← Book details Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 65

Sashe 28

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ameera ta zagaya zata shiga wata kawar jamila tace. Ke yarinya ni zan shiga gaba kallon bakida hankali ameera tayi mata tace ban gane ba ,, wannan ai babu mai ikon zama anan sai ni a kufule,, matar tayo,, kan ameera,,, ta wanke ameera Da mari tana huci tace ke har kin isa ina magana kina maidamin,, ta juya kenan zata dawo tashiga taji itama an wanke ta da mari har hudu ko ina biyu²,, a gigice ta dago tana,, neman wanda ya mare ta,, kai ta daga taga,, Ameer yana huci kamar wani maciji

Ameer yace wllh kinci darajar jamila da saina miki dukan da ko wani,, yace miki ki maran mini mata bazaki kalleshi ba ke har kin isa na zauna waje daya dake kucaka kawai bagidajiya,, to wllh ki kula babu wanda ya isa taba jikin ameera yazauna lfy yana kai karshen maganar tasa ya matsa kusa da ameera

Bude mata hannu, yayi fadawa jikinsa tayi tana kuka bubuga,, bayanta yayi " yana rarrashin ta kafin tayi shuru yace na rama miki maza

Wacce aka mara kuwa haushi da kunya da danasani ne yakamata,, ashe dama matar shice kuma sai taga,, suna mugun kama,, tace wannan kila auren gida ne a kunyace,, ta shiga wata motar,,

Bilal da jamila basuji dadin abinda ya faruba,, haka suka bar gidan sukayi hotel din da ake dinner party din

Abokin ango ne suka tsaya,, a waje saida DJ yasoma kiran amarya da ango da abokan su zasu shigo kowa yashirya nan kowa ya zuba idonshi akan kofar shigowa,,

Jeruwa sukayi bilal da jamila agaba ameer da ameera a bayansu, Anass da fatima abayan su ameer ,, tukun saura mutane suma suka jera ,, nan aka soma shiga,, kida aka kunna " na soyayya,, nan suka shigo, kowa sai kus kus yake yi wasu kuwa, sun dauka ameer da ameera ne,, amarya da angon,, saboda yadda sukayi kyau sosai ga kamannin su da suke da juna

Nan ango da amarya suka zauna,, tukun abokai,,

Nan aka bukaci abokin ango yatashi yabada dan takaitaccen tarihin ango,,, Ameer yakalli anass yace kaje kai kabada, Anass yace kai yafi dacewa kabada ba niba

Ameer yace nifa natsani wai bada wannan tarihin banaso,, Anass yace ka daure mana ,, nan ya mike

Ganin hakan yasa ameera ta mike tace,, yaya zanje wata daga cen tace kai kalli wannan yarinyar duk inda gayen nan yayi sheta bishi dayar tace yayan tane fa ko bakiga suna kama ba,, tace eh kuma hakane da alama ita autarsu ce

Hannun ta yakama,, nan suka je wajan da ake DJ din yabawa, Ameer spika yasoma,, bada tarihin ango,, amma gajeren bayani yabada saboda shifa ya tsani yazo biki yaji ana bada wannan tarihin na banza da wofi,,yana gama wa " ya kama hannun ameera suka koma,, inda suka tashe

Mutane sai kallo su sukeyi yan matan kuwa kowacce sai kallon shi takeyi

Su ammi da mommy da mama da momsy ikram suna wajan murmishi ikram tayi tace kai ina sonku dariya tabawa su mommy,, ammi tace ai nima suna burgeni ameer da ameera,, Ikram tace ga batada wuyar sabo nan suka soma yar hirar su

Haka aka bukaci kawar amarya tabada story din amarya,, nan samira ta tashi " ta bada tarihin amarya,,

Haka akaci gaba da shagali, har aka tashi kusan magarib gidan ammi aka yi da amarya gobe,zaa yi walima ta mata kawai

