← Book details Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 65

Sashe 5

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ameera tace to nan dai ta soma kalle kalle tace tab wllh wannan bayin na aljanune ko kuwa a aljanna ake ganin irin wannan bayin ahaka dai ta fidda kayan jikin ta wanka ta soma duk abinda ake anfani dashi fuziya ta nuna mata

Kuma tagane haka take dan akwai ta da saurin fashimta saida ta gama wankan tazo wanja alwala aikuwa taganta ta zama biyu idan ta taba fuskar ta sai taga wadda take gabanta ma ta taba idan ta zare ido itama saita zare ido tsoro ya kamata tana ja da baya itama ta jikin bangon tana ja da baya

Aikuwa ta saki uban ihu a guje fauziya da fatima da ameer wanda zamansa kenan yaji karan ameera aikuwa da sauri fauziya da bude toilet din taga ameera sai kerma take bakin ta na rawa

Fauziya tace lafiya dai kike wannan uhi !haka

Ameera tace wllh anty fauziya aljana ce nagani mai kama dani tana kallo na duk abinda nayi itama sai tayi

fauziya tace ina take aljanar

Ameera tace gata cen jikin bango tana nuna mata da hannu

Kallon inda ameera ta nuna fauziya tayi mirror din jikin bangon ta kalla anan ne taganta ajiki

Fatima ta kwashe da dariya tace amma anty ameera kedai kauyencin ki ya miki yawa madubi ne fa

Ameera ta turo baki gaba tace to ai mu a garinmu ba'a saka madubi a bayi

Fauziya tace to mu muna sakawa

Ameer ne ya karaso toilet din yaga ameera bako pant a jikinta yayi murmushi yace rigimanma yanzu saboda wannan ne kika saka mu gudu

fuskar tausayi ameera tayi tace to ai dai tsoro naji

nan suka fito daga toilet din fatima namata dariya

itama fitowa tayi bayan ta shirya suka fita falo suka tarar daddy da mommy a zaune suna jiran su

Daddy yace yar gidan inna ihun mai kike yi

Tace daddy wai madubi ne suka saka a bayi ni kuma da farko ban ganshi ba saida nagama na nazama biyu shine naji tsoro ko aljanu gareku agidan

Dariya daddy yayi yace to kidena jin tsoro

tace to nan suka fara cin abinci bayan sun gama

daddy yafita shida ameer ana neman sa a kasuwa

Ameer yanzu yagama karatun sa yana koyar wa a wata makaranta kuma nan yake so yakai ameera saboda ya kula da ita sosai dan ta nutsu tayi karatu

Da dare bayan an gaba cin abincin ne aka soma hira inda ameera keta basu labari irin barnar da sukayi a kauye ita da khadija kawar ta

Sai dariya suke ba kamar Fatima ma harda rike ciki takeyi

Ameera ta juya wajan mommy tace mommy kinsan harna tuna lokacin da muka yima malamin mu na school wankan kaikayi

Mommy tace kaikayi kuma ameera

,Dariya tayi tace sosai makuwa lokacin muna cikin aji sai malamin namu ya riga mu shiga shine fa da mukazo sai yace mu tsuguna a gabansa yayi ta zanemu da bulala ranar har ruwan zafi inna tayimin kuma tace sai taga waye ubansa da har zai ke zaneni haka nida khadija mukace zamu rama inna tace tana bayanmu mu rama tinda bamu yafe masa ba

Washe gari , muka je gonar mlm bukar muka cire mana mango sai gashi ya biyo mu zai zane mu muka boye a wani bayan bishiya yana isowa muka zuba masa kaikayi acikin rigar sa khadija ce ta hau sama ta zubo masa aikuwa ya soma zazzaga rigarsa baiga komai ba kuma jikin sa yana mishi kaikayi kafin wani lokacin tuni yacire rigar sa da wandon sa saina

Mukayi ta masa dariya ganin abin na karuwa ya yabar gonar yana zaginmu

Bayan yatafi muka fito nida khadija ta sauko daga sama nina fito daga inda nabuya , sai muka rankaya school din mu

