Sashe 14
Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da yake da tazara sosai tsakanin sashen nata da na Alhaji, lokacin da ta isa har Al'ameen ɗin ya kira Alhajin ta iske yana waya da Al'ameen ɗin ta nemi waje kusa dashi ta zauna, tana ta cika da batsewa, bayan ya gama wayar ne ya maida hankali shi kan Hajiya Kubran, da murmushi ɗauke kan fuskar shi ya shiga faɗin "uwargida ran gida, lafiya dai ko naga kin dawo, wannan kwalliya ai sai dai ace in biya" ya faɗa cikin zaulaya da murmushi a kan fuskar shi. Fuska a tamke take cewa "Alhaji ba wannan ba, yaron nan Al'ameen...." Dakatar da ita yayi ta hanyar ɗaga mata hannu gami da cewa "Abunda Al'ameen ɗin yayi shine daidai, ai suma mutane ne, ko kuma zai ƙyale ta ta mutu ne cikin gida yana kallo? Mutane su samu abun faɗa a gari? Kada in kuma jin kince komai akan zancen nan kuma anjima ku shirya ku duka muje a dubo ta, Allah ya bata lafiya shine fatan mu. Sannan ina so ki sanya a nemo maki wasu ƴan aikin da zasu zauna mamadin su, abarsu su huta hakanan ita yarinyar ta kula da mahaifiyarta." Yana zuwa nan a zancen ya miƙe gami da gyara zaman babbar rigar shi yana mai kallon ta sannan ya cigaba da cewa" Ni zan fita sai na dawo, kada ku manta ku shirya fa, sannan idan Allah ya kai mu gobe Asabar mu dukkan mu zamu je kankiya mu gaishe da su Alhaji tinda kowa yana ƙasar ki faɗa ma yaran ma su duka su shirya" da kallo ta bishi har ya fice, ita kanta ba tin yanzu ba ta san Alhajin kaifi ɗaya ne, dukkan isar ta da zartar da hukuncin ta, tana yi ne akan ƴaƴan ta kawai da masu aikin gidan sai kuma abokan kasuwancin ta. Amman Alhajin gagarabadau ne a wajen ta, duk abin da take taƙama dashi ya fita shi tsayayye namiji ne a cikin gidan sa, dukkanin hukuncin da ya yanke ya yanku kenan, ba shan ruwa ba ƙetare hanya.
******
Ƙarfe biyu Al'ameen ɗin ya koma gida bayan salla juma'a gami da yin wanka ya shirya, Afnan ya kira a waya ya sheda mata ta fito su tafi, aikau ta saɓo Nasreem ta kamo hannun Ayan, Afnan kenan sarkin ƴaƴa, ko MOM ɗin tasu bata faɗa mawa ba don ta san hana ta zata yi, biyawa suka fara yi, suka yi take away da sauran tarkace, sannan suka wuce asibitin kai tsaye.
A ɗakin suka taddani zaune bisa kujera, na kifa kaina jikin gadon umman tawa da har yanzu bata farfaɗo ba, ban ma ko ji ƙarar buɗe ƙofar tasu ba, na yi zurfi cikin tunani, ƙamshin turaren shi ya sanya ni sauri ɗagowa, ilai kuwa su ne shi da afnan, sanye yake cikin dakakkiyar shadda fara ƙal, yau juma'a tu babbar rana, fuskar nan tashi fayau, idanun shi tarwai cikin farin glass ɗinshi mai kama da medical glass, idanun shi ƙyam a kaina, kallo yake man mai cike da ma'anoni da tuhume tuhume, tabbas na san laifi na, take away ɗin da ya sanya aka kawo man, tin bayan fitar shi da safe, yana ajiye bisa stool ɗin ɗakin ko taɓa shi ma banyi ba har gashi yanzu Ƙarfe uku saura; ba'a magana da ƙarfi ya sanya bai ce an komai ba, sai ma ɗan ƙutawa da yayi ya ajiye sauran ledojin da suke hannun shi ya fice gaba ɗaya a ɗakin.
