← Book details Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 65

Sashe 49

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Anass kuwa,, har yanzu mamaki ne akan ,, fuskar shi " yana tunanin anya fatima batada aljanu nan yafita yashiga motar suka tafi gidan mama

Su hajara na " isa gida inna suka samu a falo ita kadai, tayi ture kaga tsiya,, tana taunar " goron ta

Da sallama suka shiga amsa musu " Inna tayi dacewa Amin wa'alaikum salam badan halinku,, ba futsararru " kundawo, kenan

Dariya hajara tayi tana sakin hannun ameer " tace eh mundawo hajiya inna mai duniya

Harara ta,, aikawa hajara tace a kinga mararsa kunya kunzo yanzu zaki soma ko to wllh karrr nake ganinki " kamar,, takarda,, ja'ira ,, kawai

Murmishi sukayi kowa yabar mata falon ganin inna ta soma fada,, suka barta ' anan tana zaginsu

Ameer na shiga dakinsa ,, ya zauna " yana rike kanshi wanda take miki ciwo sosai ,, ruwa mai sanyi ya dauko daga yar kawamar,, frijj, dinsa ,, ya kafa abaki " saida ya shanye tass kafin ya ajiye gorar ruwan,,

Kwanciya yayi yana tunanin ameera yanzu ko wani hali take,, koya labarin cikin sa dake jikinta,, kota haifa , kome ta haifa mace ko namiji, , mirginawa " yayi yace Allah sarki wife na, na kina kusa dani bazan zama maraya ba marar gata,, nasan duk daren dadewa " insha Allah zaki dawo gareni ina jin hakan a jikina, , ganin bamai bashi amsa yasa ya hakura a haka bacci yayi gaba dashi

Su fatima,, na isa gidan mama,, ko baking bai,, gabayi ba tabude motar tafito,, tana hura hanci

Anass ko yana ga ikon Allah yaudai ga fatima sa yakasa gane kanta ,, shima ciki yanufa

Da sallama,, tashiga kafin mama ta amsa tarusa kuka, tana karasowa,, wajan mama

Mama tamike tana fadin lfy fatima kedawa , rungume ta mama tayi tana rarrashin ta,,saiga anass yashigo " duk fuskar tanuna damuwa

Zama yayi ya kallesu ,, yace mama barka da gida

Amsa mishi tayi tace mekamata,, tashigo tana kuka, son

Cike da damuwa yake kallon mama yace wllh babu " abin namata,, dawowa ta kenan daga aiki na ganta tana kuka sosai ,, shinefa na tambayeta lfy,, kawai ta rufeni da masifa, kamar zata sakeni,, hakan bai mata ba " tace saina kawo gidanki ko tazo da kafar ta ,,,bakiga ko uniform ban cireba,, tasakanii agaba saida mukazo

Ran fatima ne yakara baci,, ta dago tace to, ina ruwanka dani hadda tambaya ta,, ni dan wake nakeso mama zanci yunwa nakeji

Yar dariya mama tayi tace ,, yanzu kuwa zan miki,, yarinya maza kije dakin son ki kwanta " kinji

Mikewa tayi tabi ta kusan anass saida ta mika hannu ta mintsine shi a wuya har sau uku,,

Anass yana jin ta,, yayi shuru kuma , yaji zafi sosai a wuyansa

Mama na kallon sai dariya take kasa kasa ta danne dan kar su gani

Ficewa fatima tayi hallau saita waiwayo,, aikuwa akaci sa'a anass na, kallon ta, harara ta banka mishi , ta soma kuka tace waiyo Allah mama,, kin yana min gwalo ko " wllh anjima zan rama,,

Mama tace yi tafiyarki daughter kyaleshi ni zan rama miki,,, nan fatima ta tafi

Anass ko kallon mama, yakeyi sai dariya take mishi ,, mama tace amma mai gidan nawa sai,, saka min yarinya fada yakeyi,,

Anass yace mama kamar yaya,, nifa nakasa gane kan fatima kodai aljanu gareta,, ban saniba