Yau da misalin karfe 4:00PM na yamma aka soma gabatar da wa"azi na mata sosai malamar take jan hankali akan zaman aure kowa,, yayi shuru yana sauraron ta a haka aka gama walimar kowa ya tashi

Da dare aka kai amarya gidan ta,,, Wanda yake gida dayane amma part uku ne daya na bilal daya na anass daya na ameer,, a gida daya sukayi gininsu dan sunci suna son karfafa zumincin, su hakan kuma yayiwa iyayen nasu dadi sosai

Karfe 10:00PM aka rako ango dakin amarya daga ita sai ameera sai fatima sai samira ,, nan samira tace abasu kudin siyan baki,, babu bata lokacin suka basu nan suka musu sallama,, har bakin kofa bilal ya rakasu,, kuda bilal ameer yazo wajan, kunan shi yace kabin min kanwata dai ahankali,, nasan bakada kirki dukan wasa yakai mishi suna, dariya nan suka tafi shiam yakoma cikin wajan jamila

Salla dukayi da addu'o'i sukaci kazar su tukun suka rufo kofa,, (nima nace ango da amarya asha soyayya lfy)

Saida suka fara ajiye samira tukun anass shima yamusu sallama suka nufo gida, kowa makwancinsa yanufa su ameera sukayi sama,, Fatima tayi dakinsu!!

Anan zan dakata
[27/10, 23:22] MRS. MU'UTASIM: *🌟AMEER DA AMEERA🌟*

*RUBUTAWA DA TSARAWA*

*MAMAN NUSAIBA CE ✍️*

*💫💫JARUMAI WRITERS ASSOCIATION 📚🖊️*

*Marubuta masu aiki da jarumta jarumta domin wa'azartarwa ilimantarwa nishad'antarwa tare da fad'arkawa da jama'a bisa harshen hausa 💪*

*💫(J.W.A.)💫*

*45—46*

Suna shiga a daddafe ameera, tayi wanka ta dauro alwala suka yi salla tukun sukabi lafiyar gado

Yau ameera tayi last din zuwa school gashi yau, malamin nasu mai tsauri ne baya karbar uziri idan ka makara bakazo ba da wuri inhar yarigaka, to lecture din shi tabarka

Nafeesa ta mata text message tace besty wllh yau , mlm musa ne kuma harya shiga dan haka anbarki, tana karantawa ta kalli ameer tace, waiyo Allah yaya kallon ta yayi yace meya faru , fuskar tausayi tayi tace to yaya please ka rakani ciki, wllh mlm musa ne bazai barni na shiga ba , yace to saboda me tace please yaya kazo ka kaini idan, yaga dakai zaibari nashiga " Ameer yace to muje nan suka fita a motar suka nufi class din su ameera

Suna zuwa bakin kofar noking yayi mlm musa, yace yes come in shiga ameer yayi amma daga bakin kofa ya tsaya kowa kallon yayi, mlm musa yataso yazo wajan ameer " yace, assalam alaikum amsawa mlm musa yayi suka yi musabaha ameera na makale abayan sa,, janyota yayi gabanshi yace, please sorry yau ansamu akasi ameera tayi last din zuwa school kuma lefina ne nine ban kawota da wuri a mata uziri

Mlm musa na murmishi yace amma kanwarka ce ko shima murmishi yayi yace mai kagani yace tsananin kamarku,, Ameer yace eh kanwata ce kuma matata,, da mamaki yace sure yace yes am sure , mlm musa yace ameera zoki shiga , nan ta kalli ameer tace yaya kadawo fa ka daukeni, da wuri ,gidan momsy zanje kuncinta yaja yace to wife mata jeki,, murmishi mlm musa yayi yace iyee masoya kenan,, yar dariya yayi yace thank you mlm musa yace ba komai nan yafito ita kuma ta shiga ciki

