← Book details Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 65

Sashe 60

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sosai naji tsoro saida akaga babu shatin hannun mu ajikinta tukun suka yadda bamu bane ,muka kashe ma ,, ga kukan da mukeyi nan akayi station damu

Gari na wayewa aka kai ma gidanta na gaskiya nayi kuka tamkar ruwan idona zai kare kullin ina dakinta ina kuka ,

Anyi ta bincike amma ankasa gano wannan yan fashin hakan yasa shareef yace kawai abar maganar Allah zai isar mana

Kullin ina cikin damuwa da kuka duk na rame nafita hayyacina ,,haka yasa shima yashiga damuwar halin danake ciki

Ganin yashiga damuwa saina rage tawa ina danne ta haka mukaci gaba da rayuwa agidan ma har Allah ya azirtamu da samun ciki sosai mukayi murna ,

Shareef ko kullin hirarshi babyn dake cikina hakan ba karamin dadi yaminba muma zamu karu nace idan na haifi mace zan saka mata sunan ma , Shareef yace to nan mukaci gaba da renon cikin

Cikina yanada wata biyar cikin dare wannan yan fashin suka sake dawowa gidanmu

Inda ma ta boyemu nan muka shiga muka kulle daga ciki kamar ba kowa

Shigowa dakinmu sukayi sunata dibe dibe

Daya daga cikinsu yace oga nan gidan fa ba mutane nafada maka

Ogan yace injiwa akwai yaran ta shiyasa taki bamu kudin ta duka kila sun tafi wani wajan mukoma falo mujira zuwansu ,,nan suka koma falo suka zauna kamar sun samu gidansu

Shareef yafito yadauko wayarshi yakoma inda nake ina kyerma rikeni yayi ya kiran police ,, yace inda suka kashe ma sunzo zasu kashemu nan sukace gasunan zuwa

Babu jimawa saiga kiransu yashigo wayar shareef , sukace kada mufito zasu shigo ahankali shesu kamasu ,, mukace to nan ya kashe wayar

Muna nan cen sai muji ana harbe harben bindigu sosai na tsorata , bayan wani lokaci muka ji shuru bude kofar dakinmu dan sandan yayi ya kira wayar shareef ,, nan muka fito yana rike dani

Barayin ankamasu nan nayi arba da wannan wanda sukayi fada da ma da sauri nace shine azzalimi ya kashemin mahaifiya ta dama kullin saiyazo yaci abinci yahanata kudi nan nabasu labarin fadansu ,, aka tasa keyarsu zuwa mota ,,ni kuma aka kaini asibiti saboda tsoron dana ji

Wasa wasa saida nayi sati a asibiti , ina jinya nice harda karin jini

Bayan an sallamemu ne ,, mukaje zaman kotu saida akayi sati ana shari'a tukun aka gama yanke musu hukuncin kisa ta hanyar harbi

Sosai mukaji dadin wannan hukuncin ,, bayan mun fito mukaje mukawa loyanmu godiya shareef yabiyashi kudinsa amma yaki karba ,, yace ma tana da kima a wajan sa dan haka bazai amshi kudinmu ba nan muka mishi godiya zamu tafi

Yace am shareef dazakuji shawara ta dakun siyar da gidan nan kubarma garin gaba daya saboda ,,wannan mutanen suna da diya zasu iya koma muku

Godiya muka sake mishi nan muka dawo gida

Bayan kwana biyu muka samu malamin anguwar mu muka cemishi zamu siyar da gidan , shima yace zai tashine yakoma kauyensu nan mukace zamu bishi cen kauyensu

Sosai yaji dadi yace muje inda ake siyar da gidaje , nan suka tafi da shareef ni kuma nakoma gida

Bayan kwana uku aka siyar da gidan million daya saboda wulakanci a haka ma wai mai siyan yace sai an rage mishi ,, mlm yace sam kawai yasiya ahaka , tukun yabda milion daya

Haka muka tattara kayanmu na siyarwa muka siyar wanda zamu iya dauka muka dauko nan muka hau mutar katsina

Musha tafiya sosai nagaji kafin azo katsina tinda sassafe muke tafiya har dare tukun mukazo katsina

