← Book details Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 56

Sashe 24

Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kowa ɓangare shi ya wuce, wannan ce ta sanya suma su Nihal ɗin komawa cikin nasu sashen inda suka tarar da hajiya Kubran zaune tana ta faman cika, zaman jiran Alhaji ya shigo domin ita ba da Al'ameen ɗin zata yi ba da wanda ya ɗaure mashi gindin yin abun zata yi, zata ji dalili, kuma tabbas zaman munafukar matar cen ya ƙare a gidana tinda so ake a mallake man ɗanɗa na. Abunda take ta faɗa kenan yayin da ta miƙe ta shiga safa da marwa, su dai aunty Feena da afnan ɗaki suka shige yayin da su saudat suka zauna suna ta ƙara yi mata famfo da ingiza mai kantu akan al'amari, muddin aka ce yarinyar cen ta auri yayan nasu ai sun kaɗe, yarinyar da babu irin wulaƙanci da tozarcin da basu yi mata ba, Amman ace wai zata zama aunty su, tabɗijam "lallai Mom baki ga ta zama ba" cewar Saudat ɗin

°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Kai tsaye ɗaki shi ya wuce, kayan shi kawai ya cire ya faɗa toilet ɗin ya sakar ma kanshi shower, ko sauraren Bilal ɗin baiyi ba, da yake ta mashi magana, shi ɗin ma ya san halin ƴan kayanshi, ba zai samu amsa ba, balle ma ya lura da condition ɗin abokin nashi, anya kuwa wani abu bai faru ba a zaman taron na family ɗin? Yana cikin tinani Al'ameen ɗin ya fito daga toilet, ƙugunshi ɗaure da fari ƙar ɗin towel, yana ɗauke da ɗan ƙarami yana tsane kanshi, jikin shi ko ina gargasa ce kwance luf, baƙa siɗik, abun ka da farar fata, sai tayi mashii gwanin kyau, ko kaya bai tsay Sanyawa ba, balle ya cire towel ɗin ya faɗa kan gadon yayi rigingine fuskar shi na kallon cilling.

KafaÉ—arshi Bilal É—in ya dafa yana daga kwance "Man me ya faru ne? Ka gaya man na lura baka cikin natsuwa" kaman yana jiran cewar Bilal É—in ya shiga faÉ—in "Friend na yanke É—anye hukunci, ba tare da nayi tinani ba, Friend why? Me yasa nayi haka? Anya kuwa ban sha wani abu ba? Friend gaya man" ya faÉ—a yana mai tashi zaune ya juyo sosai busa gadon yana fuskantar abokin nashi, idanu shi sun kaÉ—a sunyi jajur dasu

"Yarinyar tausayin su kawai nake yi, babu soyayyar ta ko ɗigo cikin raina game da ita, me yasa haka? Na jawo ma kaina raini, duk dan in faɗa kar da mahaifiya ta akan illar tsanar mutum haka kawai, yaya Mahaifiyar ta zata kalli abun, miƙewa yayi yana mai gyara zaman to wel ɗin a jikin shi, ya shiga taka wa a hankali cikin ɗakin, kai komo ya shiga yi cikin ɗakin kaman yana neman wani abu.

Miƙewa Bilal ɗin shima yayi yana mai kamo hannun abokin nashi, tabbas ya san duk lokacin da yaga abokin nashi cikin irin wannan halin yana buƙata neman taimako ne.

Zaunar dashi yayi bisa sofar dake ɗakin mai zaman mutum biyu, "Cool down Friend, ka natsu ka gaya man meke faruwa ne?" kaman yana jiran shi ya ɗan zabura ya zamo daga bisa kujerar kaman zai zauna ƙasa, yayin da ya kama hannun Bilal ɗin ya runtse shi sosai, kaman zai tsinke hannun "Friend ni na zaɓe ta da kaina, ni na amince ma auren ta da kaina, yarinyar da ka gani jiya a gidanmu, na amince zan aure ta, Friend ka bani shawara, how am i going to do? Wannan ƴar yarinyar Friend, ko aure zanyi Ai tayi man kaɗan, Amman nine da bakina nace su Abba su nema man auren ta Friend ya zanyi? Bata san meke faruwa ba, bata san zan iya yanke wannan ɗanyen hukunci a kanmu ba, zata so ni? Zata yarda dani? Mahaifiyarta zata amince mani? Ya faɗa yana miƙewa tsaye, shima ɗin dai Bilal ɗin a kiɗime ya miƙe jin abin da abokin nashi yake faɗa mai kama da almara, mai kama da tatsuniya.

