← Book details Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 65

Sashe 46

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Umar ya kalle ta yace yauwa my kanwa,, Allah yamiki albarka

Ameera tace ameen nan abubakar yabata muhammed

Umar zai shiga yaga, maman anty karima da sauri ya dawo , ya durkusa yace good afternoon mama , yakuke, ai ban lura kuna falon ba

Mamaki ne ,, yakara kashe maman anty karima , tace yauwa son ya gida ya su marus da beauty

Umar yace no mama yanzu marus yakoma abubakar sadeeq , ni kuma umar , mun musulinta , yanzu

Maman anty karima tace ,, muma ai zuwa mukayi ,, muji nawa zamu bayar " mushiga, nida son

Murmishin jin dadi umar yayi yace mama addinin musulinci , bada kudi ake shigar saba, kawai kalmar shahada zaa fada, miki ki biya shikenan kinzama,, musulma kamar mu sai kuma anuna miki yadda zakiyi wankan, shiga musulinci kafin ,, asoma koya miki salla da karatun salla dadai sauransu

Hannu biyu, maman anty karima ta daura ,, akai tana fashewa da kuka , sosai harda sharce majina,

Mamaki ne yakama , su ameera , saboda kunta

Ameera tace mama lfy kike kuka,, ko wani abun muka miki,

Share hawayen ta tayi ,, tace tin lokacin,, da wannan yaron ya karanta miki rubutun littafin ku , kika warke,, abun yashiga raina " sosai naji inason nashiga wannan addinin ,wanda ake bautawa Allah daya to bayan kwana biyu ,, munyi tafiya ne haihuwa akayi ,, kawata ta " mukaje suna shiyasa bandawo ba,, sai jiya shine nace zanzo naji nawa ake biya nashiga wannan addinin naku mai ,, cike da abin al'ajabi , da kuma nutsuwar,, zuciya munason musulinta,, nida dana da " mijina ku fada mana ' abinda ake fada muma muzama " irin ku ,

A tare suka ce allahu akbar ,, Ameera tace ,, bari na kira mai sunan daddy, yabaku kalmar shahada ,, nan tashiga daki da gudu,,

Wayar,, ta dauka tana kiran muhammed

Suna zaune sai hira ,, sukeyi doctor aisha da mijinta da muhammed,, karar wayar shice ta katse su dauka yayi ,, ganin ameera ce sai yayi murmishi yace assalam alaikum kanwata

Daga cen bangaren ameera " tace amin wa'alaikum salam,, barka da warhaka yaya mai sunan daddy na yakake yagida , yasu momma na da daddy

Yar dariya yayi yace kai kanwata wannan jero tambaya ,, haka kuma naji,, bakinki na motsi , nasan akwai magana to mommy gata nan, ita da daddy suna soyayya ,, abinsu

Kwashewa tayi da dariya ,, tace kai yaya wllh mommy saita zaneka ,tace yauwa kazo gidan mu yanzu akwai mutum uku zasu musulinta ,

Mikewa,, yayi baki a washe yace kai haba dan Allah da gaske ,, kikeyi kanwata ,

Ameera tace sosai makuwa kuzo harsu mommy ,

Muhammed yace to gamunan zuwa nan yakashe kiran yajuya gasu mommy dake,, kallon shi

Doctor Aisha tace muhammed ,, wanene ya kira kake wannan fara'ar

Yar dariya yayi yace mommy albishirinku

Doctor aisha tace goro fari tas tana murmishi

Muhammed yace ,, yanzu yarki takira ni tace muje gidansu " mutane uku zasu musulinta, shine nake farin, ciki

Su doctor aisha sukace Alhamdulillah to maza muje nan suka tashi doctor aisha ta dauko hijab tasaka suka fita , zuwa gidan su ameera

Babu bata lokaci , suka iso da sallama,, suka shiga cikin gidan, amsawa akayi suka shiga