Gaisawa muka yi da afnan sosai kaman babu abin da ya faru, na shiga tambayarta sauran mutanen gidan, "suna gaida ki da mai jiki" ta furta ba dan taji daɗin ƙaryar da ta furta ba. Hannun Ayan na kamo ina cewa "zo mana Ayan in ba faɗa mi ya kawo gaba?" cikin ƙarfin hali har da ɗan murmushi na na yaƙe. Text ne ya shigo wayar afnan, Ya Ameen ne yake cewa lallai ta sanya ni inci abinci, shi ya wuce sai anjima zai dawo kuma lallai kar suyi hayaniya a ɗakin nan su tada umman tawa.
_Kuyi manage da wannan please bana É—an jin daÉ—i ne ku taya ni da addu'a fans_
~Oum-Deedat ce~
[8/5, 8:23 PM] Aminatu Hassan: 🌹 *_BAN FI ƙARFINTA BA_*🌹
🌺🌺🌺🌺🌺
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~âœðŸ½âœðŸ½GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATIONâœðŸ½âœðŸ½~*
*~â„We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u nopainâœðŸ½~*
*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_
*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_
*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._
🤸ðŸ»â€â™€ðŸ’ƒðŸ»ðŸ’ƒðŸ» Kuzo ku taya É—an ku Deedat murnar cika shekara uku cif a duniya, ina fatan Allah ya Albarkaci Rayuwar shi, ya shirya shi shirin addinin islam, ya bashi rayuwa mai Albarka, ya bashi ilimi mai yawa mai amfani, ya cika mashi burin shi na zama Soja😄😆 ya bamu ikon tarbiyyantar dashi. AMEEN ya Rab, Deedat yana gaida dukkan fans na *BAN FI ƘARFIN TA BA*
_*Page ~9~*_
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
Mu kau cikin ni da umma ta, babu wanda yayi runtsawar kirki, kowa da abunda yake saƙawa cikin rai, har gara ma umman tawa, tana ƙoƙarin ganin ta kau da komai, sabo da shawarwarin likita da ya bata na tayi ƙoƙarin ganin bata riƙe abun ɓacin rai a zuciyar ta ba.
Ni kuwa Allah Allah nake gari ya waye, domin na yanke shawarar ƙundunbalan tambayan umman tawa ainihin labarin mu, da asalin mu, lokaci yayi da zata dena ɓoye mani komai, na mallaki hankalin kaina, yaci ace ta fito ta fayyace mana komai kowa ya sani, ko zata fita a zargin da mafi yawancin ƴan gidan ke mana, a kan kunnen mu mun sha jin ma wasu ƴan ƙanana maganganu akan umman tawa da ni kaina ma, kai wasu ma cewa suke yi ni shegiya ce bana da uba, tinda haka suka ganta tazo gidan a wahale ga ɗiya duƙu-duƙu kuma taƙi faɗin wacece ita da kuma ainahin daga ina take.
Alhaji Mustapha kuma ya kafa dokar kada wanda ya tambaye ta, har sai ta gaji dan kanta ta faɗa, a cewarshi babu kyau shiga rayuwar wani, kuma hakan zai tada mata tsohon mikin dake ranta, gida dai nashi ne, tau tinda haka ne ya bata izinin zama har iya lokacin da take so, kuma tinda aiki tazo nema a zaɓa mata marar wahala a bata har sai ta murmure.
Ciwon umman tawa ya so ya tashi cikin dare, amman cikin ikon Allah abun ya taƙaita, ban so ace zan tada mata maganar da safe ba, gudun sake faruwar tashin ciwon nata, tau sai dai babu yanda na iya, wannan karon haƙuri na da kawaici na yazo ƙarshe, ba zan iya jurar ganin irin wannan rashin mutuncin ba daga wajen Hajiya kubran; da haka na samu bacci ya ɗan figeni har zuwa asubar farko da kiran sallah ya tashe ni.
