← Book details Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 65

Sashe 59

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sosai maman mu ke kuka tana rokonshi yabarmu zata mana magana amma ya kiya

Yara yatara yace su koramu mubar gari mushiga duniya

Nan suka rakamu har bayan gari ,, wani acikinsu yazo kusan shareef yace kutafi kunji ,, karku yadda kudawo nan papa yace mukashe ku to amma ni bazan iya kashekuba ,,saboda kunada kirki

Godiya muka mishi sosai nan shareef yakama hannu na muka soma tafiya

Headmaster , ko yana zaune yana karanta alqur"ani mai girma ,, samarin garin suka far mishi saida suka kashe shi tukun suka barshi ,anan matacce

Haka muka ringa tafiya har mukazo cikin garin legos na gaji sosai ga yunwa , nan na fadi sumanmiya ,, a bakin hanya

Da gudu yayo kaina da karfi shareef yakira sunana maryam !!!!

*anan zan dakata ✍️bana jin dadi*

*Nagode sosai da addu'o'i ku agareni Allah yabar kauna🥰🥰*
[30/10, 19:23] MRS. MU'UTASIM: *🌟AMEER DA AMEERA 🌟*

*story and writing*

*By*

*MAMAN NUSAIBA CE ✍🏻*

💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*

https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_

*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*

*85—86*

Da gudu shareef yakaraso ,, inda nake kwance yana fadin maryame dan Allah kitashi karki tafi kibarni in kika mutu ina zan saka kaina ke kadai gareni a rayuwar yanzu banida kowa saike , nan ya sabani a kafadar shi yakawo bakin wata bishiya ya ajiye waige waige yasoyi ,,inda zaiga ruwa amma babu

Gefensa ya kalla yaga wani shago da ake siyar da abinci da ruwa , da sauri mike yana duba aljihunsa ,, kudi ya fiddo , nan yazaro dubu daya ya nufi inda shagon yake har yana hadawa da gudu

Da sauri yashiga yana fadin hello madam give me water

Kallon shi matar tayi taga baya cikin hankalin sa tace what happened

Nuna mata ni yayi inda nake kwance kamar gawa

Da sauri ta dauko ruwan suka tafo tare Inda nake suna karasowa suka zubamin ruwan

Sai cen tukun na farfado ina kiran sunan shareef ruwa zansha shareef yunwa nakeji shareef nagaji da tafiyar nan ,

Da sauri shareef ya janyoni jikinsa yace Alhamdulillah maryam tashi nabaku ruwan ga abinci saina siya miki ,, kinga kudin da aka bani na albashi na ciro dubu hamsi ashe suna aljihuna ki tashi na soya miki duk abinda kikeso

Bude idona nayi ina kallon shi matar ta mikar dani daga jikinsa ,, tace muje nabaku abinci kuci nasan wannan ,,daga ganinku kuba yan garin nan bane

Shiga kafadana tayi muka tafi zuwa shagonta ,muna zuwa ta nufi inda abinci yake ta zubo mana ta kawo mana

Mika mana tayi tace maza kuci tana kallon mu cike da tausayi

Tin kafin ta kai ga ajiyewa akasa na amshe abinci na soma loma ba k'akkautawa shi kuwa shareef sani yayi agaba yana kallo na sosai nabashi tausayi ,, yana jin yunwar shima amma yakasa cin abincin saboda ni ban goshi ba ,

Matar nan ta kuya gun costumes dinta tana sallamar su

Saida na koshi nasha ruwa mai yawa kafin nayi hamdala ga Allah

Sai alokacin na kalli shareef daya tsuramin ido

A hankali nadawo kusanshi ina taba fuskar shi

Da sauri yajuyo ,murmishi yayimin na maida miki nima namishi murmishi ,,yace kin koshi

Eh nace ina gyara zamana

Daukar sauran yayi nan yasoma cin abinci saida yacinye duka tukun yasha ruwa ,nan muka zauna kafin kame mai tuni bacci yayi gaba dani