Muna zuwa mukaga mlm kamar da gaske gaisheshi mukaje sallama muka mishi ya amsa gaishe shi mukayi nanma ya amsa da fara'arsa

Yace mana su khadijatullah ne da ameeratullah kijifa mommy dan shegen iyayi hadda mana karin suna

Khadija tazo tabayanshi ta zuba mishi kaikayin mukabar wajan

Ko minti goma ba'ayi ba akaji tana ihu asosa mishi

Shima yayi irin na mlm bukar yacire kayanshi ganin zai haukace aka kaishi gidanshi mu kuwa muna mishi dariya

Mommy na dariya tace kai ameera bakida da dama

Fatima tace ashedai kedin indon kauye ce

Ameera tace ba ruwanki yarinya

Hira akaci gaba dayi

10:00 PM ameera tasoma bacci mommy tace kowa yaje ya kwanta nan suka nufi daki akayi saida safe

𝙗𝙖𝙮𝙖𝙣 𝙨𝙖𝙩𝙞 𝙙𝙖𝙮𝙖

Aka nemawa ameera school a inda ameer yake koyawa aka kaita

Yaune zata fara zuwa sai murna takeyi saboda farin ciki ko baccin kirki batayi ba

Shiryawa tayi cikin uniform dinta blue and rid tayi kyau sosai tana fitowa falo ta zauna jira ameer bata jima da zama ba yafito cikin shirinsa

Murmishi tamishi tace good morning yaya

Shima murmishin yamata yace morning my wife kintashi lfy

Ameera tace Alhamdulillah , yace to muje mikewa tayi suka wuce

Suna zuwa school din yakaita ajin da za'a koya mata karatun tana shiga bata kula kowaba kowa yayi shuru jin malamin nasu tana tafowa
[24/10, 00:08] MRS. MU'UTASIM: https://chat.whatsapp.com/Gu2Mxr0SRlx8Da4tv0J2AR

🌟𝐀𝐌𝐄𝐄𝐑 𝐃𝐀 𝐀𝐌𝐄𝐄𝐑𝐀 🌟

𝙨𝙩𝙤𝙧𝙮 𝙖𝙣𝙙 𝙬𝙧𝙞𝙩𝙞𝙣𝙜 𝙗𝙮

𝐌𝐀𝐌𝐀𝐍 𝐍𝐔𝐒𝐀𝐈𝐁𝐀 𝐂𝐄✍🏻

5—6

Suna a haka Malamin "nasu ya shigo nan aka yasoma yimusu lecture,

Bayan antashi ameera ta fita domin zuwa wajan yayan nata tana karasawa wajan motar shima ya iso, tace yaya yunwa nakeji

Ameer yace to raguwa ai yanzu zamu tafi gida

ta turo baki gaba tace" nidai muyi sauri

yace to shikenan, nan suka fice gida

Suka zuwa gida ko dai-daita motar baiyi ba ta bude ta fita a mota

Ameer yace a wai Ameera duk yunwar ce ?

tace eh itace

yabi bayan ta suka shiga ciki

mommy suka tarar a falo fatima da fauziya ma sun dawo

Fatima tace sannunku yaya,

Yace yauwa

Mommy tace har kundawo ?

Sukace eh

mom tace to "idan kunyi wanka kuzo ga abinci angama suka amsa da to

Bayan sun gama ne kowa yafito sukaci abinci 'bayan sun gama cin abincin suka koma falo

Fatima tace anty Ameera wai da ni shekarar ki nawane?