Da gudu ameera tazo tayi hogging din doctor aisha tana, fadin waiyo momma na, nayi kewar ki sosai

Kanta doctor aisha tashafa tace nima haka ,, ameera na,, ina mai gida yake da kishiya

Ameera tace mai sunan daddy yana wajan abubakar , ita kuma ikram tana wajan mufeeda

Doctor aisha tace masha Allah nan suka zauna saida sukasha ,, ruwa kafin aka soma zancen su maman anty karima

Maman anty karima ta kira mijin ta ta fada mishi yazo gidan jenifer nan shima yazo ,

Zama sukayi,, Muhammed ya gyara , zama yace kunyi imani da Allah ,da mala'ikun Allah kunyi, imani da , annabin rahama , kunyi da kaddara mai kyau ko akasin haka, kunyi imani da littafin Allah mai tsaki , kunyi imani da ranar alkiyama

Nan suka amsa da eh dukkansu,, munyi imani dasu

Muhammed , yace masha Allah " Alhamdulillah

Kafin yace rukunnan , musulinci , guda biyar " na farko, kusheda babu abin " bautawa da gaskiya sai Allah ""
Kun sheda cewa annabi muhammadu , bawan Allah ne" kuma manzon sa ne ,, bayan nan, sai salla ,, azumi,,, zakkah , da ziyartar " dakin Allah ga wanda Allah ya nufa da zuwa , duk kun amince da wannan

Nan suka ce duka mun,, yadda dasu " kuma munason manzon Allah (S.A.W)

Muhammed,, yace Alhamdulillah ,, to yanzu duk abinda na fada ku maimaita ,,

Nan sukace ,, to

Babu bata lokaci muhmmed yabasu kalmar, , shahada , cikin ikon Allah ,, suka maimaita ,, babu matsalar komai ko tangarda ,, hakan yawa kowa dadi, musamman ma ameera

Kabbara sukayi , ameera ,, da mama suka rungume maman anty karima suna dariya , Ameera tace Alhamdulillah " Allah nagode maka

Shima, Muhammed da baban shi sukayi musabaha da baban karima da " kaninta,,

Muhammed yamusu bayanin yadda zasuyi wanka,, da alwala yace yanzu su bishi, zai koyamusu ", suratul fatiha kafin gobe ,, sukace to

Muhammed yace to yanzu ,, kunzama mu munzama ku wani suna,, kukeso asaka muku,

Baban karima yace, ni inason usman

Muhammed yace masha Allah usman suna mai dadi

Kanin karima yace ni, inason, Nazeer sunan yana burgeni shinake so

Muhammed yace masha Allah nazeer suna mai dadi

Maman anty karima tace , ni ina son maryam,, sunan yayata " ne bayan ta musulinta ,, yanzu ban sani ba tana raye kota mutu , kullin ina tunanin yanzu a wani hali take ciki " yar uwa ta ina sonta matuka, tana saka kuka ,, dan abin nacin " mata rai na rashin yayar ta tsayin shekaru,, tun suna yara, iyayensu suka,, koreta " saboda ta musulinta ,

Muhammed yace masha Allah maryama,, uwar , Isa alaihissalam ,,kidena kuka insha Allah " zakiga yar uwar taki insha Allah har tana raye a duniyar nan zaki ganta wata rana

Share hawaye mama karima tayi ,, tace to insha Allah

Shima mijin nata, kallon ta yake cike da tausayi ,, dan shima bayajin,, dadin ganin matar tashi a wannan yanayi

Kusanta ameera tazo tace,, mama kidena kuka,, kinji insha Allah zakiga maryam yayar ki, indai tana raye, indai kin daukeni kamar anty karima , to kidena kuka ", zan koya miki addu'ar reman sauki " insha Allah komai zaizo cikin sauki

Rungume ameera tayi tana share hawayen ta tace nagode sosai daughter " wllh idan ina ganin ki sainaga sak , yama sunan nata yake,, na musulmai