*******************************
Ya Ameen yana shiga ɗaki waya yasa ya kira Afnan ɗin domin sheda mata yanda sukayi da Dad ɗin nasu, "Hello yaya" ta furta daga cen ɓangaren cikin muryar bacci "My Lil bacci kike yi ne?" ya tambaye ta cikin muryarshi mai daɗin sauraro a hankali, "eh Yaya na kwanta, lafiya dai ko? Ko wani abu kake buƙata? Ta tambaye shi tana mai tashi zaune da ƙara gyara ma Ayan dake gefen ta kwance bisa gadon nata lulluɓinshi," No Lil, ina dai son faɗa maki ne munyi magana da dad ne akan maganar waccen yarinyar, Amman tinda kin fara barci mu bari zuwa safe ki same ni part ɗina kinji, Good night dear" ya faɗa yana mai datse kiran ƙit, domin ya san halin zumuɗinta yanzu tana iya cewa ta taso ta taho, shi kuma baya jin ma zai iya doguwar magana yanzu ya gaji so yake ya kwanta, yana da muhimman ayyukan da zai aiwatar gobe, murmushi ya saki na gefen baki, wanda yayi sanadiyyar ƙara ƙawata fuskar tashi cikin hasken ƙwai mai launin dark blue na dare dake falon.
Miƙewa yayi cikin salon tafiyar shi mai cike da aji, ya shiga bedroom ɗin nashi domin yin shirin bacci, kayanshi kawai ya cire ya faɗa toilet ɗin da baya gajiya da shaƙar daddaɗan ƙamshin da suhan ɗin ta sanya mashi har kawo yanzu.
-------------------
Bayan mun kammala komai na Al'adar mu, kama daga sallah, wanka, sai muka zauna karatu ni da umman tawa, muna gamawa ne naga umman na ƙoƙarin tashi na dakatar da ita ina faɗin
"Umma ina so zamuyi wata magana dake don Allah" na faɗa ina mai rufe littafin umdatul-Ahkam ɗin gami da maida shi ma'ajiyar shi, na sake muskutawa domin girman maganar, ba zan ɓoye ba zuciya ta kaman tayo tsalle ta fito nake ji ta ƙirjina, masalan ma da naga irin kallon da umman tawa ke bina dashi, mai cike da ma'anoni daban daban,
komawa tayi ta zauna domin saurarar ɗiyar tata, da kanta yake duƙe kaman tayi ma sarki ƙarya, "Ehn ina jinki mamana, sauri nake yi domin kinga lokaci ya fara ja.
Sake sunkuyar da kai nayi ina mai komawa kalar tausayi maganar tayi ma baki na nauyi, shahada nayi lokaci guda na shiga faÉ—in
"Umma ki duba girman Allah ki faɗa mani asalin mu, wanene mahaifina? ina ne asalin garin mu, umma ke kanki su wanene mahaifan ki? Umma kin fi so mu zauna a gidan da ba'a san darajar mu ba? Kin fi so mu zauna ana wulaƙanta mu, ana zargin ki, ni kuma ana sheganta ni? Kada zuciya ta tafara yadda da maganar su fa!, na bani da asali, bani da mahaifi umma! Umma su nan ɗin ba dangin mu bane, basu san zafin mu ba, ƴaƴan su ma basa so su raɓe mu, suna kyamatar mu, suna ganin sun fimu umma, bazan iya jurar aci maki fuska a gabana ba, saboda kina ɓoye mana wani abu, kinƙi ki fito ki faɗa ma kowa mu ɗin su wanene ciki kuwa harda ni...... "
******
Ƙarfe biyu Al'ameen ɗin ya koma gida bayan salla juma'a gami da yin wanka ya shirya, Afnan ya kira a waya ya sheda mata ta fito su tafi, aikau ta saɓo Nasreem ta kamo hannun Ayan, Afnan kenan sarkin ƴaƴa, ko MOM ɗin tasu bata faɗa mawa ba don ta san hana ta zata yi, biyawa suka fara yi, suka yi take away da sauran tarkace, sannan suka wuce asibitin kai tsaye.