Mama tace babu wani aljanu,, cikin jikin tane ke sakata,, yin wannan fadan

Da mamaki yake kallon mama yace,, to dama mama ciki nasaka wannan abun

Mama tace sosai makuwa,, ai halaye dayawa zakake gane awajan mace mai ciki "
Wata yasaka
Rashin magana

Wata fitana

Wata haka kawai sai kaga tana masifar fada

Wata kuma batason jin kamshin turaren mijinta

Wata kuma idan tasamu ciki sai yawan cin abinci kamar gara

Wata rashin cin abinci,

Wata bacci

Gasu nan dai dadai sauransu, ,, to ita fatima nata fada yasakata,, dan haka idan kaji tana wannan fada, bata hakuri ka rarrashe ta,, shikenan saiku daidaita

Ajiyar zuciya yasauke yace, tab lalle Allah yasaka muku iyaye da gidan aljana ,, tin daga ciki kukasha kahala,, damu har girmanmu,, har auren mu,

Ameen mama tace,, tana mikewa tace bari namata,, dan wanken inyaso " saiku tafi

Anass yace to nan yamike yanufi dakinshi,, yana zuwa yaganta tana bacci hankali kwance ,, murmishi yayi yace Allah yasaukeki lfy sweetheart dina,, nan shima ya hau gadon ya janyota jikinsa suka kwanta

Yau satin ameera biyu ,a asibiti sosai take samun kulawa " wajan doctor aisha ,, Alhamdulillah yanzu jiki yayi sauki dinkin da aka mata ya warke saidai rashin kwarin jiki " nan aka basu sallama,,

Mama ta kira " Umar yazo yakaisu gida an sallamesu

Da murna suka shigo asibitin

Su bubakar " suka tafi dakin da gudu, suna mommy mu ta warke, yeee zamu tafi gida yau

Murmishi ameera tayi ganin , sun shigo yaran su hudu,, kowa sai mommy yake cewa ,,,hannu tabude musu nan sukayo kanta,, suna rungume ta,,,,, beauty tace sannu mommy

Kallon ameera tayi shesuka bata tausayi yandda suka lafewa ajikin ta,, tace,, to kutashi muje gida kunji yaran albarka, ,, mikewa sukayi tasauko,, koya kama hannun ta, tana tsallen murna

Doctor aisha ce tashigo tace to ,she gidako " Allah yakiyaye gaba, ikram tasaki hannun ameera ta kama na doctor aisha,,

Murmishi tayi tace,, a a ikram ko mutafi gidana dake,, hannu ta daga, tana fadin umbo,, mommy, ,dariya tayi tace wai ameera wannan bagwariyar,, yar taki mai take cewa,

Kallon su ameera tayi, tace idan tace umbo,,, wato tana nufin ki dauketa, idan kuma tace aiya , to ku zauna take nufi,, idan tace, mamo kuma bacci take nufi kai wani yaren nata nima ,, kasa ganewa nakeyi idan tanayi ", saidai in tana nunamin da hannu zam gane abinci take nufi

Dariya sukayi su duka,, Umar yace ai akwai yaruka akan ikram wani abun intana jagalgwawa ,, sai ka kasa gane ina ta dosa ,

Doctor aisha tace,, gaskiya naga alama zo mutafi ,,gidana nan ta dauketa ", ita kuwa sai murna takeyi, antafi da ita,,,suma tafiya gida sukayi

Ikram ce zaune a falo,, yauma aikin tunanin ameera takeyi,, abu kamar wasa ameera har tayi shekara biyu da rabi ,, da bata yanzu a ina take

Su ameer da ameera ne suka shigo
Jikinta suka fada

firgigit tadawo daga,, tunanin tace harkun dawo,, ina daddyn ku yake

Ameer ne yace mom " daddy yace mushigo shiya koma ,wai meeting gareshi,

Tace to muje namuku wanka nan sukayi daki

Ameera ce,, kwance cikin dare sai juya kanta takeyi, tana yatsina fuska, kamar mai ciwon,, junnu a razane ta farka " har jike tayi sharkab,, kamar an zuba mata ruwa, , addu'a ta ringa yi,, , yashafa,, tanason komawa bacci amma ya gagareta " tana tunano abinda tagani a mafarkin ta.....