Matar nan tadawo inda muke tace ki bari ajima saina kaiku gidana zaku zauna a tare dani

Da sauri shareef yace eh ma zamu zauna dake mungode sosai Allah yasaka da alkhairi

Murmishi tayi tace ba damuwa , bari na hada kayan kai kuma kaji ana kiran salla idan kabi baya nan ga masallaci nan kaje kayi salla saikazo mutafi

Mikewa yayi yaje yayo alwala yatafi nima ,toilet tanuna min nashiga nayo alwala nayi salla

Bayan yadawo muka tafi gidan ma muna isa , muka shiga ciki,, gidan daki biyar ne da falo da toilet uku

Daki daya daga cikin dakunan ta nuna mana tace ,, mushiga ciki ,, har mu juya ko mai ta tuna , sai tace kutsaya yarana , nan muka dawo inda take

Kallon mu tayi tace am nace ba kudin ma'aurata ne ko yaya da kanwa ne

Shareef yace a a ansaka mana ranar biki dai bamuyi aure ba

Ma tace to ke zo muje dakina kai kuma jeka wacen dakin

Godiya sosai shareef yamata nan muka shiga dakin mai kyau da tsaruwa

Da dare tace muzo muci abinci bayan mungama muka koma falo ,, tace kusaki jikinku kunji ku dauki kamar nina haifeku , nasan soyayya ce ta kuka baro gida amma dai kufadimin,, menene yarabaky da iyayenku

Nice nace ma soyayya annabi Muhammad S.A.W da sarkin talikai itace ta rabamu da iyayen mu

Ma tace ban gane ba kuyimin yadda zangane

Nace mata saboda munshiga musulinci ,, iyayen suka koremu daga gida ,, nan nabata labarin komai game da barin mu gida

Sosai ta tausaya mana sosai tace mudauketa kamar ita ta haife mu zata zauna damu har abada

Munji dadi sosai har mukayi itama tace saboda tashiga musulinci iyayen ta suka koreta daga Enugu cen ne garinsu , tace ku inane garinku

Shareef yace mu a cikin daji muke sosai sunan garinmu mai daji saboda bamuda makotan gari shiyasa suna saka mishi suna mai daji ,

Ma tace to ku kwantar da hankalin ku nice maman ku kunji muje mu kwanta

Nan muka tashi kowa yanufo daki muka kwanta

Sosai mukejin dadin zama da ma dinmu dan da haka muke kiranta ma

Shareef yasamu ma yakai mata kudinsa yace yanason soma sana'a yagaji da zama haka gashi bashida takardun sa na school dasaiya nemi aiki ma to babu su

Ma tayi murna sosai daya zo mata da wannan shawarar shago tabude mishi ta kara mishi kari ya ringa siyar da kayan masarufi hakan ba karamin dadi mukajiba

Ni kuma kullin ina gida idan nagaji da zaman gidan naje wajan ma na tayata siyar da abinci , taso ta maidani makaranta amma na nace mata kawai zanke tayata siyar da abinci ,, haka ta hakura ta kyaleni , naci gaba da siyar mata da abinci dan yanzu komai ni nakeyi kuma muna kara samun sabbin costumes hakan ba karamin dadi yayiwa ma ba she saka mana albarka takeyi mu kuma muna jin dadin zama da ita

Wani lokacin nakanyi kukan rabuwata da ahalina ,, idan natunasu sainayi ta kuka ina tunanin ashe iyaye zasu iya rabuwa da diyansu akan wani ra'ayin banza da wofi ,, shesu zabi gunki akan mu yaransu ,, ganin ina neman sakawa kaina damuwa yasa nayi watsi da tunanin su papa nace , insha Allah bazan sake tunani akan su papa ba ,, tinda ba kaunar mu sukeyi ba harda zasu zabi wani abu akanmu