A ɗakin suka taddani zaune bisa kujera, na kifa kaina jikin gadon umman tawa da har yanzu bata farfaɗo ba, ban ma ko ji ƙarar buɗe ƙofar tasu ba, na yi zurfi cikin tunani, ƙamshin turaren shi ya sanya ni sauri ɗagowa, ilai kuwa su ne shi da afnan, sanye yake cikin dakakkiyar shadda fara ƙal, yau juma'a tu babbar rana, fuskar nan tashi fayau, idanun shi tarwai cikin farin glass ɗinshi mai kama da medical glass, idanun shi ƙyam a kaina, kallo yake man mai cike da ma'anoni da tuhume tuhume, tabbas na san laifi na, take away ɗin da ya sanya aka kawo man, tin bayan fitar shi da safe, yana ajiye bisa stool ɗin ɗakin ko taɓa shi ma banyi ba har gashi yanzu Ƙarfe uku saura; ba'a magana da ƙarfi ya sanya bai ce an komai ba, sai ma ɗan ƙutawa da yayi ya ajiye sauran ledojin da suke hannun shi ya fice gaba ɗaya a ɗakin.
Gaisawa muka yi da afnan sosai kaman babu abin da ya faru, na shiga tambayarta sauran mutanen gidan, "suna gaida ki da mai jiki" ta furta ba dan taji daɗin ƙaryar da ta furta ba. Hannun Ayan na kamo ina cewa "zo mana Ayan in ba faɗa mi ya kawo gaba?" cikin ƙarfin hali har da ɗan murmushi na na yaƙe. Text ne ya shigo wayar afnan, Ya Ameen ne yake cewa lallai ta sanya ni inci abinci, shi ya wuce sai anjima zai dawo kuma lallai kar suyi hayaniya a ɗakin nan su tada umman tawa.
_Kuyi manage da wannan please bana É—an jin daÉ—i ne ku taya ni da addu'a fans_
~Oum-Deedat ce~
[8/5, 8:23 PM] Aminatu Hassan: 🌹 *_BAN FI ƙARFINTA BA_*🌹
🌺🌺🌺🌺🌺
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~âœðŸ½âœðŸ½GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATIONâœðŸ½âœðŸ½~*
*~â„We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u nopainâœðŸ½~*
*Rubutawa*--- _Amina Hassan (Oum-Deedat)_
*Hakk'in Mallaka*--- _(Oum-Deedat)_
*Sadaukarwa*--- _Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare._
🤸ðŸ»â€â™€ðŸ’ƒðŸ»ðŸ’ƒðŸ» Kuzo ku taya É—an ku Deedat murnar cika shekara uku cif a duniya, ina fatan Allah ya Albarkaci Rayuwar shi, ya shirya shi shirin addinin islam, ya bashi rayuwa mai Albarka, ya bashi ilimi mai yawa mai amfani, ya cika mashi burin shi na zama Soja😄😆 ya bamu ikon tarbiyyantar dashi. AMEEN ya Rab, Deedat yana gaida dukkan fans na *BAN FI ƘARFIN TA BA*
_*Page ~9~*_
°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°
Mu kau cikin ni da umma ta, babu wanda yayi runtsawar kirki, kowa da abunda yake saƙawa cikin rai, har gara ma umman tawa, tana ƙoƙarin ganin ta kau da komai, sabo da shawarwarin likita da ya bata na tayi ƙoƙarin ganin bata riƙe abun ɓacin rai a zuciyar ta ba.
Ni kuwa Allah Allah nake gari ya waye, domin na yanke shawarar ƙundunbalan tambayan umman tawa ainihin labarin mu, da asalin mu, lokaci yayi da zata dena ɓoye mani komai, na mallaki hankalin kaina, yaci ace ta fito ta fayyace mana komai kowa ya sani, ko zata fita a zargin da mafi yawancin ƴan gidan ke mana, a kan kunnen mu mun sha jin ma wasu ƴan ƙanana maganganu akan umman tawa da ni kaina ma, kai wasu ma cewa suke yi ni shegiya ce bana da uba, tinda haka suka ganta tazo gidan a wahale ga ɗiya duƙu-duƙu kuma taƙi faɗin wacece ita da kuma ainahin daga ina take.
Alhaji Mustapha kuma ya kafa dokar kada wanda ya tambaye ta, har sai ta gaji dan kanta ta faɗa, a cewarshi babu kyau shiga rayuwar wani, kuma hakan zai tada mata tsohon mikin dake ranta, gida dai nashi ne, tau tinda haka ne ya bata izinin zama har iya lokacin da take so, kuma tinda aiki tazo nema a zaɓa mata marar wahala a bata har sai ta murmure.