Ameera tayi murmishi tace , sunan ta karima

Mama tace kamar ku daya da karima ta,, inason wata rana,, kuga juna " zaki gaskata maganar ,, mu dan komai naku iri daya ne ,, har hasken , kawai karima shekaru ne zata muna miki

Ameera tace insha Allah nakusa haduwa da , yar uwa ta ,

Sun jima suna hira sosai kamar,, sun shekara " da ganin juna, haka suke haka aka ringa koyawa su mama , alwala tsarki wanka ,, da,, tsada salla, da karatun suratul fatiha dan shi,, farillah ne ga wanda yazo,, yin salla da sauran abubuwan daya shafi addu'a,, wa'azi mai yatsa jiki da nutsuwa muhammed ,, ke wa mazan yana ,, nuna fada musu abinda mutum " inyayi ake sakashi wuta da launinkan azabar,, da za'awa mutum " idan ya aikata mummunan hali

Yana jaddada, musu yadda aikin alkhairi yake kai mutum aljanna da kuma yadda gidan aljanna yake da suffofin sa da rayuwar shi mai dadi ta abadan da'iman bata,, karewa

Muhammed yakara sa cewa ina mai jan hankalin ku " kada kusake zuwa wajan boka ,, idan kuna da bukata ku daga ,, hannaye ku roki " Allah abin bauta , saiya biya muku mukatar,, insha Allah

Kuka sosai sukeyi musamman ma , baban karima,,, dan yasan rayuwar ,, da sukayi ashesu basu sani ba " asarar lokacin su na duniya suke basu gane b kai Alhamdulillah , Allah yakarawa musulinci,, daraja sa daukaka

Suka amsa da ameen

Muhammed yace mazan suke zuwa ,, wajan sa daukar karatu matan kuma,, wajan ameera

Suka amsa da to

Ameera ta share hawayen farin ciki, tace yaya dama ,, inason zamu bude islamiya , a jikin gidan mu,, muke karatu mazan sukeyi dakai

Murmishi,, Muhammed yayi yace wannan kinyi tunani mai kyau , sai asoma gobe insha Allah ,

Nan masu tafiya sukata ,, tashi su ameera har bakin get suka ,, rakasu suna musu bey bey

Yau takama , Monday ,, ranar aiki kenen,, Ameer ne yafito,, sanye da inform din likitoci ,, tana sauri ,

Inna ya samu ita da su fatima fauziya hajara ummi mufeeda,, mommy and daddy ,, basu fito ba

Karasowa yayi yace good morning ummi na yana isa gareta , yamata kiss a goshinta

Itama,, kiss ta mishi tana murmishi tace morning my son katashi ,, zaa fita aikin ne

Ameer yace eh

Su fauziya ne suka gaishe shi, ya amsa suna rungume shi shi, kuma yana dan bubbuga bayansu,,,.

Hajara kuwa,, turo baki tayi " ta juya mishi baya

Su Fatima suka mata dariya ,,

Fatima sarkin ,, tsokana tace,, shagwababbar yaya ,, ai nasan dama yaya kayi " lefi jiya ,, na ganta tana kuka kamar ance mata inna ce ta mutu " kaga yadda ta ringa,, jan zuciya " ni wllh jinake ma zaneta kayi wai ashe korota ne kayi daga dakinka

Inna kuwa an soso mata inda yake mata kaikayi ,dama ta kwana biyu batayi masifa,, shiyasa yanzu har bakin ta rawa yake saboda masifa

Ubanki ne, Muhammadu zai mutu banida, yar jakar uba, ni kikewa fatan mutuwa to wllh ashir dinki , yar banza mai,, kama da kodadden,, takarda " dama ai na kauna ta kuka ba kida ameeru ,, gyarama shi dake , yar butar uwa,, taci gaba da masifa kamar ta ari baki,

Dariya suke mata

Ameer yacewa hajara my kanwaty, zo nan kinji
Chapter 46 · 0% Book details