*"WHAT"*

*Al'ameen Are U In Your Sense?*

Bilal ɗin ya shiga faɗi a kiɗime cikin ɗaga murya, yana fatan kunnen shi basu ji mashi daidai ba, yana fatan ace mafarki yake yi, ina Al'ameen ɗin ina ƴar aiki, marar galihu, jiya jiya nan fa da daddare Al'ameen ɗin ke ce mashi ba'a san asalin yarinyar ba, inko haka ne me ya ja ma abokin nashi? Me ya shiga kanshi, saɓanin abin da yake son yaji ne ya shiga faruwa, lallai Al'ameen ɗinne ya shiga gƴaɗa mashi kai cikin tabbatas wa, da kuma neman mafita.

~Oum-Deedat ce~
[8/5, 8:25 PM] Aminatu Hassan: 🌹*_BAN FI K'ARFINTA BA_*🌹

🌺🌺🌺🌺🌺

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain✍🏽~*

*Rubutawa*--- Amina Hassan (Oum-Deedat)

*Hakk'in Mallaka*---(Oum-Deedat)

*Sadaukarwa*--- Ga Hauwau Hassan (jiddon dady😘) Amarya ta ango babu wanda zai iya fasalta k'auna ta gareki, k'anwa daya tamkar da dubu Allah ya barmu tare.

*Page ~15~*

°^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^°

"Hajiya Laila kina jina ko? Ki bani way out please ƙawata, ɗan cikina ne zai auri ƴar talaka? Talakan na ma'aikaciyar gida na? Wadda bata da komai, bata da asalin kirki ma? Kai ina ba zai taɓa yiwuwa ba sam wallahi"

Hajiya kubra ce riƙe da waya a hannun ta da alama waya take yi tin bayan shigar ta sashen nasu, ko zama t akasa yi sai kai kawo take yi a tsakanin tanƙamemen falon nasu da yaji kayan alatu kaman ba za'a mutu ba

"ina jin ki Hajiya Kubra" daga ɗaya ɓangaren aka bata amsa cikin isa da izza ga dukkan alamu dai ƙawarta ce.

"Ba kina jina zaki ce ba Hajiya Laila, mafita nake nema, kin dai sanni, kinsan buri na, kin kuma san yanda nake ƙaunar Al'ameen a duk cikin ƴaƴa na"

Ta tari numfashin Hajiya Laila cikin sauri

"Gaskiya ne Hajiya ta, ai wannan maganar ba ta waya bace, anya ma kuwa ba asiri sukayi mashi ba? Kin san fa tin lokacin da kika kula da shisshige masun da yake yi ya kamata ace kin taka ma abun burki, Amman son da kike mashi ya hana"

"Hajiya Laila wallahi nayi ƙoƙarin hakan tin lokacin, Amman ɗan banzan yaron nan yaƙi bani haɗin kai, kin dai sanshi da shegen zurfi ciki, da kuma miskilanci, ni kaina rasa gane kanshi nake yi"

Hajiya Laila ce ta tari numfashin hajiya kubran da cewa, "ba kince su keyi maku girki ba?". "Eh kwarai kuwa hajiya, in ba girkin su ba baya cin na kowa wlh" humm, Hajiya laila ta numfasa gami da sakin wani ɗan guntun murmushi ta cen ɓangaren, sannan ta ɗora da faɗin

"To wallahi ina mai tabbatar maki a nan suka samu, suka samu abin da suka barbaɗa mashi yaci, yanzu abin da nake so dake ki kwantar da hankalin ki, abun zai zo mana da sauƙi, kedai kiyi ƙoƙarin dawowa akan lokaci"

