← Book details Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 65

Sashe 48

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wajan ta yayi , yana fadin Alhamdulillah, ala kulli hal " Allah abin godiya nan yasoma , bata right kiss,, da kyer ts kwace tace kaje mana " ko sokake later ne

Kallon ta yakeyi cike da kauna da farin ciki aikuwa yasoma kiran ameera yafada miki, ameer kamar, yayi me dan murna " kafin yakira ammi,, ya fada mata nan tace maza komai yake yakawo jalima, gida , bdan yasoba haka suka tafi gidan ammi "

Ameer da hajara ne,, zasu tafi gida sun tashi a aiki

Wata nosee ce tazo a guje tana fadin ,, sir " please taimakon gaggawa gamai haihuwa ,, cen rai ahannun Allah bazata iya haihuwa da kanta ba sai an mata c s ,,please muje

Kallon shi hajara tayi tace kaje mana yaya,, nizan jiraka,, kugama ,, murmishi yayi ya dauko ,,, kayan aiki yacewa,, Nosee din, maza kikai kayan , aiki wanda zamuyi " aikin kice suzama redy,, banason jira ,, da sauri tace ok sir nan suka tafi

Ba"afi minti biyar , da tafiyar ameer ba wani saurayi yazo wajan hajara ji tayi ance

Assalam alaikum

Juyawa tayi domin taga waye nan ta amsa mishi

Yace yan mata sannu , dan Allah doctor ameer fa

Saida ta harareshi kafin tace maizai baka

Yace nazo gaishe shine

Hajara ta murguda mishi baki taje tayi,, banga banga a " bakin kofar,, shiga tace,, baka isaba ka shigar wa yayana office dinsa,

Kuri mata,, da ido yace Allah sarki wannan acting dinta kamar ameera,,tabbas wannan kanwar tace " murmishi yayi yace ,, ke nifa kanin yaya ameer ne fa,, idan bayanan,, saimin bayani ", ok

Hajara tace yana dakin tiyata,, bazai fito yanzu ba

Yace ni sunana , salim idan yafito kicemai salim yazo yatafi

Dan murmishi tayi tace to shikenan ,, zan fada masa,,

Nan yatafi yana murmishi dan ba karamin burgeshi hajara tayiba

Yau yan gidan, abin bauta su raju, suka shirya kashe ameera,, nan suka kira wani ", bawan su

Raju yanuna mishi photon ameera ,, da address din gidansu,, Raju yace tana fitowa, ka kasheta "

Saurayin ya amsa yayi gaisuwar,, ban girma ya fice zuwa gidan su ameera

Ameera tafito,,sanye da hijab " kasuwa zasuje dan bata taba zuwaba,, shiyasa yau mama da umar, dukkansu yan gidan. Zasu tafi

Ita ta fara fitowa, saboda murna

Tana Kallon fitowar,, ya lallaba " da sauri ,,

Tana gyara hijab dinta taji an soka mata wuka, a hakarkari,,

Wani gigitaccen kara tayi,, tana fadin innalillahi wa inna ilaihin raju'un,, ta juya taga wanda yasoke ya kafin tasoma yin kasa

Abubakar ne yafito shida beauty suna dariya turuss suka tsaya ganin ameera acikin jini

Da karfi beauty tace ,mommy ,, mommy na,, daddy wani yakashe min mommy na please kazo

Aguje Dukkansu " suka fito daga gidan,,

Suna isa gareta mama ta fasa kuka,, tace innalillahi wa inna ilaihin raju'un nashiga ,, uku ameera wani azzalumi " ne yamiki wannan zalincin ,, shikenan sunkashe ta, umar kalli idonta sai fari bata numfashi , waiyo Allah ni zainab naga takaina

*nima nace bari na gudu kar amin irin na ameera*

*Maman nusaiba ce ✍️*
[28/10, 14:31] MRS. MU'UTASIM: *🌟AMEER DA AMEERA 🌟*

*STORY AND WRITER BY:*

*MAMAN NUSAIBA CE ✍️*

💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*

https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_

*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*

*71—72*

Karasawa,, sukayi wajan ameera ,, da take kwance kamar gawa,, jini na malala ta gefen,, cikinta,, da sauri, umar ya dauketa yasaka ta a mota ,, suka shiga sai hospital ,, tin kafin su isa,, Umar yakira , Muhammed yana fadamishi " gasunan zasuje asibitin su,, Ameera ba lfy wani ya tsoka mata wuka

