← Book details Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 56

Sashe 2

Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ganin ya kammala gininshi ga kasuwanci ya habbaka ya gina manyan store store na kayan masarufi da kuma kayan electronics sai kuma motoci daya fara shigo dasu daga qasar waje manyan 'yan kasuwa da 'yan siyasa na siye ta bangare guda kuma bai daina kasuwancinshi na qasar waje ba inda har ya zuba hannun jari a wani babban kamfani a China dayake saqa atamfofi da k'era wayoyin hannu.

K'arin girma sosai ya samu saboda karatunshi da ya qaro inda ya hada digree dinshi na farko da na biyu afannin qere qere da kasuwanci wannan shi yasanya gwamnati tarayya tafara bashi kwangila ta gina gidaje da masana'antu abundai sai Sam barka ba'a cewa komai addu'ar iyayenshi tana binshi tinda Mustapha mutum ne nagari maison kyautata ma duk wanda Allah ya hada shi zama dasu kuma baya kyamatar talaka ko mara shi duk daya ne awajen shi saboda yasan Allah ne mai azurtawa kuma yana azurta wanda yaso alokacinda yaso. Wannan kenan

*KUBRA* d'iya ce ga hamshaqin d'an kasuwa Alhj Nura,
Alhj Nura tare suke kasuwanci da Alhj Mustapha dukda ba tsaranshi bane ko kusa amman dai shi harka ta kasuwanci babu ruwanshi da wannan ta bangare guda kuma yana damawa a siyasar qasar babban dan kwangila ne da Allah ya azurtashi da makudan kudaden da shi kanshi baisan iyakarsu ba saboda yafi Alhj Mustapha kudi nesa ba kusa ba, kubra kyakkyawa ce dukda bazata gwadama Mustapha komai ba, ahaka Allah ya hada jininsu suna soyayyarsu dukda ita taganshi tace tana sonshi wanda hakan tasa Alhj Nura yima Mustapha magana, baiyi qasa aguiwa ba ya amince duba da yanzu iyayenshi babu abunda sukeso dagani irin iyalanshi kada girma ya cimmashi ahaka batare da ya tara zuri'a ba.

Kubra na da wani hali na kyamatar talaka da marar galihu inda Mustapha bayason wannan halin har yana mata magana akai irin yadda yaga in yaje fira gidansu tanama ma'aikatansu bayajin dadi sai yake dan tsawatar mata lokaci lokaci,

to tana dai kokarin kiyayewa saboda irin son da take mashi saboda Mustapha kyakkyawane ajin qarshe ga naira ga Hutu dukda bazai nunama mahaifinta komai ba.

Acikin haka ne Allah yasanya akayi auren Mustapha da amaryarshi kubra suna zaune kalau, wannan tasa ya jama yan aikinsu kunne ya gaggaya masu halinta saboda su kula kuma suna kokarin kiyayewa.

Dangin Mustapha kaf sunason kubra (kundai San yanda akeson mai kudi) iyayenshi girma ya kamasu yayinda mahaifinshi ya koma ya zauna ya barma qaninshi duka hidimominshi tinda 'ya'yan sun kawo karfi, saidai fa Mustapha ya gyara masu gida ya maidashi na zamani tinda sun k'i baro mahaifarsu ya sanya masu masu aiki da masu gadi da dreba guda daya mai suna iro suna kula dasu tinda yanzu babu sauran kowa a gabansu in ka dauke jikokinsu yaran Aisha da Fatima harma da yan biyu dake zuwar masu Hutu kuma tinda akwai ma'aikata suke kula dasu don dai hajiya zuwaira girma ya kamata don ma dai jikin nasu ba irin namu bane ba 'ya'yan yanzu.

Mustapha yaba 'yan uwanshi kaf jari kuma dukansu ya tattara su bayan aurenshi sukaje qasa mai tsarki suka sauke farali harma da wasu daga cikin ma'aikatanshi dayake ya bude babban kamfanin markada qarafuna a jihar legas yayinda ya dauki ma'aikata daga jiharshi ta haihuwa dakuma saura daga saura jihohin nigeriya

Ahaka Allah ya azurta kubra da samun diya mace kyakkyawa aka sanya mata suna Nafisa suna cemata feena daga ita sai Al'ameen suna ce mashi Ameen sai saudatu ana cemata saudat sai mai sunan Hajiya zuwaira suna cemata Nihal saikuma namiji data haifa Yusuf ana ce mashi Abi sai autarsu mai sunan maman Hajiya kubra watau bilkisu ana cemata Afnan.