Shareef yakama bama dakin biyu a hotel din garin muka kwana

Da safe yabiya kudin mukaci abinci tukun muka kama hayar k'ankara babu dadewa mukaje garin mai kyau da tsari

Gidan malam Ahmed muka je matarshi ta tarbemu da murna ,,sosai ta nuna mana karamci ,hakan yamana dadi harda malam kanshi

Ana mukaci gaba da renon cikin jikina har na haifi namiji sosai shareef yayi farin ciki da matar mlm ranar suna aka sakawa yaron ,Ahmad sunan mlm ne

Malam yayi farin ciki da takwaran da aka mishi dan haka koda yaushe yana wajanshi bacci kawai ke rabasu

Bayan shekara uku nasake haihuwa wani namiji yaci sunan muhammed , shima ansha biki sosai bayan wata shekara hudu nasake haifo namiji yaci sunan Abubakar sadeeq ,, amma ake kiransa da , Abubakar ko ace sadeeq amma Abubakar din yafi karfi

Bayan haihuwar abubakar da shekara biyu na haifi mace ,, nasha murna dan sai wannan lokacin na haifi mace , nan na saka mata sunan ma wato mufeeda , tin daga kanta haihuwa ta tsaya min

Haka muke rayuwar mu amma fadana yana nan yanzu nazama yar gari duk wanda ya tabamin mufeeda sai anyi fada dani sosai kowa na garin yagane halina

Ahmed yana da shekara goma mlm ya rasu shida matar dalilin wata tafiya sukabar yaransu mata biyu sadiya da nana

Mukaci gaba da zaman mu dukanku a wajena kuka taso

Haka muke rayuwar har kowa ya girma a cikin ku

Da kuka girma dagin matar mlm suka dauke su sadiya

Banso hakan ba amma ba yadda na iya suka tafi

Da suka girma bayan kun gama karatu aka aurawa Ahmed sadiya abubakar ya auri nana

Hakan yayimin dadi sosai Muhammad kuma ya auri fadila diyar abokin baffan ku

Wannan shine tarishinmu nida baffan ku

Inna ta kalli maman anty karima tace kanwata ,, bayan muntafi wani hali kuka shiga

Maman anty karima tace ,zan fada muku amma muje muyi salla mudawo aci abinci tukun

Nan kowa yatashi yatafi salla

Ameera ko bataso ta tashiba so take taji yadda kakan su daddy yayi lokacin daya kori su inna,,, amma akace sai anjima

*Nima nace bari naje na huta kafin sudawo*
[30/10, 19:24] MRS. MU'UTASIM: *🌟𝘼𝙈𝙀𝙀𝙍 𝘿𝘼 𝘼𝙈𝙀𝙀𝙍𝘼 🌟*

*𝙎𝙩𝙤𝙧𝙮 𝙖𝙣𝙙 𝙬𝙧𝙞𝙩𝙞𝙣𝙜 𝙗𝙮*

*𝙈𝙖𝙢𝙖𝙣 𝙣𝙪𝙨𝙖𝙞𝙗𝙖*

💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*

https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_

*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*

𝐰𝐚𝐧𝐧𝐚𝐧 𝐬𝐡𝐚𝐟𝐢𝐧 𝐧𝐚 𝐬𝐚𝐝𝐚𝐮𝐤𝐚𝐫 𝐠𝐚𝐫𝐞𝐤𝐢 𝐚𝐝𝐝𝐚𝐧𝐚 🥰🥰💃🏼💃🏼𝐧𝐢𝐤𝐚𝐝𝐚𝐢 𝐛𝐚𝐝𝐚 𝐤𝐨𝐰𝐚 𝐛𝐚:::ummu amsad 𝐤𝐢𝐣𝐢 𝐝𝐚𝐝𝐢𝐧𝐤𝐢 𝐝𝐚 𝐰𝐚𝐧𝐧𝐚𝐧 𝐟𝐚𝐠𝐞 🌺🌺🌺🌺🌺🌺

*87—88*

Suna tashi daga falon kowa ya nufi inda masaukinsa yake ameera ta nufi dakin su ita da ameer ta kyer take tafiya saboda ciwon da jikinta har wani jiri takeji saboda yayan nata jiya bai bari tayi bacci ba shiyasa yake take dafe kai