Ameera ta mata kallon tara saura kwata tace ki tafi kauyen mu ki tambayi mana inna ko umma

Fauziya tayi dariya,tace kai kudai baku rabuwa da shirme

Ameera tace to ba ita bace ke nenani

mom kuwa na kallon su sai murmushi take dan ita yaran nata burgeta sukey

"Ameera tace to shekara ta 13 years na kusa cike 14 years tana kallon ta,

Fatima tace kai nifa nadauka kinkai kamar 15 years din nan,

Ameera tace to kuma sai kiyi ai

Ameer ne yasauko tin daga sama yake jin surutun su yana saukowa yace kai wannan yara Allah yashirya ku, ku kennan sai shegen surutun tsiya. Yakare magana yana zama

......Fatima tace nifa yaya tambayar ta nayi nawane shekarun ta wai duk ma a 13years take ,tana kallon sa

Ameer yace to da jikike shekarun ta nawa ?

tace kamar 15years haka

murmushi yayi yace to haka ma ai tafiki da shekara uku

turo baki gaba tayi tace, tab injiwa wannan har zata fini

ganin fuskar Ameer a hade yasa tayi shuru bata idar ba ya tashi zai fita

Ameera tace yaya zanje tare dakai

Ameer yace a a wajan abokina zanje

Ameera tace haka nan ma zanje

mom tace kutafi mana tare

Ameer yace to shikenan sako shijab dinkin mutafi,

Tayi daki da gudu dan karma yamata wayo ya gudu a mota ta tarar dashi nan suka fita a gidan

Suna tafiya suna hira har suka isa wani gida mai gadi yabude musu suka shiga,

Ameera tafito shima fitowa yayi sukayi kofar gidan suka shiga "da sallama suka saka kai cikin falon

wata dattijuwar mace magani zaune a falon tana ganin ameer tace a awanake gani kamar ameer koda idona ne keyimin gizo

Murmushi Ameer yayi yana rike da hannun Ameera suka karaso har kasa suka durkusa suna gaisheta tace, lfy lau alhamdulillah ya maman ka yace lfy suna gaisheki tace "ina amsawa tace wannan mai kama da kai din fa ko ita ce wadda aka daura muku auren,

Cikin jin kunya yace eh mama itace ina abokina yake

tace yana dakinsa nan suka nufi dakin,

Ameer ne agaba Ameera nabiye dashi har suka shiga da sallama

abokin nasa ya rungume sa yana kai wai yau wata rana ce!!!

Harara yabanka miki ta wasa yace oho dai koma meye,

Juyowa yayi nan yaga ameera yace madam shigo mana

Kara rungume ameer tayi ta bayan shi

Dariya sukayi tare, ameer yace kaga Anass kaifa dan iska ne yanzu saika taromin ruwa kasaka min mata tsoro

Zaro ido Anass yayi yace to ikon Allah dama wannan itace amarya tamu!!

Ameer yace eh itace yabashi amsa yana hura hanci saboda kar arena mishi mata,

Dariya Anass yayi yace madam bako gaisuwa ma

Ameera da take a bakale a bayan" Ameer tace nidai yaya kace mishi karya kara cemin madam kamar wata babba

Dariya sukayi Ameer
yace to kaji dai kadena

Anass yace to shikenan tinda baki so yakai karshen maganar tasa yace to fito mana mugaisa"

Kanta ta leko taga Anass da askin nan irin wanda gayu keyi ita kuma bata taba gani a zahiri ba sai yanzu,,dafe kirji tayi tace kai kai kai yaya ?

Ameer ya kalle ta yace "manene

Tace dama shi abokin naka dan iska ne ,,

kallon anass ameer yayi don yaga menene na yan iska ajikinsa nan yaga sabon askin daya yi,,

Kawai saiya kwashe da dariya yace abokina kasan meye yasa my ameera tacema dan iska

.....Shikuwa harya hade fuska yace a a saika fada tinda kun maidani mahaukaci,

"Ameer yace wannan askin naka ne da kayi shine yasa take ganin kamar kaidin dan iska ne,,

Dariya anass yayi yace kai amma yarinyar nan kincika abin dariya"

Tsuke baki tayi dan ita "idan kanason ganin bacin ranta kace mata yarinya ita dai tana son girma..tace yaya mutafi gida

Anass yace to daga zuwa

ta murguda baki tace, to kai ina ruwanka

Anass yace ba ruwana kuwa

Ameer yadan hade rai yace Ameera wannan abokina ne ba dan iska bane karna kuma ji kince mishi "dan iska
Chapter 5 · 0% Book details