaji Mustapha da Hajiya kubra sai driver kawai, sai kuma É—ayar da ta É—auke Aunty feena da yaran nata sai Saudat, Nihal da kuma Abie da ya hakimce a gaba.

Kai tsaye motar shi ya nufa, bayan yaga ficewa mitocin daga cikin harabar gidan nasu, restaurant ya fara tsayawa ya siya abun break fast sannan ya wuce Asibiti da ya kwana tinanin su duk da son kauda tinanin nasu da yake yi daga cikin ran shi, sai dai baya iyawa, sau da dama shi karan kanshi kan shiga tinanin kan shi da kanshi, tabbas ya san yana tausayin na ƙasa dashi, da marasa galihu, da ƴan aikin nasu, tau sai dai yana mamakin kan nashi, su salon yanda yake tausaya masu ma daban ne, amman ya kan alaƙanta hakan ne da rashin lafiya da take damun Maman Suhan ɗin.

Sallama yayi daga bakin ƙofa, tsam na tashi daga kan kujerar da nake duƙunƙune tin bayan da na gama sallar asubahin na kuma komawa na kwanta domin in ɗan rutsa, don cikin dare umman tawa ta farka, cikin ƙarfin hali irin nata har fira muka ɗan taɓa tana kara jaddada man maganar karatun nawa, da kuma roƙo na akan in bama dukkan Abunda zan gani a rayuwa ta ta gaba baya.

Daga ciki na buÉ—e mashi, ina mai janyewa na bashi hanya domin ya wuce. Kai tsaye ya shiga har bakin gadon umman tawa, yana mai ajiye manyan ledojin take away da yayo mana; É—an rankwafawa yayi daidai saitin gadon umman tawa, yana mai kallon bugawar lumfashin ta.

"ta samu bacci ne?" ya jefo man tambaya yana mai janyo kujerar gefen gadon ya zauna idon shi cikin nawa, "Eh ta samu bacci, Amman ta farka cikin dare jikin da sauƙi, don har ma fira mun yi" na faɗa ina mai ƙoƙarin janye nawa idanu, tinani na ke yi, shi wanne irin mutum ne? Mutum mai daraja irin ta Ya Ameen da ba ko domin arziƙi shi ba da na iyayen shi, shi mutum ne daban ko cikin matasan garin na Abuja akeji dashi, shine yake bamu kulawa haka? Gaskiya ya cencenci a yaɓa mashi, ya cencenci a girmama shi, da dukkan iyawa.

"Hop dai bata wahalar da kanta ba wajen magana? Kin dai san dokar likita, ki dinga kula" ya faɗa yana mai kauda idanu shi daga gare ni da har yanzu nake rakuɓe daga bakin ƙofa, kwarjini shi baya bari in sake a duk lokacin da nake gaban shi.

"To zan kula insha Allah" na faɗa a hankali iya fatar baki, miƙewa yayi cikin halin ko in kula da tsayuwar da nake tayi, sannan ya shiga faɗin "Dictor ya shigo?" Lokacin da ya shiga ta kowa a hankali zuwa ga bakin ƙofar domin ficewa, amsar da na shiga bashi ce ta sanya shi ja ya tsaya ga barin ficewa, hakan ce ta sanya muke tsaye gaf da gaf, duƙar da kaina na shiga yi, bazan iya jurar haɗa idanu nashi ba, idan ma zan kula da jikina wata ƴar kyarma nake yi a hankali, me ke damuna ne ni Suhana? "Bai shigo ba yaya, Amman Nurse ta shigo sannan tace idan ta farka a bata abinci mai sauƙin nauyi, sannan mu kira ta, in kuma likita shigo shikenan" "Is OK Let Me Check On Him" Ya faɗa cikin salon turanci shi da yake kama da na turawan amurka da nake kallo a Tb ɗin babban falon gidan, ficewa yayi cikin salon tafiyar shi ta jarumin namiji, idan yaso komai cikin zafi zafi yake yin shi, idan kuma yaso kai kace wahainiya ce ke tafiya masalan ma idan yana jin ƴan miskilancin.

Office ɗin likatan ya shiga yayi daidai da isowar shi kenan Dr Ashafa ne yayi azamar miƙa mashi hannu yana faɗin "Yallaɓai ba dai har ka shigo ba? Gaskiya waɗannan patient ana ji dasu, Fatan dai jikin na maman tamu da sauƙi? Ya faɗa cikin murmushi da san ɓoye wani abu acikin ran shi;" Zamu iya zuwa ka duba Dr saboda ina so idan jikin nata ya samu sauƙi kayi discharge nasu, zanyi tafiya ne kuma bana son barin su anan babu mai kula dasu, gara su koma gida" ya maida ma da likita amsa cikin ɗan ɗaure fuska, bai san me Dr ɗin ke nufi ba, Amman ya kula tin jiya da yanda yake kallon Yarinya da take ta fama da jinya mahaifiya tata, ko menene ma nashi na damuwa? "OK to shikenan muje rana ya daɗe" likita ya faɗa yana mai ɗan sanya shakku a ranshi, Amman dai koma minene ai zai fahimta, gaba Al'ameen ɗin yayi Dr Ashafa ɗin yana biyo shi a baya tare da kayan aikin su na likitoci
Chapter 18 · 0% Book details