A rikice , Muhammed yasoma fadin innalillahi wa inna ilaihin raju'un,, garin yaya hakan tafaru, to shikenan ganinan zuwa ,

Yana kashe wayar yakira,, mommy sa ringing uku ta dauka

Tace hello son yadai

Da sauri yake magana har bakinsa rawa yakeyi,, yace mommy ,, makiya sunyo kan ameera,, yanzu umar yacemin an soke ameera da wuka,, gasunan zuwa asibitin,

A razane ta mike tana fadin me...me....mekace son ameera ce,,aka soka da wuka to saikazo dan tarosu,, bakin kofa nan ta kashe wayar

Da sauri yayi backing, ya sauka,, bude gidan baya yayi ya dauko ameera ,, tana fadin doctor please come in ,

Da gudu suka kawo gadon ya daura ta,, nan aka tafi da ameera emergency room,

Zaunar da yaran sukayi abubakar da beauty,, sai kuka sukeyi,, ganin maman nasu " a wannan halin su ikram kuwa,,, wasansu suka kamayi,, ita da muhammed suna zagaye su umar shida mama

Kallon mama tayi tace Allah sarki ,, yarinya kenan ba ruwansu wasan su sukeyi, umar yace eh basuda damuwa

Ameer na cikin yin aikinsa,, yaji gabansa yayi mummunan faduwa,, dafe saitin " zuciyar shi yayi yace my wife Allah yakareki " aduk inda kike nasan yanzu akwai abinda yasameki,,

Nosee din kusanshi ce tace ranka ya Dade,, yika dinke wanjan kar iska tashiga ,

Da sauri yadawo daga duniyar tunanin dayakeyi,,, nan yayi sauri ya gaba yafito

Hajara kuwa na bakin kofar office ,,din ameer itama taji gabanta ya fadi,, runtse ido tayi tana karanto addu'o'i sosai ,, saida taji sauki kafin ta bude idon,, amma taji duk jikinta ba dadi , tana wannan halin ta hango ameer na tafowa jiki,, a sayaye " yake tafiya da sauri ta dauki,, jakar tashi da ta ,ta nan tanufosa,,

Wanda suka kawo mai haihuwar,,ne suka mike suna fadin lokita,, yamai jikin saboda sun ganshi,, jiki a sanyaye

Kallon su yayi yace Alhamdulillah anyi nasara, anjima zaku ganta ma,,,

Godiya suka soma mishi ,, da dan gudu hajara tazo ta, fada jikinsa tana,, kuka sosai

Baki suka saki suna kallon hajara, ,, wata takasa daurewa tace doctor amma wannan kanwarka,, ce naga kuna kama sosai

Murmishi yayi yace eh kanwata ce hajiya

Wasu yan mata,, dake gefe kallon su ameer sukeyi " kamar sun samu tv

Gefen yan mata yasamu wasu,, kujeru ya zauna hajara na tsaye,, tana kuka tana banka wa ameer harara,, saboda ya rabata da jikinsa

Yar dariya yayi " ya bude mata hannu,, da sauri tashige jikinsa,, bubbuga bayanta yake, saida tayi shuru,,tukun yadagota " yace, maiyafaru ne kike kuka keda nabarki lfy nashiga emergency

Turo baki gaba tayi tace,, yaya ina zaune naji faduwar gaba " shine nayita addu'a shine naji,, banajin dadi

Murmishi yayi yace,, nima naji hakan amma nayi addu'a kitashi mutafi,, gida yunwa nakeji,,

Tashi tayi akanshi,,tace to mutafi ,,yaya so nake muje naga inna " dariya yayi yace to nidai ba ruwana bacci zanyi idan naje, , hajara tace to shikenan

