← Book details Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 56

Sashe 32

Ban Fi Karfinta Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya daɗe office zaune yana jujjuya wayar a hannu, ƙare mata kallo yake tsaf, shi dariya ma abun yake bashi, lallai mace sai dai a barta, bai ga abun kuka ba anan, ita bata san ma kukan da take masu zai ƙara masu ƙaimi wajen Abunda suke shirin aikata mata ba? Tin farkon biyo ta da sukayi yake kallon su ta cikin mota, har kawo inda ɗaya ya janyo mata ƴar hijab ɗin dake saman kanta, baiyi niyyar fita ba, Amman kasancewar hangowa da yayi abun nasu na neman wuce makaɗi har ta kai ga sun janyo mata jikka ta katse, shi ya tunzura shi ya fito a sukwane zuwa gare su, yayi niyyar hukunta su, sai kuma ya fasa ganin cewa zai iya ja mata, wata rana ko a hanya suka haɗu da ita su so su rama abinda ta sanya aka yi masu, hakan ce ta sanya bai ko tanka masu ba lokacin da ya isa wurin.

Hannun shi ya ɗaga gami da kallo, cen ƙasa zuciyar shi na raya mashi, me yasa ya kama mata hannu? Har da goge mata kwallar dake zirara saman fuskar ta? Me hakan ke nufi? Shi dai ya san in afnan ce ba zai iya bari yana kallo a so aci mata mutumci ba, ba zai iya jura ba, ita kuwa suhan ɗin yana mata kallon kamar afnan ne, ko don saboda tsananin ƙaunar afnan ɗin ga suhan ɗin.

"Sai dai kada ka manta, ita É—in ba afnan bace, ba muharrama ka bace"

Abunda wani sashe na zuciyar shi yake tinano mashi kenan, É—an murmushi ya saki yana mai girgiza kanshi irin na gamsuwa.

Murmushi ya sake saki har saida kuma tun shi gabaɗaya suka loɓa, tinowa da yayi da hajiyar shi ƴar drammer, da yanda ya rufe mata baki d damun shi da zancen aure da take yi, nisa wa yayi gami da jawo wayar shi, ya kamata ma ace sun dawo hakanan, gidan baya mashi daɗi ya kasance babu kowa daga shi, sai masu aiki, Alhaji nasu ma baya ƙasar duk da shima gaf yake da dawowa ko don hidimar bikin su Nihal ɗin.

Kira biyu yayi Alhajin ya É—auka yana dariya "Yaya dai Son? Kwana biyu kajini shiru ko?"

Murmushi ya saki yana mai cewa "Nothing Dad, good afternoon, Ya aiki?"

"Aiki Alhamdulillahi Ameenullah, ya fama da jama'a? Fatan dai komai yana tafiya normal?" Amsa mashi yayi suka ɗan taɓa fira haka mafi yawanci da ya danganci aiki ne, yana kuma sanar dashi shirye shiryen kammala ginin gidajen nashi, da yanda za'a shirya ƙaddamar dashi, Alhajin ne yace su bari tukunna su gama da hidimar bikin su Saudat ɗin, saboda kada ayyuka su rincaɓe masu, ba haka yaso ba, yaso ya cigaba da shirye shiryen shi, hidimar biki ai ba tashi bace shi da yake namiji, kuma ba bikin shi ba ko na abokin shi Bilal, da to ya amsa ma Dad ɗin nashi, sannan ya sa yo buƙatar shi ta son Alhajin yayi ma Hajiyar tashi magana su dawo gida hakanan, duk abinda basu gama siya ba, akwai a gida nigeria, shi bai ga dalilin da za'a ce siyayyar kayan gida ba, sai an kwasa zuwa wata uwa duniya, murmushi Alhaji Mustaphan yayi, ko ba komai ya san yaron nashi wajen kishin ƙasar tashi ta nigeria, amsa mashi yayi da zai kira su ya sanar dasu, sallama sukayi suna mai marmari da begen juna, ƙauna ce mura ran mai tsafta Alhajin yake ma yaron nashi, ko dan kafin hankali da zurfi tinani irin na ɗanɗan nashi, duk ayyukan dake gaban shi, baya taɓa gajiyawa, ko ya nuna ya sare, balle ya gaza, addu'a yaci gaba da bin yaron nashi, Allah ya cigaba da taimaka mashi da haskaka mashi a dukkan al'amurran da ya sanya a gaba.

***********************

Ko da Alhajin ya kira su akan su koma gidan, a cen ƙasa ran Hajiya Kubran ba haka taso ba, saidai isa da izza ba zasu bari ta bari ta nuna ba har ma waɗanda suke tare su gane, watau su Hajiya Laila, da kuma wata ƙawar ta makusanciya watau Hajiya sa'a, dama su shidda ne sukayi tafiyar sai sabuwa ƴar aikin da suka samu itama yarinya ce duk da zata ɗara ma Saudat kanta a shekaru, idanun ta a buɗe yake, dama bata aiki sai gidan masu hali, ga iya tuggu da munafunci, wannan ce ta sanya ta ƙara shisshigi ma hajiyar, duk da tana jin haushin mulki irin na hajiyar, su bakwai kenan, Hajiya Kubra, Hajiya Laila, Hajiya sa'a sai Nihal da Saudat sai hafsat ɗiyar Alhaji Awwalu da za'a haɗa bikin nata da su Nihal ɗin sai kuma sabuwar ƴar aikin tasu mai suna Maria, ana ce mata Maree.