Tana shiga, duk idonsu, akanta mamaki yakamata,, tace to ikon Allah ku kuma lfy kuke kallon ko na cenja kaman ni ne wata yar ajin su ameera tace eh ba dole kalle kiba munga yadda kuke kama da yayanki,, murmishi yayi yace to ai dama jini daya ba wasa bane yan mata " wata tace ni wllh dakin min kamu harnaji ina sonshi " nan da nan ameera ta hade , rai tace yayan nawa kikeso tace eh wllh sister,, please ki gabatar dani a wajansa kozan samu shiga " harara ameera ta banka mata " tace to wannan yafi karfin ki ,, tace kamar yaya ameera tace shidin mawane ni kadai *ameer na ameera* domin mijina ne da mamaki tace na gaske to Allah yabaki hakuri kinji ameera karkiyi kishi dani sakin fuskar ta tayi tace to shikenan nan tayi gaba

Wajan nafeesa tazo da zauna tace hello besty itama ameera tace heyy,,Mlm musa ne yashigo nan kowa yayi shuru yasoma gabatar da lecture din sa kowa ya nutsu dan bayason wasa ko reni

Bari muleka gidan amare bilal na hango a kitchen yana soya dankalin turawa da kwai duk yayi kaca kaca da kitchen din nan yahada komai yayi shayi gama komai yafito,, sama haura ,, wani daki yanufa " yashiga jamila na kwance tana baccin wahala,, " duk idonta sun kumbura saboda,, kuka " fuskar ta duk,, abin hawaye ne a bushe,, " kusa da ita yazo ya zauna

Fuskar ta yashafa,, yasoma hura,, mata iska a fuskar,, a hankali tabude, tana ganin shine da sauri ta rufe idonta ta juya mishi baya , tana rufe fuska

Kallon ta yayicike da so da kauna yace habibty na tashi mana nayimiki,, wanka bacci ya isa haka yanzu 11AM da sauri ta tashi tace da gaske jinjina, kai yayi yace, sosai

Mike tayi da sauri takoma sai hawaye,, kallon ta yayi cike da tausayi yace zo nan hannu, yabude Mata,, shigewa tayi jikinsa ya dauke yakai toilet,, ruwa mai zafi sosai ya hada mata saida yaji zata iya shiga , ya dauko ta idon a lumshe

Jinta tayi acikin ruwa mai zafi,, da sauri ta mike yayi saurin maidata yace please mana habibty zaki dena jin ciwon,, idan kika shiga, zama tayi tana kuka ,, tace nidai kafidda ni akwai zafi sosai lallashinta yakeyi har ,, ya mata cajin ruwa sau uku , tukun da fiddota daga ruwan, towel yasaka yanadeta, kamar baby nan yakai ta, gado

Mai yadauko yazo kusa,, da ita she sunne kai takeyi, bata son su hada ido dan wani mugun kunyarshi takeji,, jashi duk yawani like mata,, sai surutu yake, cikata dashi "

Towel din ya fidda yana kallon ta yana murmishi , da sauri tarufe fuskar tana sakin kuka tace,, nidai ka dauko min kayana nasaka sai wani kallo na yakeyi babu kyau fa, ganin mutum ba,,

Dariya bilal yayi yace ,, to meye ban ganiba a jikin banza ta mishi ta kwace towel din ta rufe jikinta

Shayi yakawo mata mai zafi a hankali yake bata harta shanye,, tana gamawa yabata magani,, tasha kayan ta ya dauko yasaka mata,, ya busar mata da gashinta,,, ya daureshi,, yace habibty kallo kigani na iya,, daure gashi dagowa tayi tana kallon madubi,, tace aikuwa ka iya sosai ,, yace da gaske tace eh,, rungume ta yayi,,yasoma kissing din ta,, badan tasoba yake maida mishi martani,, ganin yana neman,, zuge mata jib din rigarta,, yasa ta rike hannun shi tace,, habiby ka bari mana,, baima san tana yiba,, dan yama, manta da wahalar daya bata jiya da dare
Chapter 28 · 0% Book details