← Book details Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 65 OF 65

Sashe 65

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Kamar hajara zatayi kuka ta amsa tana runtse ido tashanye ta mikawa ameera kofin , murmishi ameera tayi tace ko kufa wannan fa gata nake muku amma kuna min wulakanci irin na amare , dariya sukayi tukun tafita ta rufo musu kofar

Da misalin karfe 2:00 pm na ranar asabar aka daura auren *hajara ahmed da muhammed usama sai na khadija hambali da aliyu alhaji hashim* akan sadaki naira dubu dari biyu biyu , sosai anguwar tacika da mutane

Anan aka fadawa yan gidan an daura auren hajara ko kuka takama yi , ita kuma khadija tagumi tayi tana kallon ta tace kefa garace hajara maimakon kiyi addu'a sai kike kuka

Hajara tace kukan farin ciki ne nakeyi ,Khadija tace kinga ni banyi kukanba

Hajara tace zakiyi aiba sosai kukayiba shiyasa bakiyi kukaba

Shuru khadija tayi tana jin maganar hajara

Da yamma aka shirya amare sunsha ado ga kyau kamar kasacesu ka gudu , fitowa sukayi a aka soma daukar kawayen amarya

Ni kuma ina tsaye ina dube dube naga wata mota zan shiga sai naga tawagar *fans din ameer da ameera* ansha anko kowacce takashe nan aka shiga mota sai wajan diner

Sai kusan magarib aka tashi kowa yayo gida

Washe gari akayi walima da da dare aka kai amare gidansu nasiha sosai aka musu tukun kowacce aka barta da mijinta (to hajara da khadija Allah yabada zaman lfy)

Bayan biki ameera da ameer hadda su umma duka dai family sukaje garinsu inna sosai ameera taga canji duk sun musulinta anyi masallaci da islamiya kowa kagani a garin abin burgewa hakan yakara faranta ran ameera da family ta

Kwana su goma tukun suka dawo gida aka cigaba da rayuwa mai dadi

BAYAN SHEKARA GOMA SHA BIYAR

Wata na gano tana saurin fitowa daga wani part da bulala a hannun ta tana bin wata karamar yarinya

Ita kuma yarinya taki tsayawa sai gudu takeyi

Shigowa akayi da gidan ya tifo da sauri ya tareta ta dauke yace haba wifey wai ummin nawace zaki daka har kika sauri haka kuna tsare , hararar shi tayi tana fadin dama aikai kake daure mata gindi tana rashin ji to bazan daukaba

Tajuya tashiga ciki binta yayi a falo yasameta tana kwashe kayan wasan data tara

Sunkuyawa yayi suka kwashe kafin yazauna yace mamana mai kikawa mommy naki

Yarinyar tace daddy wannan abun ne fa na zubar shine zata dakeni

Shafa kanta yayi yace to shikenan kidena kinji ,da to ta amsa yace ina yayanki yake tace yana gidan granny dukansu dai kadai ce banje ba ,Ameer yace to jekiyi wasa zanyi wanka idan nadawo saimuje cen din ko

Tana fadin ameer ya janyo ameera jikinsa yace duk fushin ne wifey na kefa yanzu kinzama babba kidena fushi

Dukan wasa takai mishi tace amma ai duk girmana a wajan ka ni yarinya ce

Kuncinta yaja yace hakane baby na muje kiyimin wanka ko , tasukayi , sukayi daki zan shiga ameer yace koma ki huta maman nusy

Nace to

Tammat bihamdulillah anan na kawo karshen littafin *ameer da ameera* Allah yasa muyi anfani da darasin dake cikinsa , kuskuren dana yi Allah ka yafemin

Shin acikin wannan littafin wani guri yafi baki dariya
Wani waje yafi burgeki

Wani waje yafi baki haushi

Wani waje yafi baki tuasayi

Ina jiran amsar ku fans 💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼

Muhadu daku a sabon novel dina mai sunan *hafsat*

*Takuce har kullin maman nusaiba ✍🏻*

*Nan zan tsaya*
Chapter 65 · 0% Book details