Harsun,, dan wuce wajan yan matan,, nan wata tace
Hello ameera

Cak suka tsaya " Hajara tajuyo tana kallon ta,,

Mikewa budurwar tayi,, tace kai ameera wannan kallon fa kamar baki taba ganina ba,, nice yar ajinku "dana taba cewa inason ameer ,, kika cemin mijinki ne,, nabaki hakuri,, kin tunani ko,, tana kama hannun hajara

Hawaye ,, hajara ta share tace,, niba ameera bace

Da sauri ta kalle ta tace haba ameera,, dan kinga nazo gaban ameer dinki " shine kike cewa bake bace,

Hajara tace, da gaske nake bani bace,, Ameera nan tabata " labari batan ameera yanzu shekara biyu da rabi kenan,, da batan ameera

Kuka take sosai,, tana fadin innalillahi wa inna ilaihin raju'un waiyo Allah ameera,, gaskiya natayaka jimami " yaya ameer ,, Allah yabayyana ,, mana ita

A tare sukace,, ameen

Tace ni sunana ,Rabi'atu ni friend din ameera ce,, Allah yabayyana ta " ban taba jin labarin batan ameera ba sai,, yanzu

Nan suka yi sallama ,

Kawar ,, Rabi'atu tace, wai dama kinsan sune

Rabi'atu tace nasan yayan ta ashe wai ta jima da bata matar wannan doctor dince ,, kuma wllh inkika ganta kamar an tsaga kara da ameera da ameer da wannan kanwar tasu,, Allah ya bayyana tadai ,, tace ameen nan suka tafi ,,

Su mama sunkasa tsaye sunkasa, zaune, ' har sukafi awa biyu ,, awajan baa bude,, kofar dakin da aka saka ameera,, har muhammed yazo shima duk a kidime yake

Bawan minti kamar arba'in aka bude kofar, doctor aisha ce tafito,, tana share gumin dake goshinta,,

Da sauri suka yo wajan ta muhammed yace mommy,, ya jikin ameera ",
Kallon shi tayi tace Alhamdulillah mun tsaida jinin,, insha Allah zata samu lfy ,,a tare suka " sauke ajiyar zuciya nan suka zauna

Doctor aisha ta matso kusan su ikram,, tace baby da murna ikram tayo wajan doctor aisha daukar ta tayi tana mata wasa,, shikuwa muhammed yana bakale jikin abubakar,, ,, ko kallon inda su ikram suke bayiba yayi kwanciyar shi

Umar yace zai koma gida ya dauko , kayan abinci da,, dana sawar ameera nan ya tafi

Fatima ce zaune ,, tana rusar kuka " hadda jan majina takeyi da sauri anass nazo,, yana fadin lfy sweetheart

Kallon shi tayi kawai sai taji,, wata masifar fada nacinta "

A masifamce,, ta mike tana banka mishi harara,, kamar idonta zai fadi kasa tace,, to ruwanka dani dama kake tambaya " ta konace kazo inda nake mutum sai naci ,, wllh kafita idona,, kona shuka maka rashin mutumci,,, a gidan nan har zakake kallona kace min wai lfy to meye naka aciki " iyee nace meye naka " da kake tambaya ta,, kamar wani ,, minkarin da walakiri " ko a kabari nake da zakake tambaya ta " nifa banason damuwa kafita idona na rufe wllh kuma kazo ka kaini gidan mama kona tafi da kafata,, eehee

Baki da ido,, yabude yana kallon fatima namishi masifa " da kashe shi da mamaki ,, wai shi takewa fada to danya,, tambayi dalilin kukan nata, shine " take wannan fadan " kodai akwai wanda yataba ne kafin yazo

Ita kuwa, Fatima ganin yana kallon ta kamar yasamu tv yasa ta karasa,, inda yake tana dafe cikinta daya mata kyau sosai , tace magana fa nake kawani,, saki baki kana kallo na kamar wata tv

Dawowa,, yayi daga tunanin sa, yace muje

Nan tasaka,, hijab din ta tayi gaba abinta ko kallon shi batayi ba
Chapter 48 · 0% Book details