Suna shiga ameer ya rikota yana shinhina wuyar ta da gashinta wanda yasha gyara sosai
Ganin yana neman zufe mata jib din rigarta tayi sauri rike hannun shi tace , yaya cikani salla fa

Idonshi a rufe yace wifey yunwa nakeji fa jiyama ban goshiba

Kura mishi ido tayi wani tausayin shine yakama ta amma ta danne dan itadai ko ba zata koma wajan jin karashen labarin su inna ba tofa bazai yiyuba ta kuma hayeta saboda ko ina na jikinta ciwo yake mata

Tace yaya please kayi hakuri wllh duk jikina ciwo yakeyi kasan bayana kamar zai fita bazan iya daukar nauyinka koda na yadda bazaka samu abinda kakeso ba kayi hakuri kuma kaga zamu ida jin labarin su mama dan haka kabari sai dare kafin lokacin nayi bacci na ware

Rungume ta yayi yace shikenan na hakura muje muyi salla idan angama jin labarin saikiyi bacci

Tashi sukayi toilet suka nufa da yin alwala bayan sun gama salla suka sauko

Kowa yadawo nan baba laraba ta gabatar musu da abinci mazan suka tafi dakin baki matan ko suka zauna a falo nan aka soma cin abinci

Ikram karama ce ta tashi daga bacci , waigawa tayi ko ina taga ba muhammed aikuwa ta soma kuka iya karfinta

Da sauri suka juya ameera tace kai wllh yarinyar anyi ja'ira wllh fice kibamu waje duk kin damemu da ihun kuka tafiyar wajan uban naki

Fatima tace to ke ina ruwanki ,, yar iya bata tafiya nandin gidankine , bare amata gori kema tafi gidanki

Hajara tace kedai bari wai hadda ta tafi to bata zuwa zonan ikram

Ikram ko nufar hajara tayi tana fadin daddy mommy daddy

Dariya sukayi mommy tace wannan yarinyar tayo gadon uwarta wllh

Mama tace da alama kuwa

Umma tace tashi hajara ki kaita wajanshi wannan ba shuru zatayi ba inbata Ganshi ba

Mikewa hajara tayi tana fadin to umma nan ta dauketa suka nufi dakin baki

Takusa isa shima muhammed ya fito dan yana tunanin kar ikram ta tashi take nemanshi yasan halin rigimar ta

Karo suka kusanyi da hajara ta tsaya tace a tureni zakayi

Zaro ido yayi sai kuma yayi murmishi yace banganki bane yar kanwata

Ikram na ganinshi ta soma dariya tana daddy daddy

Hannu yamika mata yace yar kanwata dama yanzu nake tunanin kintashi ashe hakane

Mika mishi ita hajara tayi tace yanzufa da anty ameera ta zaneta kamar zata daketa

Da sauri yace tab yar mommy din ce zata daka lalle data ga police a gidanta dan bamai tabamin kanwa ta

Murmishi tamishi tace to shikenan nina tafi

Muhammed yace am sai kuma yayi shuru

Hajara tace magana kakeyi ne ,, da sauri yace a a ba komai nan tayi gaba abinta

Muhammed yace kash maiyasa ban fada mata ba ,amma ba komai wani lokacin zan fada

Ameer ne yafito yace to yar mommy harta tashi daga bacci ne
Muhammed yace eh yanzu hajara takawota wajena

Ameer yace lalle wannan anyo gadon su yar inna ,,,dariya sukayi tukun sauran suka fito nan aka nufi falo

Matan ma sungama cin abinci har an gyara wajan tsaf

Zama kowa yayi aka nutsu ana sauraron mama maryam

Mama ta gyara murya tace ,, lokacin da papa ya koreku munsha kuka sosai nida yan uwana sosai muka shiga damuwa maman mu tafi sati a hospital tana kwance ba lafiya

Maman yohun itama haka abin yadameta kowa na family mu yashiga damuwa harma su papa da daddy haka suka shiga damuwa

Sosai granny mu tayiwa papa fada tace akan me zai kore ku ba gyara a kori headmaster din ba yakoma garinsu amma yanzu anyi biyu babu ba ku din ba headmaster din duk kowa baya garin

Haka muka kasance muna jin kewarku maman mu ko abin ciwo yazame mata sosai ciwon zuciya yakama maman mu
Chapter 60 · 0% Book details