*ko meye ameera tagani a mafarki oho*

*thank you my fans ina godiya da addu'o'i ku agareni Allah yabar kauna*
[30/10, 17:51] MRS. MU'UTASIM: *🌟AMEER DA AMEERA🌟*

*STORY AND WRITER*
*BY*

*MAMAN NUSAIBA CE ✍️*

💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*

https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_

*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*

*73—74*

Tagumi ameera tayi tana tunano abinda tagani a mafarkin nata ,, anty karima ce tagani wasu mutane najanta ,, tana kiran sunan ameera kizo ki ceceni kada kibari sutafi dani " please ameera....ta fada da karfi

Da gudu ameera tabisu harta kama anty karima zasu gudu wani daga cikinsu ya bige ta akai nan tafadi,, ihu anty karima keyi saboda ganin abuge ameera tana jijjiga,, ta nan sukazo suka dauke anty karima " wani daki suka sakata,,, ajiyar zuciya tasauke bayan tadawo daga tunanin mafarkin data yi sosai jikinta yayi sanyi tashi tayi tashiga toilet , tayo alwala nan ta soma jero nafila

Umar ma , yadda ameera tayi mafarkin shima haka yayi,, da sauri yadiro daga kan gadon yana safa da marwa ,, shi yakasa gane wannan dakin acikin gidan bauta a wani waje yake babu inda bai sani ba gidan bauta amma wannan dakin baisan shiba kai dasake lokaci yayi da zai je gidan bauta yaduba lungu da sako saiya gano wannan dakin ,, yaga ko karima na ciki ganin hakan ba mafita bane yasa shi tashi yayo alwala yasoma nafila ,, yanakai kukansa wajan Allah daya bayyana mishi matar shi ya kareta aduk inda take

Su bilal abin nema yasamu sai nan nan ake da jamila ita har mamaki ma yake bata in yanayin wani abun, ,, da wuri yake dawowa daga wajan aiki yazo " yayi tawa cikin jamila magana wai yana magana da babyn shi

Dariya jamila keyi duk lokacin daya soma wannan abun

Yauma suna zaune ya kara kunnanshi ajikin cikin , dagowa yayi yace habibty wllh baby yana motsi ,, yasan babanshi na kusa dashi

Kallon shi tayi tana murmishi tace, eh nima naji yana motsi " kasan dani zaiyi kama bada kaiba

Harara ya aika mata yace, tab wllh baki isaba dani zaiyo kama yarinya ,, nasha wahalar samar dashi amma kice dake zaiyi kama, ninefa nafi yin aiki wajan samunsa

Dariya sosai jamila tayi tace habiby wannan maganar haka bakajin kunya,, to naji yayi kama dakai shikenan

Murmishi yayi yace ai dole ma kibar min maganar insha Allah dani zaiyi kama

Tace ameen

Shafa cikin yayi yace waida watan shi nawa cikin nan

Bakwai ta bashi amsa

Yace kai ashe nakusa zama daddy wllh Allah yamiki albarka habibty Allah yasaukeki lfy

Tace ameen habiby. ,,Fatima kuwa haihuwa ko yai ko gobe insha Allah

Bilal yace eh wllh bakiga yadda cikin ya keretaba idan kika ganta abin tausayi ,, kai Allah yasakawa iyayenmu da Alkhairi ,, Jamila tace ameen ya Allah ,nan sukaci gaba da hirarsu ta masoya

Fatima ce tafito , tana tafiya da kyer anass ne ya taimaka mata,, ta zauna ahankali

Kallon ta yake cike da tausayi yana matukar tausaya mata ,, yadda cikin ya hanata komai amma duk da haka,, bata hanashi hakkin sa " gaskiya yana jinjina wa fatima kukan tane yadawo dashi da sauri yarike ta yace yadai

Kwantar da kanta, tayi a kafadar shi tace sweetheart

Juyowa yayi yana kallon ta yace na'am meke miki ciwo ne
Chapter 49 · 0% Book details