Yara ne sun taso cikin gata da kulawa,kuma ga karatun arabi dana boko gabaki daya Allah ya basu saboda mahaifinsu mutum ne mai tsantseni yaran wasuma ya tsaya ya kula dasu bare nashi, Sam bayason abunda zai bata mashi tarbiyya da karatun 'ya'yan nashi, wannan ce ta sanya ya tattara kan 'ya'yan nashi ya tafi qasar waje dasu bawai don ya raina tashi qasar ta haihuwa bane a'a saidai kawai irin yanda yanzu karatun kasar namu ya tabarbare

acen yasanyasu makaranta mai kyau da ta Haddar alkur'ani dasauran litattafai, ahaka nafisa tasamu miji a cen qasar ta Dubai inda akadawo nigeriya akayi bikin kasancewar shima dan nigeriya ne iyayenshi yan asalin garin zariya ne,amman acen yake kasuwancinshi dama karatu ya kai shi kuma ya gama harma ya fara aiki da wani kamfanin kera takalma da abaya irin na mata.

Gabadayansu sun gama karatunsu inda mohd Al'ameen ya karanta fannin kasuwanci da fasaha (watau dai ya gaji mahaifinshi) ya hada masters dinshi ya jona yanaso yayi doctrine dinshi ita kuma sauda tayi degree na biyu yayinda Nihal da abi suka kammala degree na daya itakuma afnan tana aji na biyu secondary wannan ne ya sanya Alhaji Mustapha ya tattara kan iyalanshi ya dawo qasarshi ta haihuwa domin qasar ta amfana da ilimin da 'ya'yan nashi suka samu

Amman sun baro afnan gidan aunty feena domin karasa nata karatun, suma su Nihal da abi zasu koma idan sunso su cigaba amman alhaji yace sai sunyi aure tukunna domin ya gaji da ganinsu haka zaga zaga dasu ba aure.

Inda moh'd Al'ameen ya wuce qasar america domin karasa karatunshi daya dauko ta fannin fasahar zamani domin kasuwanci ya iya harma ya fara da taimakon mahaifin nashi

Hajiya kubra tana nan da halinta dakuka Santa dashi tin farko saima abunda yaci gaba domin mahaifinta Alhj Nura Allah yayi mashi rasuwa bayan haihuwar Nihal aka raba masu gadonsu, kasancewar ta na diya daya tilo ta mallaki dukiya da qadarorin da suka kara mata girman kai da dagawa domin yanzu bata jiran Alhaji wajen komai saboda itama ta mallaki dukiyarta ta agani afada wannan shi ya qara sangarta 'ya'yanta dukansu in ka dauke yaAmeen da afnan da bama ta qasar gabaki daya saidai tazo Hutu

Gida na nunama sa'a alhaji mustapha ya qera masu a garin abuja suka tarkato daga gidanshi na katsina, ya ba yayanshi alhaji auwalu da ya tara zuriya shima da matarshi Zainab abun dai sai sam barka yayinda ya sake siyan fili ya k'ek'ara ma iyayenshi gida a cikin kankiyan tunda tsufa ya kamasu kuma sunki barin mahaifar tasu ya kuma Gina masu gidan gona Inda aka cigaba da kiwon dabbobi kama daga su kaji,talo talo dawisu,shanu,awakai da duk wasu nau'in dabbobi da kuka sani ya kuma bada ana masu noma tinda itace tushen arzikinsu shiyasa basu yada ta ba.