Ciwon umman tawa ya so ya tashi cikin dare, amman cikin ikon Allah abun ya taƙaita, ban so ace zan tada mata maganar da safe ba, gudun sake faruwar tashin ciwon nata, tau sai dai babu yanda na iya, wannan karon haƙuri na da kawaici na yazo ƙarshe, ba zan iya jurar ganin irin wannan rashin mutuncin ba daga wajen Hajiya kubran; da haka na samu bacci ya ɗan figeni har zuwa asubar farko da kiran sallah ya tashe ni.
*******************************
Ya Ameen yana shiga ɗaki waya yasa ya kira Afnan ɗin domin sheda mata yanda sukayi da Dad ɗin nasu, "Hello yaya" ta furta daga cen ɓangaren cikin muryar bacci "My Lil bacci kike yi ne?" ya tambaye ta cikin muryarshi mai daɗin sauraro a hankali, "eh Yaya na kwanta, lafiya dai ko? Ko wani abu kake buƙata? Ta tambaye shi tana mai tashi zaune da ƙara gyara ma Ayan dake gefen ta kwance bisa gadon nata lulluɓinshi," No Lil, ina dai son faɗa maki ne munyi magana da dad ne akan maganar waccen yarinyar, Amman tinda kin fara barci mu bari zuwa safe ki same ni part ɗina kinji, Good night dear" ya faɗa yana mai datse kiran ƙit, domin ya san halin zumuɗinta yanzu tana iya cewa ta taso ta taho, shi kuma baya jin ma zai iya doguwar magana yanzu ya gaji so yake ya kwanta, yana da muhimman ayyukan da zai aiwatar gobe, murmushi ya saki na gefen baki, wanda yayi sanadiyyar ƙara ƙawata fuskar tashi cikin hasken ƙwai mai launin dark blue na dare dake falon.
Miƙewa yayi cikin salon tafiyar shi mai cike da aji, ya shiga bedroom ɗin nashi domin yin shirin bacci, kayanshi kawai ya cire ya faɗa toilet ɗin da baya gajiya da shaƙar daddaɗan ƙamshin da suhan ɗin ta sanya mashi har kawo yanzu.
-------------------
Bayan mun kammala komai na Al'adar mu, kama daga sallah, wanka, sai muka zauna karatu ni da umman tawa, muna gamawa ne naga umman na ƙoƙarin tashi na dakatar da ita ina faɗin
"Umma ina so zamuyi wata magana dake don Allah" na faɗa ina mai rufe littafin umdatul-Ahkam ɗin gami da maida shi ma'ajiyar shi, na sake muskutawa domin girman maganar, ba zan ɓoye ba zuciya ta kaman tayo tsalle ta fito nake ji ta ƙirjina, masalan ma da naga irin kallon da umman tawa ke bina dashi, mai cike da ma'anoni daban daban,
komawa tayi ta zauna domin saurarar ɗiyar tata, da kanta yake duƙe kaman tayi ma sarki ƙarya, "Ehn ina jinki mamana, sauri nake yi domin kinga lokaci ya fara ja.
Sake sunkuyar da kai nayi ina mai komawa kalar tausayi maganar tayi ma baki na nauyi, shahada nayi lokaci guda na shiga faÉ—in
"Umma ki duba girman Allah ki faɗa mani asalin mu, wanene mahaifina? ina ne asalin garin mu, umma ke kanki su wanene mahaifan ki? Umma kin fi so mu zauna a gidan da ba'a san darajar mu ba? Kin fi so mu zauna ana wulaƙanta mu, ana zargin ki, ni kuma ana sheganta ni? Kada zuciya ta tafara yadda da maganar su fa!, na bani da asali, bani da mahaifi umma! Umma su nan ɗin ba dangin mu bane, basu san zafin mu ba, ƴaƴan su ma basa so su raɓe mu, suna kyamatar mu, suna ganin sun fimu umma, bazan iya jurar aci maki fuska a gabana ba, saboda kina ɓoye mana wani abu, kinƙi ki fito ki faɗa ma kowa mu ɗin su wanene ciki kuwa harda ni...... "