Ko da Hajiyar ta faɗa masu batun komawa tasu, basu ji daɗi ba matuƙa, kumburi suka shiga yi, harda cewa zasu kira Dad ɗin nasu su roƙeshi ya ƙara masu sati, Hajiya Kubran ce ta hana su, saboda mulki da taƙama na kai kawo acikin jinin jikin ta, kuma bata isa saɓa ma Alhajin ba, saboda shi ɗin namiji ne tsayayye a gidan shi, baya ɗaukar wargi ko saɓa dokar da ya gindaya akan kowa dake zaune a gidan.

Ta ɓangaren Hafsat kuwa abun yafi kowa faranta mata rai, cikin zuciyar ta dama ta ƙagara su koma ƙasar tata ta haihuwa, ta samu ta koma gidan su cen Katsina, dama abban ta ne ya tilasta mata zuwa, ko mahaifiya ta ba don taso ba, saboda ta san yanda family ɗin na ƙanen mijin nata suke da bala'i jin kai da sangarta, uwa uba kuma mahaifiya su da dama ba wani shirin arziƙi suke ba, domin ita ba zata iya binta ba, a matsayi ta na wadda take gaba da ita, ko ba komai daga ita har mijin nata basa jiran komai daga garesu, don dai ma kawai ƴan uwantaka, da kuma shi Alhaji Mustaphan da ba halin shi ɗaya ba Sam da matar tashi.

Ware ta suke yi, komai za'a siya ko za'a zaɓa ra'ayin su ake ɗauka, ba kuma komai bane in an siya masu ake siya mata ba, to don dai itama mahaifiya tata tayi ƙoƙari wajen ganin ta haɗo ta da ƴan kuɗaɗe daidai ƙarfin ta, gudun faruwa hakan, Hafsat yarinya ce mai natsuwa da kawaici, hakan ce ta sanya ko sunyi waya da mahaifiyar tata bata faɗa mata komai da halin da take ciki, ta riga da ta san Allah ya bata miji da gari, mai natsuwa na nuna ma sa'a, ita ba wannan abun duniyar ne yake gabanta ba, fatan ta dai kawai ɗaya ta koma ƙasar tata ta haihuwa, ko zata ga mahaifiyar ta mai share mata ku kanta, tana kewarta sosai, dan wanda zata aura bata jin shi, saboda kullum suna tare a waya ko kuma we-chat.

Saboda haka yanda suke ware ta ko kuma suke nuna mata halin ko in kula bai dameta ba, duk da abun na mata ciwo, wai ace waɗannan ƴan uwanka ne, Amman babu wata alaƙar arziƙi da zata haɗa ka dasu, kai su dai waɗannan ba suyi da cen hali ba, nazajen su sun kwasar ma kansu, yara babu abinda suka sani daga sangarta sai jin kai? Ta lura ita kanta ƴar aikin tasu Maree munafuka ce, bata cen bata cen, wannan ce tasa ta ja jikin ta bata sake masu sosai su kansu, balle su wulaƙanta ta, duk da ta san maƙudan kuɗi Alhajin ya haɗo su dasu, kuma Yayansu Al'ameen na sake turo masu wasu akai akai, hakan bai sanya mata kwaɗayin abun su ba Sam, kuma shi Alhajin da sunan siyayyar yara uku yake bada komai, har shi Al'ameen ɗin yana sake haddada masu duk da Abunda suka siya su siyawa Hafsat itama, Amman basa ji daga su har mahaifiyar tasu, da ta kwaso ƴan barandanta saboda kankan a suka wani taho siyayyar aure.

************

Cikin kwana na biyun da basu umarni sai gasu sun tarkato sun dawo dukan su da tarin siyayya raga raga, tare suka taho da kayansu, hayaniya Æ´an taron su ne ya alamta mana da dawowar tasu, ba zance bamuji daÉ—i ba, saidai lallai gabanmu ya faÉ—i, daga ni har umman tawa.

Jiki ba kwari muka fito taron su muma, gefe mukaja muka tsaya gami da gaishe su, cikin su ba wadda ta amsa mana, sai a tsaki da Saudat tayi ta shige war ta cikin gida, Hajiya Laila ce naga tana mani wani irin kallo da na Gaza gane ma'anar shi, ita kau Hajiya Kubran ko kallo bamu isheta ba, Hafsat ce kawai ta matso inda muke tsaye cikin girmamawa ta gaida umma ta, cikin fara'a ta amsa tana mai tambayar ta Mamanta, Lafiyarsu lau ta tabbatar mata, sannan ta janyo hannuna da nake tsaye gefe guda cikin zaulaya tace "Ƴan mata ya ake ciki?" murmushi nayi ina jan hannun ta zuwa gefe, na shiga cewa "ke Hafsat zakiyi laifi fa, ki bari zamuyi magana anjima" da to ta bini, tana mai matsawa gefe, hakan ce ta sanya ta ƙara basu haushi, bata ko kula su ba ta shige cikin gidan.

Bamu bar wajen ba muna tsaye har saida suka shige cikin gidan, sauran ma'aikatan duk suka watse suka barnu nan tsaye, umma ta ce ta matso inda nake tsaye ta shiga kallo na cikin gargaɗi, "Ki kula suhan, kar ki ja mana wani abu daban, kinga dai yadda suka dawo, tin anan ya alamta maki yanda abun yake, ki kiyaye" gyaɗa mata kai na shiga yi cikin gamsuwa da maganar ta, wucewa tayi gaba Ina binta laƙwai-laƙwai har zuwa sashe namu.

***************

Al'ameen da yake tsaye ta jikin window É—inshi, yana kallon duk abubuwan dake faruwa, tin daga shigowar shi gidan har watsewar su, ya sauke ajiyar zuciya, lallai Abunda yake gudun afkuwar shi ne yake faruwa, tsanar mutanen guda biyu ce yake hange cikin kayar idanun mahaifiyar da Æ´an uwa nashi.
Chapter 32 · 0% Book details