'Yan uwanshi mata duka ya gina masu gidaje ya qara masu jari kuma duk shekara sai wasu sunje hajji su da iyalansu
ya dauki nauyin karatun 'ya'yan gaba dayansu kuma sunayin karatunsu cikin kwanciyar hankali wasu ma ya fiddasu qasar waje suna karatun tinda Allah ya hore mashi yanzu duk fadin Nigeria babu dan kwangila sama dashi,ya gina ma'aikatu yana daukar ma'aikata ga sana'ar motoci da qarafuna duk ya nayi,kudi dai ko ta wacce hanya juyasu yakeyi wannan shine silar arzikin Alhaji Mustapha Dambulan din kudi kenan inda ya tara tarin masoya da mahassada arayuwarshi.

YaAmeen ya dawo daga karatunshi hankali kwance da tarin Alkhairai,qasar ta amurka taso rikeshi saboda kaifin hankali da hazakarshi, amman ya qiya saboda irin tarbiyyar mahaifinshi dakuma kishin qasar tashi nigeriya.

*Wannan Kenan Yanzu Aka Fara*

🌹🌺~Oum-Deedat ce~🌺🌹
[8/5, 8:20 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹

🌺🌺🌺🌺🌺

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~*

*Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat)

*Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat)

*Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, qanwa daya tamkar dubu,Allah ya barmu tare.

Page ~3~

•∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆∆•

Muje zuwa.......

Ahankali zanmaku wacece "Suhan" ya labarinta yake kuma me ya kawosu irin wannan gida dayake cike da tarin gadara, shagwaba, mutumci, halarci,dakuma miskilanci

"""""""""""""""""***********"""""""""""""""

Cikin hanzari na siya abunda duk nasan anada bukata na baro kasuwar da tarin idanu yayiman yawa,
adaidaita na hau tare da fada mashi sunan unguwar da zai kaini.

yayinda muka isa nace mashi ya ajiyeni nesa kadan da gidan, sanin danayi cewa YaAmeen yana gida, kuma zai iya tambayata dalilin dayasanya driver bai kaini ba, tinda shikuma ya hanani hawan okada, acewarshi drebobin basuda amfani in har wani acikin ahalin gidan zai dinga hawa hayis,

(oh ko su wanene ahalin gidan oho😵)

Ilai kuwa yana qofar gidan zaune bisa darduma, yana shan daddad'ar iskar dake busowa ta sanyin marece dakuma flowers dake busowa, a lokaci daya kuma yana latsa iPad din dake hannunshi, dagani wani abu muhimmi yakeyi,cikin sanyinshi da halinshi ko wayar ma sai an yi mata Jan aji da yanga?🙄

Suf suf na wuce, wuf na shige ta tamqamemen gate din dake kofar gidan mai double,

saboda har ga Allah yanzu nidai kunyarshi nakeji tun abunda yafaru dazu dani akanshi,wai nice yau kwance a k'irjin yaAmeen...k'irjin da kowa ke mararin ganin mamallakiyarshi shi, k'irjin da mata da yawa keson kasan cewa bisa shi,
ni nayi imani in ka kadauke kannenshi nice ta farko da na fara kwanciya bisa shi, nima fa a tsautsayi ne ba yin kaina bane ba tinda ko magana zamuyi bana yarda in kusanci inda yake kawai ina tsayawa ne ta inda zan iya jin maganar shi
Shima kuma yana k'ok'ari wajen ganin ya ma baya ga duk wata d'iya mace da ba muharramarshi ba.

( yo wa ma zai iya rungumewa wannan sarkin 'yan miskilan🤔)

Da wannan guntun tinanin nashige sashenmu damin isarma da ummarmu aikenta, nima inyi maza in hada ma aunty Nihal fruit salad d'in da ta ceman tana so,wanda saboda tsabar isa da taqama saidai tayiman text din in hada mata d'in.

Shi kau ta bangarenta yana lura da ita tin sa'adda napep ya ajiyeta da sand'on da takeyi kada ya ganta, bata san ta riga ta makaro ba,

murmushi yayi mai kama da an sanyashi dole, domin shidai lamarin yayinyar na bashi dariya, shidai har ga Allah ba shiga lamarinta yakeyi ba, amman ya kula mahaifiyarta na iyakar kokarinta wajen bata tarbiyya, ko motocin gidan ya kula mahaifiyarta ta hanata hawa.
Chapter 2 · 0% Book details