Haka mukaci gaba da rayuwa a wajan ma sosai shareef yake samun kudi , hakan yasa yabude account bank na soma tara kudi

Ma tace ya tara kudi yasiyo min kayan lefe sai yakawo sadaki a daura mana aure

Shareef yaji dadi sosai nan yakara kaiminsa yana tara kudi

Ranar da muka cika shekara a wajan ma shareef yahadamin lefe yakawo kudin sadakina dubu talatin , sosai ma tayi farin ciki nan ,,ya kaiwa wani malamin anguwar mu sadakin aka daura mana aure nida shareef

Ranar munyi farin ciki sosai marar musaltuwa ma ta gaiyato kawayenta da abokan kasuwancin ta tace ,, tana yiwa yaranta biki

Sosai mutane ke mamaki to ina tasamu yara bayan sun jima da sanin batada kowa ita kadai take

Wata kawar ta ta tambayeta mu suwaye ,, sai ma tace ai mu yaranta ne da haka sukabar maganar

Bayan ansha biki , ma da kanta takaine dakin shareef ,ta hadamu tamana nasiha mai ratsa zuciya tukun ta tafi

Tana fita shareef ya matso kusana yace maryam kinga ikon Allah ko ashe iyayenmu bazata ga aurenmu ba ,, Allah Allah yasaka wa ma da gidan aljanna

Na amsa da ameen nan mukayi sallar miga godiya ga Allah daya mallaka ,, mana juna tukun muka kwanta

Haka mukaci gaba da rayuwar mu mai cike da farin ciki da jin dadi ,

Wata rana wadda bazan taba manta wa ba a cikin tarishin rayuwar mu ,,,,wani mutum yazo wajan ma yaci abinci ,, amma yahana ta kudi

Aikuwa ma tace batasan ,zancen ba kullin saiyazo yaci abinci amma saiya gudu yau tace bai isaba saiya biyata kudinta

Ganin tana neman tara mishi jama'a ya kwance rigarsa ta tafi aguje

Ma tace kaci wuta bal bal nan tadawo kan abincin ta taci gaba da siyar wa

Bayan mundawo gida mun kwanta cen cikin dare aka diro mana ta katanga ,, bamu ankara ba mukaji muryan ma tana basu hakuri

Da gudu tayo dakinmu tana huce ta dauko card din bankinta ,, ta jefowa shareef tace maza kubi wannan kofar tabaya ku tsere banason su tabaku ,, ninasan kwanana yakare tana kuka

Da sauri muka rungume ta muna kuka nace ma ina zamuje kece uwarmu kece ubanmu yanzu idan muka barki ina zamuje ,, kawai muma su kashemu

Da sauri ta dagomu ta kalle mu tace wannan card dinane na banki idan kun tashi kuje kucire kudin duka dama bamai yawa bane na dauko jiya , tana fadin haka ta turamu ta wani kofa mai lungu ta kullemu

Haka munaji muna gani suka kashe ma dan kurma ihu shareef yarufemun baki yana matseni ajikinsa ,, saida suka tafi tukun muka fito daga inda ma ta tura mu

Ina ganinta cikin jini na fadi sumanmiya sosai hankalin shareef yatashi ganin wannan mugun aiki

Baiyi wata wataba ya kira nember police ya fada musu yan fashi sunzo gidanmu sun kashe mana mahaifiya

Yana kashewa ya dauko ruwa yazuba min ,, bayan na farfado , naringa kuka sainaje zan taba ma ,,sai shareef yace karna taba ta , idan akaga shatin hannu na zaace nina kasheta ,, inajin hakan na hakura

Police suka kira shareef wacce anguwa suke nan yatura musu address din gidan ,,babu mata lokaci suka karaso

Inda ma take suka nufa nan aka soma bincike munsha tambaya dan wani ma cewa yayi mune muka akshe ta
Chapter 59 · 0% Book details