Nisawa Hajiya Kubra tayi cikin ƙunar zuciya da tsanani ɓacin rai, kaman zata haɗiyi zuciya ta mutu, sannan ta cigaba da cewa

"Shikenan Hajiya Laila, ina so please kiyi tinanin neman mafita, saboda ni duka ma kaina ya ƙulle wallahi, gabaki ɗaya yaron nan so yake ya birki ta mani lissafi, na yarda dake ne, insha Allahu kuma zanyi ƙoƙarin ganin na dawo akan lokaci, yanzu ma zuwan maneman su suhan ne kawai zai tsaida ni"

"Is OK Hajiya Kubra, baki da damuwa ki kwantas da hankalin ki, ina mai tabbatar maki da maganar nan zata sha ruwa, ko shi Alhajin da ya goya mashi baya, ba zai ma ƙara tada maganar ba, balle wani Alhaji Auwalu cen, da zaki ɗaga hankalin ki aka shi;To ko Isuhun ma bai isa ba balle ƴaƴanshi"😒

Hajiya Kubran ce ta murmusa mai cike da yaƙe, "Humm Hajiya Laila kenan, baki da dama, haka nake so, Shiyasa nake son ki nafi yadda dake akan kowa cikin ƙawaye na, na mayar dake aminiyata ta hannun dama ta, wuƙa da nama na hannun ki, a fara komai kafin in dawo, zan tura maki duk abin da za'a buƙata"

"Ba damuwa Hajiya Laila, ke dai sai kin dawo dai, ƙibar komai a hannuna, sai mun yi magana"

"OK shikenan a huta lafiya Hajiya Laila, sai Naji daga gare ki" ta faɗa tana mai datse kiran gami da zama cikin ɗan samun sassauci, saboda sanin halin hatsabibancin ƙawar tata, komai take so mai sauƙi samu ne, indai tabi ta hannun amini yar tata.

**************

"Look Friend kayi gaggawar yanke hukunci, aure ba abu bane da akeyi mashi hawan ƙawara, yarinya r zaka iya taimako ta, ba sai ka aure ta ba, ina so ka sani aure babu soyayya ba abu ne da ke ɗorewa ba, masalan yanda zaka yi manage na zama da ita, a yanda na san ka yarinyar bata yi daidai da ra'ayin ka ba, beside ma mahaifiyar ka...... "

Dakatar dashi Al'ameen ɗin yayi, ta hanyar ɗaga mashi hannu," Bilal! Please mubar maganar haka, kayi man addu'a kawai" abin da ya faɗa kenan, ya miƙe a hankali ya zura kayanshi, gami da zarar keys ɗinshi na mota ya fice daga gidan ma baki ɗaya.

Da kallo abokin nashi ya bishi dashi, "Hooo Al'ameen kenan, ko sai yaushe zai cenza? Kaman bashi bane yanzu yake neman way out, yaro kaman mai bira'izai? Wannan ko auren yayi wahalar da yarinyar kawai zai yi, bai iya wata soyayya ba, balle ya tsaya bata kulawar da ta dace, kullum kai kenan a murɗe? A baibai? Humm" ya faɗa a fili yana mai miƙewa shima ya fice daga ɗakin zuwa cikin lambu.

***********

Da sallama ya shiga sashen nasu, fuskar shi a matuƙar ɗaure, ko babu komai ya san bata kyauta mashi ba, a gaban kowa ciki har da iyayen shi ma, Amman taso tayi jayayya dashi, har tana ɗaga murya akan kowa da ficewa ma baki ɗaya daga perlour ɗin, dole ya nuna mata ɓacin ran shi, alwashi ne ya sha shi aure sai anyi, zai ga wanda yake gaba, cikin shi da ita; ko ɓangaren da take bai kalla ba, ya wuce kai tsaye zuwa bedroom ɗinshi domin wanka da shirya ma zuwa sallar magariba da ta gabato.
Chapter 24 · 0% Book details